Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    • Shafin Farko
    • Labarai

      Gwamnatin Kano Ta Shiryawa Ƴan Jaridar Yanar Gizo Horo Na Yini Biyu a Jigawa

      January 15, 2026

      Tanka Ta Murƙushe Mutane 5 a Gombe

      January 12, 2026

      Babu Siyasa a Binciken Da Ake Yi Wa Malami – EFCC

      January 12, 2026

      Ƴan Bindiga Sun Kashe Soja Da Jam’in NSCDC a Benue

      January 12, 2026

      Manyan Jiga-jigan APC 3 a Kogi Sun Mutu

      January 12, 2026
    • Siyasa

      Manyan Jiga-jigan APC 3 a Kogi Sun Mutu

      January 12, 2026

      Ganduje Zai Gana Da Masu Ruwa-da-tsaki Na APC

      January 11, 2026

      Datti Baba-Ahmed Ya Musanta Batun Tsayawa Takarar Shugaban Ƙasa

      January 9, 2026

      Fubara Barazana Ne Ga Demokaraɗiyya – Kakakin Majalisar Rivers

      January 9, 2026

      Kotu Ta Ƙi Bayar da Belin Kwamishinan Kuɗi Na Bauchi

      January 6, 2026
    • Addini

      Kano: Hisbah Ta Karɓi Ƙorafe-Ƙorafe Sama da 12,000 a 2025

      January 2, 2026

      Da Ɗumi-ɗumi : Sheikh Dahiru Bauchi Ya rasu

      November 27, 2025

      Zakaran Gwajin Dafi : Hajji 2025 Karkashin Farfesa Saleh Pakistan  

      November 24, 2025

      Hajji Da Shugabanci Nagari Ƙarƙashin Jagorancin Farfesa Pakistan

      November 17, 2025

      Hukumar NAHCON Ta Sanar Da Rage Kudin Aikin Hajjin 2026

      November 10, 2025
    • Nishadi

      Oculus Founder Makes a VR Headset That Can Literally Kill You

      January 13, 2021
      85

      Braun Series 7 Electric Shaver Review: Quality at a Good Price

      January 13, 2021
      85

      Google Pixel 7, iPhone 14 Compared: Check Out 5 Major Differences

      January 13, 2021

      Why Apple Should Skip The MacBook Pro Launch

      January 12, 2021

      Apollo G2J Showcases Electric Sports Car

      January 12, 2021
    • Tsaro

      Sojojin Najeriya Sun Ƙwato lita 290,000 Na Man Fetur a Yankin Neja Delta

      October 21, 2025

      Ƴan Bindiga Sun Ƙwace Wayoyin Ƴan Sanda a Zamfara

      October 2, 2025

      Gwamnan Kano Ya Buƙaci Tinubu Ya Tsige Kwamishinan Ƴan Sandan Jihar

      October 1, 2025

      Will Using a VPN on Phone Helps Protect You from Ransomware?

      January 14, 2021

      Popular New Xbox Game Pass Game Being Review Bombed With “0s”

      January 14, 2021
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    Home » Har Yanzu Bamu Janye Dakatarwar Shekaru 30 Da Mu Ka Yi Wa El-Rufai Ba – SDP
    Featured

    Har Yanzu Bamu Janye Dakatarwar Shekaru 30 Da Mu Ka Yi Wa El-Rufai Ba – SDP

    Abbass AbdurrahmanBy Abbass AbdurrahmanNovember 2, 2025No Comments2 Mins Read

    Ƙungiyar shugabannin jam’iyyar Social Democratic Party (SDP) na jihohi 37 ta sake jaddada cewa tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Mallam Nasir El-Rufai, yana nan a karkashin haramcin shekaru 30 daga shiga jam’iyyar. Wannan sanarwa ta fito ne bayan jita-jitar cewa El-Rufai na shirin komawa cikin jam’iyyar kafin babban taron kasa mai zuwa. Shugaban ƙungiyar, Femi Olaniyi, ya bayyana a wani taron manema labarai a Abuja cewa hukuncin da kwamitin gudanarwa na ƙasa ya yanke kan El-Rufai ba zai canza ba, yana mai cewa an kore shi bisa ka’ida kuma har yanzu ana kan wannan hukunci.

    Olaniyi ya ce El-Rufai ya shiga jam’iyyar ne ta “ƙofa ta baya,” ba bisa tsarin jam’iyyar ba. Ya tunatar da cewa tun a watan Afrilu 2025 an bayyana cewa duk wanda yake son shiga SDP dole ne ya bi matakin gunduma da jiha kafin ya zama ɗan jam’iyya na gaskiya. A cewarsa, abin da El-Rufai ya aikata a cikin tsarin jam’iyyar ya saba wa dokokin cikin gida, kuma an tabbatar da hukuncin korarsa da cikakken goyon bayan shugabannin jihohi.

    Rahotanni sun nuna cewa wannan rikicin ya raba jam’iyyar SDP gida biyu, inda bangaren shugabannin jihohi ke kiran a “yi wa jam’iyyar tiyata” domin cire abin da suka kira “cutar Gabamism” — wato bangaren da ke goyon bayan tsohon shugaban jam’iyyar na ƙasa, Shehu Gabam, wanda shi ma aka dakatar. Bangaren Gabam kuwa ya dage cewa dakatarwar ba a bisa ƙa’ida take ba, abin da ke nuna cewa rikicin zai iya kaiwa kotu.

    Tsohon gwamnan, wanda bai yi tsokaci kan lamarin ba har zuwa lokacin da aka wallafa rahoton, an zarge shi da amfani da takardun bogi, da kuma ƙoƙarin karkatar da tsarin jam’iyyar ta hanyoyi da ba su da izini. Hukumar gudanarwa ta jam’iyyar ta bayyana cewa El-Rufai ba zai iya shiga ko hulɗa da SDP ba har tsawon shekaru 30 masu zuwa.

    El - Rufai SDP
    Share. Facebook Twitter WhatsApp Telegram
    Previous ArticleBankin Duniya Na Duba Yiwuwar Bawa Najeriya Rancen Dala Biliyan Ɗaya
    Next Article Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 17 a Kaduna da Filato
    Abbass Abdurrahman
    • Website

    Related Posts

    Featured

    Gwamnatin Kano Ta Shiryawa Ƴan Jaridar Yanar Gizo Horo Na Yini Biyu a Jigawa

    January 15, 2026
    Featured

    Tanka Ta Murƙushe Mutane 5 a Gombe

    January 12, 2026
    Featured

    Babu Siyasa a Binciken Da Ake Yi Wa Malami – EFCC

    January 12, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    SABBIN LABARAI

    Gwamnatin Kano Ta Dakatar da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi

    October 1, 202542 Views

    Kotu Ta Yankewa Tsohon Firayim Ministan Mali Hukuncin Zaman Gidan Yari Sakamakon Rubutu a Shafin Sada Zumunta

    October 27, 202541 Views

    Dantawaye Ya Zama Sabon Kwamishinan Ƴansanda a Abuja

    October 17, 202532 Views

    An Gano Motar Ofishin Mataimakin Gwamna Da Aka Sace

    November 12, 202527 Views

    NAFDAC Ta Yi Gargaɗi Kan Wani Kororon Roba Me Matuƙar Haɗari Ga Lafiya

    December 30, 202525 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    • Telegram
    © 2026 Bechi Hausa News. Developed by: ENGRMKS & CO.
    • Shafin Farko
    • Game da Mu
    • Ƙarin Bayani
    • Manufar Sirri
    • Ka’idoji da Sharudda
    • Tuntuɓe Mu

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.