Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    • Shafin Farko
    • Labarai

      Gwamnatin Kano Ta Shiryawa Ƴan Jaridar Yanar Gizo Horo Na Yini Biyu a Jigawa

      January 15, 2026

      Tanka Ta Murƙushe Mutane 5 a Gombe

      January 12, 2026

      Babu Siyasa a Binciken Da Ake Yi Wa Malami – EFCC

      January 12, 2026

      Ƴan Bindiga Sun Kashe Soja Da Jam’in NSCDC a Benue

      January 12, 2026

      Manyan Jiga-jigan APC 3 a Kogi Sun Mutu

      January 12, 2026
    • Siyasa

      Manyan Jiga-jigan APC 3 a Kogi Sun Mutu

      January 12, 2026

      Ganduje Zai Gana Da Masu Ruwa-da-tsaki Na APC

      January 11, 2026

      Datti Baba-Ahmed Ya Musanta Batun Tsayawa Takarar Shugaban Ƙasa

      January 9, 2026

      Fubara Barazana Ne Ga Demokaraɗiyya – Kakakin Majalisar Rivers

      January 9, 2026

      Kotu Ta Ƙi Bayar da Belin Kwamishinan Kuɗi Na Bauchi

      January 6, 2026
    • Addini

      Kano: Hisbah Ta Karɓi Ƙorafe-Ƙorafe Sama da 12,000 a 2025

      January 2, 2026

      Da Ɗumi-ɗumi : Sheikh Dahiru Bauchi Ya rasu

      November 27, 2025

      Zakaran Gwajin Dafi : Hajji 2025 Karkashin Farfesa Saleh Pakistan  

      November 24, 2025

      Hajji Da Shugabanci Nagari Ƙarƙashin Jagorancin Farfesa Pakistan

      November 17, 2025

      Hukumar NAHCON Ta Sanar Da Rage Kudin Aikin Hajjin 2026

      November 10, 2025
    • Nishadi

      Oculus Founder Makes a VR Headset That Can Literally Kill You

      January 13, 2021
      85

      Braun Series 7 Electric Shaver Review: Quality at a Good Price

      January 13, 2021
      85

      Google Pixel 7, iPhone 14 Compared: Check Out 5 Major Differences

      January 13, 2021

      Why Apple Should Skip The MacBook Pro Launch

      January 12, 2021

      Apollo G2J Showcases Electric Sports Car

      January 12, 2021
    • Tsaro

      Sojojin Najeriya Sun Ƙwato lita 290,000 Na Man Fetur a Yankin Neja Delta

      October 21, 2025

      Ƴan Bindiga Sun Ƙwace Wayoyin Ƴan Sanda a Zamfara

      October 2, 2025

      Gwamnan Kano Ya Buƙaci Tinubu Ya Tsige Kwamishinan Ƴan Sandan Jihar

      October 1, 2025

      Will Using a VPN on Phone Helps Protect You from Ransomware?

      January 14, 2021

      Popular New Xbox Game Pass Game Being Review Bombed With “0s”

      January 14, 2021
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    Home » Mun Fara Shirye-shiryen Kai Hari Najeriya – Amurka
    Featured

    Mun Fara Shirye-shiryen Kai Hari Najeriya – Amurka

    Abbass AbdurrahmanBy Abbass AbdurrahmanNovember 2, 2025Updated:November 2, 2025No Comments2 Mins Read

    Sakataren Yaƙin Amurka, Pete Hegseth, ya bayyana cewa ma’aikatarsa tana shirin kai hari a Najeriya, sakamakon zarge-zargen kisan Kiristoci da ake cewa na ƙaruwa a ƙasar. Hegseth ya fadi haka ne bayan shugaban Amurka, Donald Trump, ya wallafa a Truth Social cewa gwamnatin Najeriya “na rufe ido” kan hare-haren da ake kaiwa Kiristoci, yana mai gargadi cewa Amurka na iya katse tallafi da kuma kaddamar da farmaki kan kungiyoyin ta’addanci a Najeriya.

    Trump ya ce idan gwamnati ta gaza kare Kiristoci, Amurka za ta “tsinke duk wata taimako ga Najeriya” kuma tana iya shiga ƙasar “da makamai a bude” domin kawar da ‘yan ta’adda. Ya kuma umarci Ma’aikatar Yaƙi ta fara shirin kai farmaki, yana mai cewa, “idan muka kai hari, zai kasance da sauri, da ƙarfi, kuma da daɗi — kamar yadda ‘yan ta’addan ke kai wa Kiristoci hari.”

    A martanin da Hegseth ya wallafa a dandalin X (Twitter), ya tabbatar da cewa sun fara shiri bisa umarnin shugaban ƙasarsu. Ya ce, “Gobarar kashe Kiristoci ba za ta ci gaba ba. Idan gwamnatin Najeriya ba ta kare su ba, mu ne za mu kare su ta hanyar kawar da ‘yan ta’addan da ke aikata waɗannan manyan laifuka.” Wannan ya nuna yiwuwar Amurka ta ɗauki matakin soja kai tsaye idan halin da ake ciki bai sauya ba.

    Wannan lamari ya faru ne kwana guda bayan Trump ya sake sanya Najeriya cikin jerin ƙasashen da ke da “tsananin take hakkin addini,” yana zargin cewa ana kashe Kiristoci da yawa a hannun kungiyoyin masu tsattsauran ra’ayi. Sai dai shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya mayar da martani cikin ƙarfi, yana cewa Najeriya ƙasa ce mai dimokuraɗiyya da ke ba kowa ‘yancin addini, kuma gwamnatin sa ba za ta yarda wani ya bata sunan ƙasar da ƙarya ba.

    Amurka
    Share. Facebook Twitter WhatsApp Telegram
    Previous ArticleKotu Ta Yankewa Wani Malami Hukuncin Ɗaurin Rai da Rai a Abuja
    Next Article Bankin Duniya Na Duba Yiwuwar Bawa Najeriya Rancen Dala Biliyan Ɗaya
    Abbass Abdurrahman
    • Website

    Related Posts

    Featured

    Gwamnatin Kano Ta Shiryawa Ƴan Jaridar Yanar Gizo Horo Na Yini Biyu a Jigawa

    January 15, 2026
    Featured

    Tanka Ta Murƙushe Mutane 5 a Gombe

    January 12, 2026
    Featured

    Babu Siyasa a Binciken Da Ake Yi Wa Malami – EFCC

    January 12, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    SABBIN LABARAI

    Gwamnatin Kano Ta Dakatar da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi

    October 1, 202542 Views

    Kotu Ta Yankewa Tsohon Firayim Ministan Mali Hukuncin Zaman Gidan Yari Sakamakon Rubutu a Shafin Sada Zumunta

    October 27, 202541 Views

    Dantawaye Ya Zama Sabon Kwamishinan Ƴansanda a Abuja

    October 17, 202532 Views

    An Gano Motar Ofishin Mataimakin Gwamna Da Aka Sace

    November 12, 202527 Views

    NAFDAC Ta Yi Gargaɗi Kan Wani Kororon Roba Me Matuƙar Haɗari Ga Lafiya

    December 30, 202525 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    • Telegram
    © 2026 Bechi Hausa News. Developed by: ENGRMKS & CO.
    • Shafin Farko
    • Game da Mu
    • Ƙarin Bayani
    • Manufar Sirri
    • Ka’idoji da Sharudda
    • Tuntuɓe Mu

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.