Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    • Shafin Farko
    • Labarai

      Matatar Dangote Ta Ƙara Farashin Man Fetur

      March 3, 2026

      Doguwa Ya Yi Murabus Daga Muƙamin Kwamishinan Ruwa Na Kano

      March 3, 2026

      Amurka Na Da Isassun Makaman Yaƙi Da Za a Iya Amfani Da Su “Har Abada” – Trump 

      March 3, 2026

      ICPC Ta Bayyana Abubuwan Da Ta Samo Daga Gidan El-Rufai a Abuja

      March 3, 2026

      Ɗan Atiku Ya Ajiye Muƙamin Kwamishina a Gwamnatin Adamawa

      March 3, 2026
    • Siyasa

      Doguwa Ya Yi Murabus Daga Muƙamin Kwamishinan Ruwa Na Kano

      March 3, 2026

      Gwamnan Adamawa Ya Sauya Sheƙa Zuwa APC

      February 27, 2026

      NDLEA Ta Kama Wata Mata Mai Cikin Bogi Ɗauke da Hodar Iblis a Iyakar Seme

      February 22, 2026

      Jam’iyyun Adawa Sun Kaurace wa Zaɓen Kano, APC Ta Lashe Kujerun Majalisa a Rivers

      February 22, 2026

      Kotu Ta Umarci INEC Ta Yi Wa Jam’iyyar NDP Rajista

      February 19, 2026
    • Addini

      Bauchi Ta neman ƙarin Kujerun Hajji Daga Saudiyya

      February 16, 2026

      Sarkin Musulmi Ya Umarci Ƴan Najeriya Su Fara Duban Jinjirin Watan Ramadan Ranar Talata

      February 16, 2026

      Tinubu Ya Naɗa Ambasada Ismail Abba Yusuf a Matsayin Sabon Shugaban NAHCON

      February 11, 2026

      Sheikh Usman Kusfa Zaria (Rigi-rigi) Ya Rasu

      February 2, 2026

      Jigawa Ta Fara Gwajin Lafiya ga Maniyyatan Hajjin 2026

      January 28, 2026
    • Nishadi

      Oculus Founder Makes a VR Headset That Can Literally Kill You

      January 13, 2021
      85

      Braun Series 7 Electric Shaver Review: Quality at a Good Price

      January 13, 2021
      85

      Google Pixel 7, iPhone 14 Compared: Check Out 5 Major Differences

      January 13, 2021

      Why Apple Should Skip The MacBook Pro Launch

      January 12, 2021

      Apollo G2J Showcases Electric Sports Car

      January 12, 2021
    • Tsaro

      Ba a Fasa Bututun Mai Ko Ɗaya a Niger Delta a 2025 Ba – Sojoj

      January 20, 2026

      Sojojin Najeriya Sun Ƙwato lita 290,000 Na Man Fetur a Yankin Neja Delta

      October 21, 2025

      Ƴan Bindiga Sun Ƙwace Wayoyin Ƴan Sanda a Zamfara

      October 2, 2025

      Gwamnan Kano Ya Buƙaci Tinubu Ya Tsige Kwamishinan Ƴan Sandan Jihar

      October 1, 2025

      Will Using a VPN on Phone Helps Protect You from Ransomware?

      January 14, 2021
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    Home » Gwamnatin Tarayya Za Ta Yi Wa Yara Miliyan 106 Allurar Rigakafi
    Featured

    Gwamnatin Tarayya Za Ta Yi Wa Yara Miliyan 106 Allurar Rigakafi

    Abbass AbdurrahmanBy Abbass AbdurrahmanOctober 12, 2025No Comments2 Mins Read

    Gwamnatin Tarayya tare da jihohi da sun ƙaddamar da gagarumin shirin rigakafin yara sama da miliyan 106 a fadin Najeriya, domin yaƙar cututtukan da ake iya daƙilesu ta hanyar alluran rigakafi. Shirin, wanda zai gudana daga Oktoba 2025 zuwa Fabrairu 2026, ya haɗa da rigakafin cututtuka kamar shan-inna (polio), mashako da rubella (measles–rubella), da kuma rigakafin HPV ga ‘yan mata ‘yan shekaru 9 zuwa 14, tare da rigakafin yau da kullum. Uwargidan Shugaban Kasa, Sanata Oluremi Tinubu, ce ta ƙaddamar da shirin a Abuja a ranar 6 ga Oktoba, inda ta bayyana shi a matsayin muhimmin mataki na kare rayuwar yara a Najeriya.

    Shirin ya fara ne a jihohi 11 da Babban Birnin Tarayya, inda ake gudanar da wayar da kai ta hanyoyi daban-daban ciki har da amfani da motocin sanarwa, haɗin gwiwa da makarantu, iyaye, malamai, kungiyoyin addini da shugabannin gargajiya. Daraktan Rigakafi da Kula da Cututtuka na Hukumar NPHCDA, Dakta Garuba Rufai, ya bayyana cewa an haɗa wannan kamfen da shirye-shiryen lafiya kamar yaki da zazzabin cizon sauro da cututtukan da ake sakaci da su (NTDs).

    A yayin da ake ci gaba da wannan shiri, Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ta jaddada muhimmancin rigakafi, tana mai cewa bai dace a ƙarni na 21 yara su ci gaba da kamuwa da cututtukan da za a iya kare su ba. Dr. Kumshida Balami, mai kula da shirin WHO a FCT, ta bayyana cewa rigakafi abin dogaro ne kuma mai aminci, tana kira ga iyaye da masu kula da yara su tabbatar da cewa an yi wa dukkan yara rigakafi don kare su daga makanta, raunin ji, lahani ga kwakwalwa da mace-mace sakamakon mashako ko rubella.

    Daraktan Hukumar NPHCDA, Dakta Muyi Aina, tare da Sakataran Lafiya na FCTA, Dakta Adedolapo Fasawe, sun jagoranci ƙungiyar sa ido domin tantance yadda aikin ke gudana a cibiyoyin lafiya a Abuja da Kogi. Sun yaba da jajircewar ma’aikatan lafiya tare da tabbatar musu cewa gwamnati na aiki don magance ƙalubalen da suke fuskanta a karkashin shirin gyaran lafiyar “Renewed Hope”. Haka kuma sun yi kira ga iyaye da al’umma da su fita kwansu da kwarkwata su kai ‘ya’yansu wurin yin rigakafi, domin kare su daga cututtuka da za su iya hana su kai matsayin da Allah Ya tsara musu.

    FCT FCTA NPHCDA WHO
    Share. Facebook Twitter WhatsApp Telegram
    Previous ArticleHukumar Kwastam Ta Gargadi Masu Neman Aiki a Hukumar Da Su Guji Labaran Ƙarya Da Ake Yaɗawa
    Next Article Sojoji Sun Kashe Wani Ɗansanda a Bauchi
    Abbass Abdurrahman
    • Website

    Related Posts

    Featured

    Matatar Dangote Ta Ƙara Farashin Man Fetur

    March 3, 2026
    Featured

    Doguwa Ya Yi Murabus Daga Muƙamin Kwamishinan Ruwa Na Kano

    March 3, 2026
    Featured

    Amurka Na Da Isassun Makaman Yaƙi Da Za a Iya Amfani Da Su “Har Abada” – Trump 

    March 3, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    SABBIN LABARAI

    Gwamnatin Kano Ta Dakatar da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi

    October 1, 202544 Views

    Kotu Ta Yankewa Tsohon Firayim Ministan Mali Hukuncin Zaman Gidan Yari Sakamakon Rubutu a Shafin Sada Zumunta

    October 27, 202541 Views

    Dantawaye Ya Zama Sabon Kwamishinan Ƴansanda a Abuja

    October 17, 202532 Views

    NAFDAC Ta Yi Gargaɗi Kan Wani Kororon Roba Me Matuƙar Haɗari Ga Lafiya

    December 30, 202527 Views

    An Gano Motar Ofishin Mataimakin Gwamna Da Aka Sace

    November 12, 202527 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    • Telegram
    © 2026 Bechi Hausa News. Developed by: ENGRMKS & CO.
    • Shafin Farko
    • Game da Mu
    • Ƙarin Bayani
    • Manufar Sirri
    • Ka’idoji da Sharudda
    • Tuntuɓe Mu

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.