Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    • Shafin Farko
    • Labarai

      Gwamnatin Kano Ta Shiryawa Ƴan Jaridar Yanar Gizo Horo Na Yini Biyu a Jigawa

      January 15, 2026

      Tanka Ta Murƙushe Mutane 5 a Gombe

      January 12, 2026

      Babu Siyasa a Binciken Da Ake Yi Wa Malami – EFCC

      January 12, 2026

      Ƴan Bindiga Sun Kashe Soja Da Jam’in NSCDC a Benue

      January 12, 2026

      Manyan Jiga-jigan APC 3 a Kogi Sun Mutu

      January 12, 2026
    • Siyasa

      Manyan Jiga-jigan APC 3 a Kogi Sun Mutu

      January 12, 2026

      Ganduje Zai Gana Da Masu Ruwa-da-tsaki Na APC

      January 11, 2026

      Datti Baba-Ahmed Ya Musanta Batun Tsayawa Takarar Shugaban Ƙasa

      January 9, 2026

      Fubara Barazana Ne Ga Demokaraɗiyya – Kakakin Majalisar Rivers

      January 9, 2026

      Kotu Ta Ƙi Bayar da Belin Kwamishinan Kuɗi Na Bauchi

      January 6, 2026
    • Addini

      Kano: Hisbah Ta Karɓi Ƙorafe-Ƙorafe Sama da 12,000 a 2025

      January 2, 2026

      Da Ɗumi-ɗumi : Sheikh Dahiru Bauchi Ya rasu

      November 27, 2025

      Zakaran Gwajin Dafi : Hajji 2025 Karkashin Farfesa Saleh Pakistan  

      November 24, 2025

      Hajji Da Shugabanci Nagari Ƙarƙashin Jagorancin Farfesa Pakistan

      November 17, 2025

      Hukumar NAHCON Ta Sanar Da Rage Kudin Aikin Hajjin 2026

      November 10, 2025
    • Nishadi

      Oculus Founder Makes a VR Headset That Can Literally Kill You

      January 13, 2021
      85

      Braun Series 7 Electric Shaver Review: Quality at a Good Price

      January 13, 2021
      85

      Google Pixel 7, iPhone 14 Compared: Check Out 5 Major Differences

      January 13, 2021

      Why Apple Should Skip The MacBook Pro Launch

      January 12, 2021

      Apollo G2J Showcases Electric Sports Car

      January 12, 2021
    • Tsaro

      Sojojin Najeriya Sun Ƙwato lita 290,000 Na Man Fetur a Yankin Neja Delta

      October 21, 2025

      Ƴan Bindiga Sun Ƙwace Wayoyin Ƴan Sanda a Zamfara

      October 2, 2025

      Gwamnan Kano Ya Buƙaci Tinubu Ya Tsige Kwamishinan Ƴan Sandan Jihar

      October 1, 2025

      Will Using a VPN on Phone Helps Protect You from Ransomware?

      January 14, 2021

      Popular New Xbox Game Pass Game Being Review Bombed With “0s”

      January 14, 2021
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    Home » Ƴan Sanda Sun Kama Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Shanu a Jigawa
    Featured

    Ƴan Sanda Sun Kama Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Shanu a Jigawa

    Abbass AbdurrahmanBy Abbass AbdurrahmanNovember 2, 2025No Comments2 Mins Read

    Rundunar ‘Yan sandan Jihar Jigawa ta kama mutane 10 da ake zargi da satar shanu, tumaki da kuma babur, wanda kimarsu ta kai sama da naira dubu 570,000 a yayin wani samame da aka gudanar don dakile ayyukan masu satar dabbobi a jihar. Mai magana da yawun rundunar, SP Shi’isu Adam, ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da aka fitar a ranar Lahadi, inda ya ce kama waɗannan mutane na daga cikin matakan da rundunar ke ɗauka wajen rage laifuka a yankin.

    A cewar SP Adam, an kama wasu daga cikin masu laifin ne a ranar 22 ga Oktoba bayan samun kiran gaggawa daga al’umma game da satar dabba a yankin Balangu. Masu laifin sun haɗa da Muhd Jafaru, Gidare Kansila, Dare Kabo, Buba Umaru da Manu Musa, waɗanda ake zargi da haɗa kai wajen satar saniya ɗaya mai kimanin naira 450,000 da tumaki masu darajar naira 120,000. Rundunar ta ce an sami nasarar kwato dabbobin da aka sace kuma za a gurfanar da su a kotu nan ba da jimawa ba.

    Haka zalika, a ranar 27 ga Oktoba, jami’an sashen Takur Site sun cafke wani matashi mai suna Mubarak Nasir, ɗan shekara 23, wanda ake zargi da satar babur a Dutse. Bincike ya nuna cewa Nasir ya amsa laifinsa, kuma shari’arsa tana kan tafiya. A wani samame daban a ranar 28 ga Oktoba, rundunar ta Hadejia ta kama wasu maza biyu, Ado Manu da Ibrahim Audu, daga ƙaramar hukumar Kiri Kasamma, bayan an same su da saniya da ake zargi da sacewa daga wani kauye da ake kira Zagari.

    SP Shi’isu Adam ya tabbatar da cewa duk waɗanda aka kama za a gurfanar da su a gaban kotu bayan kammala bincike, tare da jaddada cewa rundunar ta ƙuduri aniyar kawar da satar dabbobi a fadin Jigawa. Ya kuma yi kira ga jama’a da su ci gaba da bayar da bayanai don taimaka wa jami’an tsaro wajen yaki da masu aikata laifi.

    Jigawa
    Share. Facebook Twitter WhatsApp Telegram
    Previous ArticleYan Bindiga Sun Kashe Mutum 17 a Kaduna da Filato
    Next Article Babu Wani Martani Da Na Yi Kan Kalaman Donald Trump – Akpabio
    Abbass Abdurrahman
    • Website

    Related Posts

    Featured

    Gwamnatin Kano Ta Shiryawa Ƴan Jaridar Yanar Gizo Horo Na Yini Biyu a Jigawa

    January 15, 2026
    Featured

    Tanka Ta Murƙushe Mutane 5 a Gombe

    January 12, 2026
    Featured

    Babu Siyasa a Binciken Da Ake Yi Wa Malami – EFCC

    January 12, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    SABBIN LABARAI

    Gwamnatin Kano Ta Dakatar da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi

    October 1, 202542 Views

    Kotu Ta Yankewa Tsohon Firayim Ministan Mali Hukuncin Zaman Gidan Yari Sakamakon Rubutu a Shafin Sada Zumunta

    October 27, 202541 Views

    Dantawaye Ya Zama Sabon Kwamishinan Ƴansanda a Abuja

    October 17, 202532 Views

    An Gano Motar Ofishin Mataimakin Gwamna Da Aka Sace

    November 12, 202527 Views

    NAFDAC Ta Yi Gargaɗi Kan Wani Kororon Roba Me Matuƙar Haɗari Ga Lafiya

    December 30, 202525 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    • Telegram
    © 2026 Bechi Hausa News. Developed by: ENGRMKS & CO.
    • Shafin Farko
    • Game da Mu
    • Ƙarin Bayani
    • Manufar Sirri
    • Ka’idoji da Sharudda
    • Tuntuɓe Mu

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.