Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    • Shafin Farko
    • Labarai

      Kotu Ta Sake Dakatar Da Babban Taron PDP

      November 11, 2025

      Bayan 2026 Bazan Sake Buga Gasar Kofin Duniya Ba – Ronaldo

      November 11, 2025

      Masu Zanga-zanga Sun Isa Majalisar Dokoki Dan Neman Tabbatar Da Ramat a Matsayin Shugaban NERC

      November 11, 2025

      Mutane Miliyan 24 Na Fama Da Ciwon Suga a Afrika – WHO

      November 11, 2025

      EFCC Na Neman Tsohon Gwamnan Bayelsa Ruwa-a-Jallo

      November 11, 2025
    • Siyasa

      Kotu Ta Sake Dakatar Da Babban Taron PDP

      November 11, 2025

      INEC Ta Ayyana Soludo a Matsayin Wanda Ya Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra

      November 9, 2025

      An Rantsar Da Shugaban Ƙasa Mafi Tsufa a Duniya

      November 7, 2025

      Gombe Na Amfana Da Cire Tallafin Man Fetur – Inuwa Yahya

      November 4, 2025

      Sabon Rikici Na Shirin Kunno Kai Tsakanin Sanata Natasha Da Akpabio

      November 4, 2025
    • Addini

      Hukumar NAHCON Ta Sanar Da Rage Kudin Aikin Hajjin 2026

      November 10, 2025

      Ƙungiyoyin Fityanul Islam Da Samarin Tijjaniyya Sun Yi Ƙarar Gwamnatin Kano a Kotu

      November 5, 2025

      Saudiyya Ta Ragewa Najeriya Kujerun Hajjin 2026

      October 17, 2025

      Sarkin Musulmi Ya Buƙaci a Samar Da Dokokin Amfani Da Kafafen Sada Zumunta a Najeriya

      October 16, 2025

      Hisbah Ta Kama Wasu Matasa Da Laifin Yin Aure Ba Tare Da Amincewar Iyayensu Ba

      October 13, 2025
    • Nishadi

      Oculus Founder Makes a VR Headset That Can Literally Kill You

      January 13, 2021
      85

      Braun Series 7 Electric Shaver Review: Quality at a Good Price

      January 13, 2021
      85

      Google Pixel 7, iPhone 14 Compared: Check Out 5 Major Differences

      January 13, 2021

      Why Apple Should Skip The MacBook Pro Launch

      January 12, 2021

      Apollo G2J Showcases Electric Sports Car

      January 12, 2021
    • Tsaro

      Sojojin Najeriya Sun Ƙwato lita 290,000 Na Man Fetur a Yankin Neja Delta

      October 21, 2025

      Ƴan Bindiga Sun Ƙwace Wayoyin Ƴan Sanda a Zamfara

      October 2, 2025

      Gwamnan Kano Ya Buƙaci Tinubu Ya Tsige Kwamishinan Ƴan Sandan Jihar

      October 1, 2025

      Will Using a VPN on Phone Helps Protect You from Ransomware?

      January 14, 2021

      Popular New Xbox Game Pass Game Being Review Bombed With “0s”

      January 14, 2021
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    Home » Mutane Miliyan 24 Na Fama Da Ciwon Suga a Afrika – WHO
    Featured

    Mutane Miliyan 24 Na Fama Da Ciwon Suga a Afrika – WHO

    Abbass AbdurrahmanBy Abbass AbdurrahmanNovember 11, 2025No Comments2 Mins Read

    Hukumar Lafiya ta Duniya WHO ta bayyana cewa akalla mutane miliyan 24 masu shekaru tsakanin 20 zuwa 79 suna fama da ciwon suga a nahiyar Afirka. Rahoton ya nuna cewa rabin wannan adadi, kusan miliyan 12, ba su ma san suna da cutar ba, lamarin da ke ƙara haɗarin samun nakasa, rikicewar jiki ko mutuwa kafin lokaci. WHO ta yi gargadin cewa idan ba a dauki matakin gaggawa ba, yawan masu ciwon suga zai kai miliyan 60 nan da shekara ta 2050.

    Daraktan WHO na yankin Afirka, Dr. Mohamed Janabi, ya ce wannan ƙaruwa tana da nasaba da sabuwar rayuwa ta zamani, rashin motsa jiki, yawaitar kiba, da kuma ƙarancin samun kulawa a asibitoci. Ya bayyana cewa ciwon suga kan iya lalata zuciya, koda, idanu da jijiyoyi, wanda hakan ke jefa iyalai da al’umma cikin tashin hankali da karin nauyin kashe kuɗin jinya.

    Ya ce taken bikin Ranar Ciwon Suga ta bana shi ne “Diabetes Across Life Stages” wato ciwon suga ba ya barin kowa; yara, matasa, manya da tsofaffi na iya kamuwa da shi. Don haka ya ce ana bukatar kulawa daga matakin rigakafi har zuwa gano cuta da kula da ita na tsawon rayuwa. Ya kuma tunatar da cewa kasashen Afirka sun amince su daidaita tsarin yaki da cutar tun shekarar 2024.

    Janabi ya ce WHO na tallafa wa kasashe wajen aiwatar da hanyoyin kula da marasa lafiya a matakin cibiyoyin kiwon lafiya na farko, musamman ta hanyar shirin WHO PEN da PEN-Plus da ake amfani da su a ƙasashe da dama. Ya bukaci gwamnati a nahiyar ta karfafa kasafin kudi ga cututtukan da ba sa yaduwa, da kuma haɗa yaki da ciwon suga cikin shirin lafiya na kasa domin kare rayuka da inganta lafiya baki daya.

    WHO
    Share. Facebook Twitter WhatsApp Telegram
    Previous ArticleEFCC Na Neman Tsohon Gwamnan Bayelsa Ruwa-a-Jallo
    Next Article Masu Zanga-zanga Sun Isa Majalisar Dokoki Dan Neman Tabbatar Da Ramat a Matsayin Shugaban NERC
    Abbass Abdurrahman
    • Website

    Related Posts

    Featured

    Kotu Ta Sake Dakatar Da Babban Taron PDP

    November 11, 2025
    Featured

    Bayan 2026 Bazan Sake Buga Gasar Kofin Duniya Ba – Ronaldo

    November 11, 2025
    Featured

    Masu Zanga-zanga Sun Isa Majalisar Dokoki Dan Neman Tabbatar Da Ramat a Matsayin Shugaban NERC

    November 11, 2025
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    SABBIN LABARAI

    Gwamnatin Kano Ta Dakatar da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi

    October 1, 202537 Views

    Kotu Ta Yankewa Tsohon Firayim Ministan Mali Hukuncin Zaman Gidan Yari Sakamakon Rubutu a Shafin Sada Zumunta

    October 27, 202536 Views

    Dantawaye Ya Zama Sabon Kwamishinan Ƴansanda a Abuja

    October 17, 202526 Views

    Matuƙar Ba’a Yi Yadda Aka Yi a Afghanistan Ba Baza’a Kawo Ƙarshen Ta’addanci a Najeriya Ba – Amurka

    November 6, 202522 Views

    Zama a Banɗaki Fiye Da Kima Kan Haifar Da Matsala Ga Lafiyar Ɗan Adam – Likita

    October 28, 202520 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    • Telegram
    © 2025 Bechi Hausa News. Developed by: ENGRMKS & CO.
    • Shafin Farko
    • Game da Mu
    • Ƙarin Bayani
    • Manufar Sirri
    • Ka’idoji da Sharudda
    • Tuntuɓe Mu

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.