Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    • Shafin Farko
    • Labarai

      Gwamnatin Kano Ta Shiryawa Ƴan Jaridar Yanar Gizo Horo Na Yini Biyu a Jigawa

      January 15, 2026

      Tanka Ta Murƙushe Mutane 5 a Gombe

      January 12, 2026

      Babu Siyasa a Binciken Da Ake Yi Wa Malami – EFCC

      January 12, 2026

      Ƴan Bindiga Sun Kashe Soja Da Jam’in NSCDC a Benue

      January 12, 2026

      Manyan Jiga-jigan APC 3 a Kogi Sun Mutu

      January 12, 2026
    • Siyasa

      Manyan Jiga-jigan APC 3 a Kogi Sun Mutu

      January 12, 2026

      Ganduje Zai Gana Da Masu Ruwa-da-tsaki Na APC

      January 11, 2026

      Datti Baba-Ahmed Ya Musanta Batun Tsayawa Takarar Shugaban Ƙasa

      January 9, 2026

      Fubara Barazana Ne Ga Demokaraɗiyya – Kakakin Majalisar Rivers

      January 9, 2026

      Kotu Ta Ƙi Bayar da Belin Kwamishinan Kuɗi Na Bauchi

      January 6, 2026
    • Addini

      Kano: Hisbah Ta Karɓi Ƙorafe-Ƙorafe Sama da 12,000 a 2025

      January 2, 2026

      Da Ɗumi-ɗumi : Sheikh Dahiru Bauchi Ya rasu

      November 27, 2025

      Zakaran Gwajin Dafi : Hajji 2025 Karkashin Farfesa Saleh Pakistan  

      November 24, 2025

      Hajji Da Shugabanci Nagari Ƙarƙashin Jagorancin Farfesa Pakistan

      November 17, 2025

      Hukumar NAHCON Ta Sanar Da Rage Kudin Aikin Hajjin 2026

      November 10, 2025
    • Nishadi

      Oculus Founder Makes a VR Headset That Can Literally Kill You

      January 13, 2021
      85

      Braun Series 7 Electric Shaver Review: Quality at a Good Price

      January 13, 2021
      85

      Google Pixel 7, iPhone 14 Compared: Check Out 5 Major Differences

      January 13, 2021

      Why Apple Should Skip The MacBook Pro Launch

      January 12, 2021

      Apollo G2J Showcases Electric Sports Car

      January 12, 2021
    • Tsaro

      Sojojin Najeriya Sun Ƙwato lita 290,000 Na Man Fetur a Yankin Neja Delta

      October 21, 2025

      Ƴan Bindiga Sun Ƙwace Wayoyin Ƴan Sanda a Zamfara

      October 2, 2025

      Gwamnan Kano Ya Buƙaci Tinubu Ya Tsige Kwamishinan Ƴan Sandan Jihar

      October 1, 2025

      Will Using a VPN on Phone Helps Protect You from Ransomware?

      January 14, 2021

      Popular New Xbox Game Pass Game Being Review Bombed With “0s”

      January 14, 2021
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    Home » Bazan Damu Ba Don Atiku Ya Samu Tikitin Takara a ADC — Obi
    Featured

    Bazan Damu Ba Don Atiku Ya Samu Tikitin Takara a ADC — Obi

    Abbass AbdurrahmanBy Abbass AbdurrahmanOctober 19, 2025No Comments2 Mins Read

    Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar Labour a zaɓen 2023, Peter Obi, ya ce bai ji tsoron cewa tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, zai karɓe tikitin takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ba a zaɓen 2027. Obi ya bayyana haka ne yayin wata hira da jaridar Sunday PUNCH a Abuja, inda ya bayyana Atiku a matsayin “babba kuma jagora.”

    Maganganunsa na zuwa ne bayan rahotanni da ke nuna cewa magoya bayan Atiku daga jam’iyyar PDP na komawa cikin hadakar ADC, abin da ya jefa magoya bayan Obi cikin fargabar yiwuwar Atiku ya mamaye jam’iyyar. Hakan ya ƙara tayar da ƙura bayan maganar da Atiku ya fada a wata hira da BBC Hausa cewa ba zai ja daga takara ba sai dai idan aka kayar da shi a zaben fidda gwani na ADC. Tsohon sanata Shehu Sani ma ya gargadi cewa zai zama da wahala a kayar da Atiku idan ya shiga kowace jam’iyya.

    Sai dai Obi ya bayyana cewa hadakar ADC ba fagen gasa ba ce, illa wani yunƙuri na haɗa ƙarfi don ceto ƙasa. Ya ce, “Atiku babban ɗan uwa ne kuma jagora. Ni mamba ne na jam’iyyar Labour kuma ina cikin hadakar da ke samar da ADC don zaɓen 2027. Dukkanmu za mu haɗu a matsayin mutane masu kishin ƙasa domin yin abin da ya dace.” Ya kuma nuna cewa yana da niyyar tsayawa takara, yana mai cewa cancanta da iya aiki su ne abin dubawa wajen zaɓar shugaba mai zuwa.

    Obi ya jaddada cewa yana da ƙwarewa da ƙudurin sauya tafiyar Najeriya cikin shekaru huɗu. Ya kuma kira ’yan Najeriya da su mayar da hankali kan manufofi da walwalar al’umma maimakon jam’iyyu kawai. Obi da Atiku duka sun sha kaye a hannun Bola Tinubu a zaɓen 2023, wanda ya kasance ɗaya daga cikin mafi zafi a tarihin dimokuraɗiyyar Najeriya.

    ADC
    Share. Facebook Twitter WhatsApp Telegram
    Previous ArticleBamu Nemi Kotu Ta Hana Gudanar Da Zanga-zangar Sakin Nnamdi Kanu Ba – Ƴansanda
    Next Article Matuƙar Atiku Ya Goyawa Obi Baya Tabbas Za Su Kayar Da Tinubu a 2027 – LP
    Abbass Abdurrahman
    • Website

    Related Posts

    Featured

    Gwamnatin Kano Ta Shiryawa Ƴan Jaridar Yanar Gizo Horo Na Yini Biyu a Jigawa

    January 15, 2026
    Featured

    Tanka Ta Murƙushe Mutane 5 a Gombe

    January 12, 2026
    Featured

    Babu Siyasa a Binciken Da Ake Yi Wa Malami – EFCC

    January 12, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    SABBIN LABARAI

    Gwamnatin Kano Ta Dakatar da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi

    October 1, 202542 Views

    Kotu Ta Yankewa Tsohon Firayim Ministan Mali Hukuncin Zaman Gidan Yari Sakamakon Rubutu a Shafin Sada Zumunta

    October 27, 202541 Views

    Dantawaye Ya Zama Sabon Kwamishinan Ƴansanda a Abuja

    October 17, 202532 Views

    An Gano Motar Ofishin Mataimakin Gwamna Da Aka Sace

    November 12, 202527 Views

    NAFDAC Ta Yi Gargaɗi Kan Wani Kororon Roba Me Matuƙar Haɗari Ga Lafiya

    December 30, 202525 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    • Telegram
    © 2026 Bechi Hausa News. Developed by: ENGRMKS & CO.
    • Shafin Farko
    • Game da Mu
    • Ƙarin Bayani
    • Manufar Sirri
    • Ka’idoji da Sharudda
    • Tuntuɓe Mu

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.