Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed, ya sallami Kwamishinan Tsaron Cikin Gida da Harkokin Cikin Gida, Alhaji Ibrahim Gambo Galadima, daga mukaminsa nan take. An yanke wannan shawara ne a wani sauyi ƙanana da aka yi a cikin majalisar zartarwar jihar.
Sanarwar sallamar ta fito ne ta hannun Mai Ba Gwamna Shawara kan Harkokin Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Kwamared Mukhtar Gidado, a safiyar Litinin. Sanarwar ta ce gwamnan ya amince da sake fasalin majalisar domin ƙara inganta tafiyar da mulki a jihar.
Gwamna Bala Mohammed ya gode wa Galadima bisa gudunmawar da ya bayar a lokacin da yake kan mukamin, tare da yi masa fatan alheri a nan gaba. Haka kuma gwamnan ya tabbatar wa al’ummar Bauchi cewa gwamnatinsa na ci gaba da jajircewa wajen tabbatar da zaman lafiya, tsaro da kyakkyawan shugabanci, yayin da aka ce za a sanar da wanda zai maye gurbinsa nan gaba.

