Amurka da Najeriya sun gudanar da taron farko a Abuja domin ƙarfafa haɗin gwiwar tsaro da kare fararen hula daga hare-haren ƙungiyoyi masu ɗauke da makamai ƴanbindiga. Taron ya mayar da hankali ne kan tabbatar da cewa mabiya dukkan addinai za su iya gudanar da addininsu cikin aminci ba tare da tsoro ba.
Taron ya biyo bayan ayyana Najeriya a matsayin ƙasar da ake da damuwa a kanta, musamman dangane da ikirarin kisan kiyashi kan Kiristoci, zargin da hukumomin Najeriya suka musanta. Amurka ta yaba da ƙoƙarin da Najeriya ke yi na shawo kan matsalar rashin tsaro, musamman a jihohin Arewa ta Tsakiya.
Mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro, Nuhu Ribadu, ya jagoranci tawagar Najeriya, yayin da mataimakiyar sakataren harkokin wajen Amurka, Allison Hooker, ta jagoranci tawagar Amurka. Sanarwar haɗin gwiwa da aka fitar ranar Alhamis ta jaddada ƙudurin ƙasashen biyu na kare ƴancin addini, ƴancin faɗin albarkacin baki, da musayar bayanan sirri domin yaki da ta’addanci a arewacin Najeriya.

