Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    • Shafin Farko
    • Labarai

      Mutane 2 Sun Mutu, 8 Sun Jikkata a Harin Boko Haram a Yobe

      March 4, 2026

      ADC Ta Nuna Goyon Bayanta Ga El-Rufai Da Malami

      March 4, 2026

      Matatar Dangote Ta Ƙara Farashin Man Fetur

      March 3, 2026

      Doguwa Ya Yi Murabus Daga Muƙamin Kwamishinan Ruwa Na Kano

      March 3, 2026

      Amurka Na Da Isassun Makaman Yaƙi Da Za a Iya Amfani Da Su “Har Abada” – Trump 

      March 3, 2026
    • Siyasa

      ADC Ta Nuna Goyon Bayanta Ga El-Rufai Da Malami

      March 4, 2026

      Doguwa Ya Yi Murabus Daga Muƙamin Kwamishinan Ruwa Na Kano

      March 3, 2026

      Gwamnan Adamawa Ya Sauya Sheƙa Zuwa APC

      February 27, 2026

      NDLEA Ta Kama Wata Mata Mai Cikin Bogi Ɗauke da Hodar Iblis a Iyakar Seme

      February 22, 2026

      Jam’iyyun Adawa Sun Kaurace wa Zaɓen Kano, APC Ta Lashe Kujerun Majalisa a Rivers

      February 22, 2026
    • Addini

      Bauchi Ta neman ƙarin Kujerun Hajji Daga Saudiyya

      February 16, 2026

      Sarkin Musulmi Ya Umarci Ƴan Najeriya Su Fara Duban Jinjirin Watan Ramadan Ranar Talata

      February 16, 2026

      Tinubu Ya Naɗa Ambasada Ismail Abba Yusuf a Matsayin Sabon Shugaban NAHCON

      February 11, 2026

      Sheikh Usman Kusfa Zaria (Rigi-rigi) Ya Rasu

      February 2, 2026

      Jigawa Ta Fara Gwajin Lafiya ga Maniyyatan Hajjin 2026

      January 28, 2026
    • Nishadi

      Oculus Founder Makes a VR Headset That Can Literally Kill You

      January 13, 2021
      85

      Braun Series 7 Electric Shaver Review: Quality at a Good Price

      January 13, 2021
      85

      Google Pixel 7, iPhone 14 Compared: Check Out 5 Major Differences

      January 13, 2021

      Why Apple Should Skip The MacBook Pro Launch

      January 12, 2021

      Apollo G2J Showcases Electric Sports Car

      January 12, 2021
    • Tsaro

      Ba a Fasa Bututun Mai Ko Ɗaya a Niger Delta a 2025 Ba – Sojoj

      January 20, 2026

      Sojojin Najeriya Sun Ƙwato lita 290,000 Na Man Fetur a Yankin Neja Delta

      October 21, 2025

      Ƴan Bindiga Sun Ƙwace Wayoyin Ƴan Sanda a Zamfara

      October 2, 2025

      Gwamnan Kano Ya Buƙaci Tinubu Ya Tsige Kwamishinan Ƴan Sandan Jihar

      October 1, 2025

      Will Using a VPN on Phone Helps Protect You from Ransomware?

      January 14, 2021
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    Home » Gwamnatin Kwara Ta Biya Ƴan Fansho Naira Biliyan 3.3
    Featured

    Gwamnatin Kwara Ta Biya Ƴan Fansho Naira Biliyan 3.3

    Abbass AbdurrahmanBy Abbass AbdurrahmanOctober 23, 2025No Comments2 Mins Read

    Gwamnatin Jihar Kwara ta bayyana cewa ta biya bashin fansho da ya kai naira biliyan 3.3 da ta gada daga tsohuwar gwamnati, domin rage tarin bashin da ake bin tsofaffin ma’aikatan kananan hukumomi a fadin jihar. Kamar yadda Kwamishiniyar Kudi, Dr. Hauwa Nuhu, ta bayyana a Ilorin yayin taron manema labarai na zango na uku na shekara ta 2025, gwamnatin ta ce ta gaji bashi da ya kai naira biliyan 19 tun daga shekarar 2009, inda har yanzu naira biliyan 12 daga ciki aka iya biya.

    A cewar Nuhu, an kammala biyan hakkokin ma’aikatan kananan hukumomi har zuwa shekarar 2011, yayin da aka ware naira biliyan 2.5 domin biyan bashin shekarun 2012, 2013 da 2014. Ta kuma ce biyan fansho na ma’aikatan jiha ya kai har zuwa shekarar 2016, duk da cewa har yanzu ana bin gwamnatin naira biliyan 22. Don rage wannan nauyi, gwamnatin ta ware naira biliyan 5.6 daga kudaden harajin cikin gida na zangon uku na 2025 domin ci gaba da biyan waɗannan hakkoki.

    Kwamishinar ta bayyana cewa jihar ta samu naira biliyan 15.7 daga harajin cikin gida a zango na uku na shekarar 2025, kuma duka an tura su kai tsaye zuwa asusun gwamnati na Treasury Single Account (TSA) domin tabbatar da gaskiya da bin doka. Ta ce jimillar bashin cikin gida na jihar yanzu ya kai naira biliyan 57, wanda ya haɗa da fansho da bashin ma’aikata.

    Dr. Nuhu ta danganta yawaitar bashin fansho da aiwatar da karin albashi na ₦30,000 da ₦70,000 da gwamnatin AbdulRahman AbdulRazaq ta kaddamar. Sai dai ta tabbatar da cewa gwamnati na ci gaba da biyan bashin a hankali tare da bayyana komai a fili ga jama’a. “Babu wani abu da muke ɓoyewa — kowane ɗan Kwara na iya ganin yadda ake aiwatar da kasafin kudin mu a shafin gwamnati,” a cewar ta.

    Gwamnatin Kwara
    Share. Facebook Twitter WhatsApp Telegram
    Previous ArticleNajeriya Ta Shigo Da Lita Biliyan 15 Na Fetur Duk Da Samuwar Masana’antar Dangote — NMDPRA
    Next Article Jihohin Najeriya Za Su Rabauta Da Naira Biliyan 32 Daga Gwamnatin Tarayya
    Abbass Abdurrahman
    • Website

    Related Posts

    Featured

    Mutane 2 Sun Mutu, 8 Sun Jikkata a Harin Boko Haram a Yobe

    March 4, 2026
    Featured

    ADC Ta Nuna Goyon Bayanta Ga El-Rufai Da Malami

    March 4, 2026
    Featured

    Matatar Dangote Ta Ƙara Farashin Man Fetur

    March 3, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    SABBIN LABARAI

    Gwamnatin Kano Ta Dakatar da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi

    October 1, 202544 Views

    Kotu Ta Yankewa Tsohon Firayim Ministan Mali Hukuncin Zaman Gidan Yari Sakamakon Rubutu a Shafin Sada Zumunta

    October 27, 202541 Views

    Dantawaye Ya Zama Sabon Kwamishinan Ƴansanda a Abuja

    October 17, 202532 Views

    NAFDAC Ta Yi Gargaɗi Kan Wani Kororon Roba Me Matuƙar Haɗari Ga Lafiya

    December 30, 202527 Views

    An Gano Motar Ofishin Mataimakin Gwamna Da Aka Sace

    November 12, 202527 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    • Telegram
    © 2026 Bechi Hausa News. Developed by: ENGRMKS & CO.
    • Shafin Farko
    • Game da Mu
    • Ƙarin Bayani
    • Manufar Sirri
    • Ka’idoji da Sharudda
    • Tuntuɓe Mu

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.