Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    • Shafin Farko
    • Labarai

      Jirage Marasa Matuƙa Sun Kai Hari Matatar Man Saudiyya

      March 2, 2026

      Najeriya Ta Buƙaci a Kawo Karshen Rikicin Gabas ta Tsakiya

      March 2, 2026

      Iran Ta Naɗa Ayatollah Arafi A Matsayin Jagoran Addini Na Riƙo

      March 1, 2026

      Majalisar Dattawa Ta Sha Alwashin Amincewa da Dokar Kafa ‘Yan Sandan Jihohi Kafin Ƙarshen 2026

      March 1, 2026

      Iran Ta Ayyana Zaman Makoki na Kwanaki 40 Bayan Mutuwar Jagora Ayatoullah Khamenei 

      March 1, 2026
    • Siyasa

      Gwamnan Adamawa Ya Sauya Sheƙa Zuwa APC

      February 27, 2026

      NDLEA Ta Kama Wata Mata Mai Cikin Bogi Ɗauke da Hodar Iblis a Iyakar Seme

      February 22, 2026

      Jam’iyyun Adawa Sun Kaurace wa Zaɓen Kano, APC Ta Lashe Kujerun Majalisa a Rivers

      February 22, 2026

      Kotu Ta Umarci INEC Ta Yi Wa Jam’iyyar NDP Rajista

      February 19, 2026

      Gwamnan Zamfara Ya Zargi Gwamnatin Tarayya da Nuna Masa Wariya Saboda Bambancin Jam’iyya

      February 18, 2026
    • Addini

      Bauchi Ta neman ƙarin Kujerun Hajji Daga Saudiyya

      February 16, 2026

      Sarkin Musulmi Ya Umarci Ƴan Najeriya Su Fara Duban Jinjirin Watan Ramadan Ranar Talata

      February 16, 2026

      Tinubu Ya Naɗa Ambasada Ismail Abba Yusuf a Matsayin Sabon Shugaban NAHCON

      February 11, 2026

      Sheikh Usman Kusfa Zaria (Rigi-rigi) Ya Rasu

      February 2, 2026

      Jigawa Ta Fara Gwajin Lafiya ga Maniyyatan Hajjin 2026

      January 28, 2026
    • Nishadi

      Oculus Founder Makes a VR Headset That Can Literally Kill You

      January 13, 2021
      85

      Braun Series 7 Electric Shaver Review: Quality at a Good Price

      January 13, 2021
      85

      Google Pixel 7, iPhone 14 Compared: Check Out 5 Major Differences

      January 13, 2021

      Why Apple Should Skip The MacBook Pro Launch

      January 12, 2021

      Apollo G2J Showcases Electric Sports Car

      January 12, 2021
    • Tsaro

      Ba a Fasa Bututun Mai Ko Ɗaya a Niger Delta a 2025 Ba – Sojoj

      January 20, 2026

      Sojojin Najeriya Sun Ƙwato lita 290,000 Na Man Fetur a Yankin Neja Delta

      October 21, 2025

      Ƴan Bindiga Sun Ƙwace Wayoyin Ƴan Sanda a Zamfara

      October 2, 2025

      Gwamnan Kano Ya Buƙaci Tinubu Ya Tsige Kwamishinan Ƴan Sandan Jihar

      October 1, 2025

      Will Using a VPN on Phone Helps Protect You from Ransomware?

      January 14, 2021
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    Home » EFCC Na Neman Tsohon Gwamnan Bayelsa Ruwa-a-Jallo
    Featured

    EFCC Na Neman Tsohon Gwamnan Bayelsa Ruwa-a-Jallo

    Abbass AbdurrahmanBy Abbass AbdurrahmanNovember 11, 2025No Comments2 Mins Read

    Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa EFCC ta ayyana tsohon Gwamnan Jihar Bayelsa kuma tsohon Ministan Albarkatun Man Fetur, Chief Timipre Sylva, a matsayin wanda take nema ruwa-a-jallo, bisa zargin hada baki da karkatar da dala miliyan $14.8. EFCC ta ce kudaden sun fito ne daga tallafin da Hukumar Kula da Cigaban Albarkatun Man Najeriya (NCDMB) ta saka a aikin gina masana’antar tace mai a Brass, cikin Bayelsa, wanda kamfanin Atlantic International Refinery ke jagoranta.

    Rahotanni sun nuna cewa an zuba dala miliyan $35 a aikin tun 2020 don gina masana’antar mai mai iya tace ganga 2,000 a rana tare da wasu kayayyaki kamar tashar jiragen ruwa da wutar lantarki, amma har yanzu aikin ya tsaya cak babu wani ci gaba da za a gani. EFCC ta riga ta kama da kuma gudanar da bincike kan shugabannin wasu daga cikin masu gudanar da aikin, ciki har da tsohon sakataren NCDMB da kuma shugaban kamfanin da ya jagoranci shirin.

    Sai dai Sylva ta bakin mai magana da yawunsa, Julius Bokoru, ya karyata zargin, yana cewa wannan mataki wani sabon yunkuri ne na bata masa suna ta siyasa. Ya ce EFCC ba ta kira ko sanar da shi kafin fitar da sanarwar neman sa ba, kuma hakan ya nuna an shirya lamarin ne domin tada jijiyoyin wuya da tunzura jama’a. Ya kara da cewa Sylva yanzu yana kasar Birtaniya domin duba lafiyarsa.

    Tawagar Sylva ta ce za shi girmama duk wata gayyata daga hukumar idan aka turo ta yadda ya dace, tare da jaddada cewa aikin gina matatar mai yana da cikakken takardu da tsarin aiki. Sun roki magoya baya su kwantar da hankula, suna mai cewa gaskiya za ta bayyana daga karshe, duk wani yunkuri na rage tasirin siyasar Sylva ba zai yi nasara ba.

    EFCC
    Share. Facebook Twitter WhatsApp Telegram
    Previous ArticleAmbaliyar Ruwa Ta Hallaka Mutane 241 Yayin Da Dubbai Suka Rasa Muhallinsu a 2025 – NEMA
    Next Article Mutane Miliyan 24 Na Fama Da Ciwon Suga a Afrika – WHO
    Abbass Abdurrahman
    • Website

    Related Posts

    Featured

    Jirage Marasa Matuƙa Sun Kai Hari Matatar Man Saudiyya

    March 2, 2026
    Featured

    Najeriya Ta Buƙaci a Kawo Karshen Rikicin Gabas ta Tsakiya

    March 2, 2026
    Featured

    Iran Ta Naɗa Ayatollah Arafi A Matsayin Jagoran Addini Na Riƙo

    March 1, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    SABBIN LABARAI

    Gwamnatin Kano Ta Dakatar da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi

    October 1, 202543 Views

    Kotu Ta Yankewa Tsohon Firayim Ministan Mali Hukuncin Zaman Gidan Yari Sakamakon Rubutu a Shafin Sada Zumunta

    October 27, 202541 Views

    Dantawaye Ya Zama Sabon Kwamishinan Ƴansanda a Abuja

    October 17, 202532 Views

    NAFDAC Ta Yi Gargaɗi Kan Wani Kororon Roba Me Matuƙar Haɗari Ga Lafiya

    December 30, 202527 Views

    An Gano Motar Ofishin Mataimakin Gwamna Da Aka Sace

    November 12, 202527 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    • Telegram
    © 2026 Bechi Hausa News. Developed by: ENGRMKS & CO.
    • Shafin Farko
    • Game da Mu
    • Ƙarin Bayani
    • Manufar Sirri
    • Ka’idoji da Sharudda
    • Tuntuɓe Mu

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.