Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    • Shafin Farko
    • Labarai

      Gwamnatin Kano Ta Shiryawa Ƴan Jaridar Yanar Gizo Horo Na Yini Biyu a Jigawa

      January 15, 2026

      Tanka Ta Murƙushe Mutane 5 a Gombe

      January 12, 2026

      Babu Siyasa a Binciken Da Ake Yi Wa Malami – EFCC

      January 12, 2026

      Ƴan Bindiga Sun Kashe Soja Da Jam’in NSCDC a Benue

      January 12, 2026

      Manyan Jiga-jigan APC 3 a Kogi Sun Mutu

      January 12, 2026
    • Siyasa

      Manyan Jiga-jigan APC 3 a Kogi Sun Mutu

      January 12, 2026

      Ganduje Zai Gana Da Masu Ruwa-da-tsaki Na APC

      January 11, 2026

      Datti Baba-Ahmed Ya Musanta Batun Tsayawa Takarar Shugaban Ƙasa

      January 9, 2026

      Fubara Barazana Ne Ga Demokaraɗiyya – Kakakin Majalisar Rivers

      January 9, 2026

      Kotu Ta Ƙi Bayar da Belin Kwamishinan Kuɗi Na Bauchi

      January 6, 2026
    • Addini

      Kano: Hisbah Ta Karɓi Ƙorafe-Ƙorafe Sama da 12,000 a 2025

      January 2, 2026

      Da Ɗumi-ɗumi : Sheikh Dahiru Bauchi Ya rasu

      November 27, 2025

      Zakaran Gwajin Dafi : Hajji 2025 Karkashin Farfesa Saleh Pakistan  

      November 24, 2025

      Hajji Da Shugabanci Nagari Ƙarƙashin Jagorancin Farfesa Pakistan

      November 17, 2025

      Hukumar NAHCON Ta Sanar Da Rage Kudin Aikin Hajjin 2026

      November 10, 2025
    • Nishadi

      Oculus Founder Makes a VR Headset That Can Literally Kill You

      January 13, 2021
      85

      Braun Series 7 Electric Shaver Review: Quality at a Good Price

      January 13, 2021
      85

      Google Pixel 7, iPhone 14 Compared: Check Out 5 Major Differences

      January 13, 2021

      Why Apple Should Skip The MacBook Pro Launch

      January 12, 2021

      Apollo G2J Showcases Electric Sports Car

      January 12, 2021
    • Tsaro

      Sojojin Najeriya Sun Ƙwato lita 290,000 Na Man Fetur a Yankin Neja Delta

      October 21, 2025

      Ƴan Bindiga Sun Ƙwace Wayoyin Ƴan Sanda a Zamfara

      October 2, 2025

      Gwamnan Kano Ya Buƙaci Tinubu Ya Tsige Kwamishinan Ƴan Sandan Jihar

      October 1, 2025

      Will Using a VPN on Phone Helps Protect You from Ransomware?

      January 14, 2021

      Popular New Xbox Game Pass Game Being Review Bombed With “0s”

      January 14, 2021
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    Home » Halin Da Najeriya Ke Ciki Na Taɓarɓarewar Tsaro Yana Matuƙar Damuna – Tinubu
    Featured

    Halin Da Najeriya Ke Ciki Na Taɓarɓarewar Tsaro Yana Matuƙar Damuna – Tinubu

    Abbass AbdurrahmanBy Abbass AbdurrahmanNovember 22, 2025No Comments2 Mins Read

    Shugaban Najeriya, Bola Ahmad Tinubu, ya bayyana cewa matsalar tsaro ce babbar damuwarsa a halin yanzu, musamman a Arewacin ƙasar. Ya ce dole ne a ɗauki matakan gaggawa domin dawo da zaman lafiya, gina amana da haɗin kai tsakanin al’umma. Tinubu, wanda Kakakin Majalisar Wakilai Tajudeen Abbas ya wakilta, ya yi wannan jawabi ne a bikin cika shekaru 25 da kafuwar Arewa Consultative Forum (ACF) tare da kaddamar da Asusun tallafawa ayyukanta.

    A cewar shugaban, gwamnati ta gada matsalolin tsaro masu rikitarwa, amma tana kokarin magance su da gaggawa da zuciya ɗaya. Ya ce ba za a samu cigaban tattalin arziki da ilimi ba muddin ta’addanci da fashi da makami ba su ƙare ba. Tinubu ya kuma nuna kyakkyawar fatan cewa Arewacin Najeriya zai koma matsayinsa na ƙarfi, yana mai ambaton yiwuwar fitar da man fetur daga gonakin mai na Kolmani da sauran yankuna. Shugaban ya ce dole Arewa ta faɗi gaskiya ba tare da jin tsoro ba domin kare al’umma masu rauni.

    Ya kuma bayyana muhimmancin manyan ayyukan gine-ginen da ake ƙoƙarin kammalawa, ciki har da titin Abuja–Kaduna–Kano, yana mai nanata cewa shugabannin yankin za su ci amanar al’umma idan suka yi shiru yayin da talakawa ke fama da yunwa da tsoro. Tinubu ya yabawa ACF bisa rawar da ta taka na tsawon shekaru 25 wajen kare mutunci, gaskiya da adalci ga al’ummar Arewa, yana mai cewa wannan jubili na musamman tamkar bikin ƙarfin hali da jajircewa ne.

    Shugaban ya bukaci shugabanni daga kowane mataki su sake sabunta alkawarin bin akidu masu kyau da suka kafa ACF, domin dorewar zaman lafiya da cigaban Arewa wanda shi ne ginshiƙin zaman lafiyar Najeriya gaba ɗaya.

    Tinubu
    Share. Facebook Twitter WhatsApp Telegram
    Previous ArticleGwamnatin Tarayya Ta Ƙaryata Jita-jitar Rufe Makarantu a Fadin Kasar
    Next Article Gwamnatin Neja Ta Sanar Da Rufe Makaranta a Faɗin Jihar
    Abbass Abdurrahman
    • Website

    Related Posts

    Featured

    Gwamnatin Kano Ta Shiryawa Ƴan Jaridar Yanar Gizo Horo Na Yini Biyu a Jigawa

    January 15, 2026
    Featured

    Tanka Ta Murƙushe Mutane 5 a Gombe

    January 12, 2026
    Featured

    Babu Siyasa a Binciken Da Ake Yi Wa Malami – EFCC

    January 12, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    SABBIN LABARAI

    Gwamnatin Kano Ta Dakatar da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi

    October 1, 202542 Views

    Kotu Ta Yankewa Tsohon Firayim Ministan Mali Hukuncin Zaman Gidan Yari Sakamakon Rubutu a Shafin Sada Zumunta

    October 27, 202541 Views

    Dantawaye Ya Zama Sabon Kwamishinan Ƴansanda a Abuja

    October 17, 202532 Views

    An Gano Motar Ofishin Mataimakin Gwamna Da Aka Sace

    November 12, 202527 Views

    NAFDAC Ta Yi Gargaɗi Kan Wani Kororon Roba Me Matuƙar Haɗari Ga Lafiya

    December 30, 202525 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    • Telegram
    © 2026 Bechi Hausa News. Developed by: ENGRMKS & CO.
    • Shafin Farko
    • Game da Mu
    • Ƙarin Bayani
    • Manufar Sirri
    • Ka’idoji da Sharudda
    • Tuntuɓe Mu

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.