Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    • Shafin Farko
    • Labarai

      Tinubu Ya Sha Alwashin Murƙushe Ta’addanci a Najeriya

      November 6, 2025

      Hukumar Kiyaye Afkuwar Haɗura Ta Ƙasa Ta Kama Direbobi 27,000 a Abuja

      November 6, 2025

      Gidaje 20 Da Ake Zargina a Kansu Ba Nawa Bane Ne Waɗanda Mahaifinmu Ya Bar Mana Gado Ne – Abba Kyari

      November 6, 2025

      Matuƙar Ba’a Yi Yadda Aka Yi a Afghanistan Ba Baza’a Kawo Ƙarshen Ta’addanci a Najeriya Ba – Amurka

      November 6, 2025

      Shekarau @ 70: Damuwa Bata Taɓa Hanani Bacci Ba – Shekarau

      November 6, 2025
    • Siyasa

      Gombe Na Amfana Da Cire Tallafin Man Fetur – Inuwa Yahya

      November 4, 2025

      Sabon Rikici Na Shirin Kunno Kai Tsakanin Sanata Natasha Da Akpabio

      November 4, 2025

      Har Yanzu Bamu Janye Dakatarwar Shekaru 30 Da Mu Ka Yi Wa El-Rufai Ba – SDP

      November 2, 2025

      Gwamnan Taraba Zai Koma Jam’iyyar APC

      October 29, 2025

      Gwamnonin PDP Sun Zaɓi Tanimu Turaki a Matsayin Ɗan Takararsu a Zaɓen Shugabancin Jam’iyya

      October 25, 2025
    • Addini

      Ƙungiyoyin Fityanul Islam Da Samarin Tijjaniyya Sun Yi Ƙarar Gwamnatin Kano a Kotu

      November 5, 2025

      Saudiyya Ta Ragewa Najeriya Kujerun Hajjin 2026

      October 17, 2025

      Sarkin Musulmi Ya Buƙaci a Samar Da Dokokin Amfani Da Kafafen Sada Zumunta a Najeriya

      October 16, 2025

      Hisbah Ta Kama Wasu Matasa Da Laifin Yin Aure Ba Tare Da Amincewar Iyayensu Ba

      October 13, 2025

      Tinubu Ya Bawa NAHCON Umarnin Rage Kuɗin Hajjin 2026 Cikin Gaggawa

      October 7, 2025
    • Nishadi

      Oculus Founder Makes a VR Headset That Can Literally Kill You

      January 13, 2021
      85

      Braun Series 7 Electric Shaver Review: Quality at a Good Price

      January 13, 2021
      85

      Google Pixel 7, iPhone 14 Compared: Check Out 5 Major Differences

      January 13, 2021

      Why Apple Should Skip The MacBook Pro Launch

      January 12, 2021

      Apollo G2J Showcases Electric Sports Car

      January 12, 2021
    • Tsaro

      Sojojin Najeriya Sun Ƙwato lita 290,000 Na Man Fetur a Yankin Neja Delta

      October 21, 2025

      Ƴan Bindiga Sun Ƙwace Wayoyin Ƴan Sanda a Zamfara

      October 2, 2025

      Gwamnan Kano Ya Buƙaci Tinubu Ya Tsige Kwamishinan Ƴan Sandan Jihar

      October 1, 2025

      Will Using a VPN on Phone Helps Protect You from Ransomware?

      January 14, 2021

      Popular New Xbox Game Pass Game Being Review Bombed With “0s”

      January 14, 2021
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    Home » Gwamnatin Tarayya Ta Cire Darasin Lissafi Cikin Sharaɗin Shiga Jami’a Ga Wasu Ɗalibai
    Featured

    Gwamnatin Tarayya Ta Cire Darasin Lissafi Cikin Sharaɗin Shiga Jami’a Ga Wasu Ɗalibai

    Abbass AbdurrahmanBy Abbass AbdurrahmanOctober 15, 2025No Comments2 Mins Read

    Gwamnatin Tarayya ta sanar da cewa daliban manyan makarantun sakandare da ke bin bangaren fasaha da al’adun gargajiya (arts & humanities) ba lallai ne su sami sakamako na “credit” a Mathematics ba kafin su samu gurbin shiga jami’a ko kwalejojin kimiyya a Najeriya. Wannan mataki, kamar yadda Ma’aikatar Ilimi ta bayyana a cikin wata sanarwa da mai magana da yawunta, Folasade Boriowo, ta fitar, na cikin sabbin ka’idojin shigar dalibai makarantu na gaba da sakandare da aka sabunta.

    A cewar sabbin ka’idojin, daliban jami’a za su bukaci akalla “credit” biyar cikin darussa masu dacewa da fannin da za su karanta, ciki har da Turanci, amma Mathematics za ta kasance wajibi ne kawai ga bangarorin kimiyya, fasaha da zamantakewa. A matakin polytechnic kuma, daliban fannin kimiyya ne kawai za a bukaci su samu Mathematics yayin da sauran fannonin za su bukaci Turanci kawai. Haka zalika, a matakin HND da NCE akwai bambance-bambance bisa nau’in shirin karatu.

    Ministan Ilimi, Dr. Tunji Alausa, ya bayyana cewa wannan sauyi na nufin rage shingayen da ke hana dalibai shiga jami’a da fadada damar samun ilimi a matakin gaba da sakandare. Ya ce gwamnati ta amince da cikakken sauye-sauyen tsarin shigar dalibai domin kara yawan wadanda ake karɓa daga kusan 700,000 a kowace shekara zuwa sama da miliyan daya.

    Gwamnati ta ce sabon tsarin zai ba da damar karin dalibai kimanin 250,000 zuwa 300,000 a kowace shekara su sami gurbin karatu a jami’o’i, polytechnics, da kwalejojin ilimi a fadin kasar. Wannan sauyi ya biyo bayan dogon lokaci na takura da ya hana dubban dalibai masu cancanta damar ci gaba da karatu saboda shingayen samun Mathematics.

    Gwamnatin Tarayya
    Share. Facebook Twitter WhatsApp Telegram
    Previous ArticleGwamnan Bayelsa Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP
    Next Article ‘Yan Sanda Sun Cafke Dillalan Miyagun Kwayoyi 105 a Jihar Jigawa
    Abbass Abdurrahman
    • Website

    Related Posts

    Featured

    Tinubu Ya Sha Alwashin Murƙushe Ta’addanci a Najeriya

    November 6, 2025
    Featured

    Hukumar Kiyaye Afkuwar Haɗura Ta Ƙasa Ta Kama Direbobi 27,000 a Abuja

    November 6, 2025
    Featured

    Gidaje 20 Da Ake Zargina a Kansu Ba Nawa Bane Ne Waɗanda Mahaifinmu Ya Bar Mana Gado Ne – Abba Kyari

    November 6, 2025
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    SABBIN LABARAI

    Gwamnatin Kano Ta Dakatar da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi

    October 1, 202535 Views

    Kotu Ta Yankewa Tsohon Firayim Ministan Mali Hukuncin Zaman Gidan Yari Sakamakon Rubutu a Shafin Sada Zumunta

    October 27, 202533 Views

    Dantawaye Ya Zama Sabon Kwamishinan Ƴansanda a Abuja

    October 17, 202526 Views

    Zama a Banɗaki Fiye Da Kima Kan Haifar Da Matsala Ga Lafiyar Ɗan Adam – Likita

    October 28, 202520 Views

    Kotu Ta Bayar Da Belin Sowore

    October 24, 202519 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    • Telegram
    © 2025 Bechi Hausa News. Developed by: ENGRMKS & CO.
    • Shafin Farko
    • Game da Mu
    • Ƙarin Bayani
    • Manufar Sirri
    • Ka’idoji da Sharudda
    • Tuntuɓe Mu

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.