Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II, ya bayyana cewa ba sai kundin tsarin mulki ya ba shi izini ba kafin ya ba shugaban ƙasa ko gwamnan jiha shawara kan al’amuran ƙasa. Ya ce sarakunan gargajiya ginshiƙai ne na gina ƙasa da kyakkyawan shugabanci.
Sarkin ya yi wannan bayani ne a shirin Morning Brief na Channels Television a ranar Laraba, inda ya ce ikon ba da shawara ya samo asali ne daga jagorancin al’ummar da yake yi. A cewarsa, duk da girmama ikon zartarwa na gwamnoni, sarakunan gargajiya na da rawar da za su taka wajen nuna abin da ya dace ga ƙasa.
Sarki Sanusi ya kuma jaddada muhimmancin shigar mata cikin harkokin siyasa da gina ƙasa, yana mai kira da a ƙara wakilcinsu a mukaman zaɓe. Haka nan ya yi Allah-wadai da cin zarafin mata, yana mai cewa babu wata al’ada da za ta halatta tauye haƙƙin ’yan ƙasa.

