Wata mummunar gobara ta tashi a Kasuwar Singer da ke Kano, inda ta lalata dukiyoyi da darajarsu ta haura naira biliyan 5, tare da shafar fiye da ‘yan kasuwa 1,000, yayin da aka bayyana cewa mutum bakwai sun bace. Shugaban kasuwar, Alhaji Junaid Zakari, ne ya bayyana haka a ranar Lahadi, 15 ga Fabrairu, 2026, yana mai cewa wannan na daga cikin manyan masifun da kasuwar ta taba fuskanta.
Ya ce gobarar ta kone gine-ginen zama guda hudu da ake hada kasuwanci a cikinsu, inda kayayyaki, kayan aiki da duk wasu kadarori suka lalace gaba daya, lamarin da ya jefa daruruwan iyalai cikin mawuyacin hali. Ya kara da cewa ana ci gaba da bincike domin gano inda mutanen da suka bace suke, ko suna raye ko kuwa sun mutu.
Rahotanni sun nuna cewa jami’an agajin gaggawa da hukumomin tsaro na kokarin gano musabbabin gobarar, yayin da ‘yan kasuwar da abin ya shafa ke kokarin ceto ragowar kayayyakinsu. Wasu ‘yan kasuwa sun bayyana cewa sun yi asarar dukiyoyi masu yawa, inda wani mai shago, Alhaji Isa Abubakar, ya ce shi kadai ya yi asarar kayayyakin da suka kai naira miliyan 200. Wannan lamari na kara jefa al’ummar Kano cikin jimami, kamar yadda majiyar News Agency of Nigeria ta rawaito.
Shugaban kasuwar ya yaba da matakin da gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya dauka na kai ziyara wurin da gobarar ta tashi yayin da take ci gaba, yana mai cewa hakan ya nuna kulawa da goyon bayan gwamnati ga ‘yan kasuwar da abin ya shafa. Hukumomi dai na ci gaba da bincike domin gano hakikanin abin da ya haddasa gobarar.

