Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    • Shafin Farko
    • Labarai

      Najeriya Ta Musanta Zargin Goyon Bayan Yunƙurin Juyin Mulki a Nijar

      September 4, 2026

      A shirye nake na mutu domin kare ƙuri’ata – Peter Obi

      September 4, 2026

      Sarkin Gumel Alhaji Ahmed Muhammad Sani Ya Rasu 

      September 3, 2026

      Gwamnatin Kano ta fitar da iyakoki tsakanin Jam’iar Bayero da alummar Rimin Zakara bayan kammala biyan diyya

      September 3, 2026

      Ƙungiyar Miyetti Allah Ta Buƙaci Tinubu Ya Sa a Saki Shugabanta

      September 3, 2026
    • Siyasa

      A shirye nake na mutu domin kare ƙuri’ata – Peter Obi

      September 4, 2026

      Ɗan Takarar Sanatan Kano ta Tsakiya a NDC Na Shirin Komawa APC

      September 2, 2026

      Ƴan Siyasa Ne Matsalar Najeriya – Peter Obi

      August 31, 2026

      Bai kamata Tinubu ya bar Najeriya a dai dai lokacin da matsaloli ke addabar ƙasarsa ba – Atiku

      August 31, 2026

      Atiku Ya Yi Alkawarin Sake Buɗe Iyakokin Najeriya Idan Ya Lashe Zaɓen 2027

      August 28, 2026
    • Addini

      Shugaban Asibitin Kwararru na Best Choice, Na Taya Gwamnan Kano Da Al’umma Bikin Murnar Maulidi Annabi SAW

      September 2, 2026

      Hajj 2027 : Kano ta kammala sayar da kujeru 3,050 da aka ware wa jihar

      August 31, 2026

      Gwamnatin Kano ta bayar da hutu domin bikin Takutaha

      August 26, 2026

      Wasu Malamai Daga Arewacin Najeriya Sun Goyi Bayan Tazarcen Tinubu

      August 23, 2026

      Gwamnatin Tarayya ta ayyana Talata a matsayin ranar hutun Maulidi

      August 21, 2026
    • Nishadi

      Oculus Founder Makes a VR Headset That Can Literally Kill You

      January 13, 2021
      85

      Braun Series 7 Electric Shaver Review: Quality at a Good Price

      January 13, 2021
      85

      Google Pixel 7, iPhone 14 Compared: Check Out 5 Major Differences

      January 13, 2021

      Why Apple Should Skip The MacBook Pro Launch

      January 12, 2021

      Apollo G2J Showcases Electric Sports Car

      January 12, 2021
    • Tsaro

      Ƴanbindiga Sun Sace Shugaban Jam’iyyar ’iyyar APC Na Ƙaramar Hukumar Rogo

      September 1, 2026

      Amurka Za Ta Janye Sojoji Kusan 200 Daga Najeriya

      August 28, 2026

      Sojoji Sun Kama Ƴan Ƙasashen Waje Da Ake Zargin Suna da Hannu a Matsalar Tsaron Najeriya – Bwala

      July 18, 2026

      ‘Yan Sanda Sun Fara Kwato Makaman Da Ke Hannun Jama’a Ba Bisa Ka’ida Ba – IGP Disu 

      July 17, 2026

      Sojoji Sun Gano Ƴan Ƙasashen Waje Uku Cikin Mayaƙan ISWAP a Borno

      July 13, 2026
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    Home » Ana Fargabar Rashin Abinci Mai Gina Jiki Zai Yi Sanadiyyar Mutuwar Yara 96,000 a Najeriya
    Featured

    Ana Fargabar Rashin Abinci Mai Gina Jiki Zai Yi Sanadiyyar Mutuwar Yara 96,000 a Najeriya

    Abbass AbdurrahmanBy Abbass AbdurrahmanOctober 30, 2025No Comments2 Mins Read

    Kungiyar hadin gwiwar kungiyoyin agaji na ƙasa da ƙasa (INGO Forum) ta yi gargaɗi cewa sama da yara 96,000 a jihohi shida na arewacin Najeriya — Adamawa, Borno, Katsina, Sokoto, Yobe da Zamfara — na cikin haɗarin mutuwa sakamakon matsanancin rashin abinci ami gina jiki. Shugaban Action Against Hunger, Thierno Diallo, ya bayyana cewa lamarin akwai tayar da hankali, inda ya ce kimanin mutane miliyan 31 ke fuskantar ƙarancin abinci a 2025, wanda hakan zai sa Najeriya ta zama ƙasar da ke da mafi girman matsalar abinci a duniya.

    A cewar rahoton, hukumar UNICEF ta ruwaito cewa yara miliyan 11 ‘yan ƙasa da shekara biyar na fama da “ƙarancin abinci” inda suke cin abinci daga ƙananan rukunai, abin da ke ƙara musu yiwuwar fama da lalurar “wasting”. Haka kuma, Hukumar Abincin Duniya (WFP) ta yi hasashen cewa mutane miliyan 33 na iya fuskantar matsanancin yunwa idan ba a ɗauki matakan gaggawa ba, musamman saboda rikice-rikicen tsaro, hauhawar farashi, da sauyin yanayi da ke lalata noma da rayuwa.

    Diallo ya ce cikin watanni uku masu zuwa, yara 600,000 masu ƙasa da shekara biyar za su kasance cikin haɗarin matsanancin rashin abinci mai gina jiki, inda daga cikinsu yara 96,000 za su iya mutuwa idan ba su samu magani ba. Ya ƙara da cewa mata masu juna biyu da masu shayarwa sama da 800,000 ma suna cikin haɗari, yayin da kashi 32% na yara ƙasa da shekara biyar a Najeriya ke da matsalar “stunting” — rashin girma saboda rashin gina jiki.

    Shugaban Save the Children International (Nigeria), Duncan Harvey, da wakilar Plan International, Helen Idiong, sun bukaci gwamnati da abokan hulɗa su ɗauki matakin gaggawa tare da ƙara saka hannun jari wajen yaki da yunwa. Sun bayyana cewa yunwa da rashin abinci mai gina jiki ba wai matsalar jin kai ba ce kawai, har ma da take hakkin ‘ya’yan Najeriya na rayuwa da ci gaba. Sun kuma bukaci ƙarfafa tallafin abinci, magungunan gina jiki, da tsare-tsaren kare talakawa daga matsalolin tattalin arziki a gaba.

    Najeriya
    Share. Facebook Twitter WhatsApp Telegram
    Previous ArticleMajalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Dr. Bernard Doro a Matsayin Minista
    Next Article APC Ta Samu Rinjayen Kashi Biyu Cikin Uku a Zauren Majalisar Wakilai
    Abbass Abdurrahman
    • Website

    Related Posts

    Featured

    Najeriya Ta Musanta Zargin Goyon Bayan Yunƙurin Juyin Mulki a Nijar

    September 4, 2026
    Featured

    A shirye nake na mutu domin kare ƙuri’ata – Peter Obi

    September 4, 2026
    Featured

    Sarkin Gumel Alhaji Ahmed Muhammad Sani Ya Rasu 

    September 3, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    SABBIN LABARAI

    Ba Don Gudunmawar Masu Yiwa Ƙasa Hidima Ba Da Jihohi Dayawa Basu Kai Yadda Suke a Yanzu Ba – Minista

    December 8, 2025229 Views

    Sabon Rikici Ya Kunno Kai a NDC : Ƴan Takara Sun Kai Ƙara Kan Zaɓen Fidda-gwani a Kano

    June 30, 202680 Views

    Gwamnatin Kano Ta Dakatar da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi

    October 1, 202551 Views

    Gwamnatin Kano Ta Raba Filaye Ga Masu Taimakawa Gwamna Sama da 2,500

    August 1, 202644 Views

    Kotu Ta Yankewa Tsohon Firayim Ministan Mali Hukuncin Zaman Gidan Yari Sakamakon Rubutu a Shafin Sada Zumunta

    October 27, 202541 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    • Telegram
    © 2026 Bechi Hausa News. Developed by: ENGRMKS & CO.
    • Shafin Farko
    • Game da Mu
    • Ƙarin Bayani
    • Manufar Sirri
    • Ka’idoji da Sharudda
    • Tuntuɓe Mu

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.