Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    • Shafin Farko
    • Labarai

      Ba Za Mu Bayar da Tabbacin Sahihin Zaɓe a 2027 Ba – Amupitan

      March 2, 2026

      Jirage Marasa Matuƙa Sun Kai Hari Matatar Man Saudiyya

      March 2, 2026

      Najeriya Ta Buƙaci a Kawo Karshen Rikicin Gabas ta Tsakiya

      March 2, 2026

      Iran Ta Naɗa Ayatollah Arafi A Matsayin Jagoran Addini Na Riƙo

      March 1, 2026

      Majalisar Dattawa Ta Sha Alwashin Amincewa da Dokar Kafa ‘Yan Sandan Jihohi Kafin Ƙarshen 2026

      March 1, 2026
    • Siyasa

      Gwamnan Adamawa Ya Sauya Sheƙa Zuwa APC

      February 27, 2026

      NDLEA Ta Kama Wata Mata Mai Cikin Bogi Ɗauke da Hodar Iblis a Iyakar Seme

      February 22, 2026

      Jam’iyyun Adawa Sun Kaurace wa Zaɓen Kano, APC Ta Lashe Kujerun Majalisa a Rivers

      February 22, 2026

      Kotu Ta Umarci INEC Ta Yi Wa Jam’iyyar NDP Rajista

      February 19, 2026

      Gwamnan Zamfara Ya Zargi Gwamnatin Tarayya da Nuna Masa Wariya Saboda Bambancin Jam’iyya

      February 18, 2026
    • Addini

      Bauchi Ta neman ƙarin Kujerun Hajji Daga Saudiyya

      February 16, 2026

      Sarkin Musulmi Ya Umarci Ƴan Najeriya Su Fara Duban Jinjirin Watan Ramadan Ranar Talata

      February 16, 2026

      Tinubu Ya Naɗa Ambasada Ismail Abba Yusuf a Matsayin Sabon Shugaban NAHCON

      February 11, 2026

      Sheikh Usman Kusfa Zaria (Rigi-rigi) Ya Rasu

      February 2, 2026

      Jigawa Ta Fara Gwajin Lafiya ga Maniyyatan Hajjin 2026

      January 28, 2026
    • Nishadi

      Oculus Founder Makes a VR Headset That Can Literally Kill You

      January 13, 2021
      85

      Braun Series 7 Electric Shaver Review: Quality at a Good Price

      January 13, 2021
      85

      Google Pixel 7, iPhone 14 Compared: Check Out 5 Major Differences

      January 13, 2021

      Why Apple Should Skip The MacBook Pro Launch

      January 12, 2021

      Apollo G2J Showcases Electric Sports Car

      January 12, 2021
    • Tsaro

      Ba a Fasa Bututun Mai Ko Ɗaya a Niger Delta a 2025 Ba – Sojoj

      January 20, 2026

      Sojojin Najeriya Sun Ƙwato lita 290,000 Na Man Fetur a Yankin Neja Delta

      October 21, 2025

      Ƴan Bindiga Sun Ƙwace Wayoyin Ƴan Sanda a Zamfara

      October 2, 2025

      Gwamnan Kano Ya Buƙaci Tinubu Ya Tsige Kwamishinan Ƴan Sandan Jihar

      October 1, 2025

      Will Using a VPN on Phone Helps Protect You from Ransomware?

      January 14, 2021
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    Home » Muna Allah-wadai Da Juyin Mulki a Guinea-Bissau – Najeriya
    Featured

    Muna Allah-wadai Da Juyin Mulki a Guinea-Bissau – Najeriya

    Abbass AbdurrahmanBy Abbass AbdurrahmanNovember 28, 2025No Comments2 Mins Read

    Gwamnatin Najeriya ta tabbatar da cewa tsohon shugaban ƙasa Goodluck Jonathan ya tsira kuma ya bar ƙasar Guinea-Bissau ta jirgi na musamman. Jonathan ya je ƙasar ne a matsayin jagoran tawagar West African Elders Forum domin sa ido kan zaɓen shugaban ƙasa da na ’yan majalisa. Amma sai sojojin ƙasar suka kifar da gwamnatin Umaro Sissoco Embaló, suka rufe iyakoki, tare da ɗaukar ikon mulki gaba ɗaya. Rikicin ya ɓarke ne yayin da ake jiran sakamakon zaɓen da aka gudanar ranar 23 ga Nuwamba.

    Majalisar Wakilai ta Najeriya ta tattauna batun cikin gaggawa, inda mataimakin Kakakin Majalisa Benjamin Kalu ya nemi gwamnati ta tabbatar da ceto Jonathan cikin gaggawa. Shugabannin majalisa sun yaba irin rawar da ya taka wajen sa ido kan zaɓe a ƙasashe daban-daban, tare da bukatar a yi duk mai yiwuwa wajen kare lafiyarsa. Gwamnatin tarayya ta kuma yi tir da juyin mulkin, tana mai cewa matakin babban barazana ne ga damokradiyya a yammacin Afirka. Abuja ta bukaci a gaggauta mayar da tsarin mulki da sakin duk wadanda aka kame.

    Jonathan, tare da tsohon shugaban Mozambique Filipe Nyusi da jagoran tawagar ECOWAS Issifu Kamara, sun fitar da sanarwa mai tsaurin kalamai kan juyin mulkin. Sun ce an yi yunkurin dakile tsarin zaɓe da kuma kwanciyar hankali na ƙasar. Bechi Hausa ta tattaro cewa an samu harbe-harbe a kusa da fadar shugaban ƙasa, aka kai hari ofishin Hukumar Zaɓe, yayin da sojoji suka toshe manyan hanyoyi. A halin da ake ciki, rundunar sojoji ta naɗa Janar Horta N’Tam a matsayin shugaban riƙo na shekara guda.

    Guinea-Bissau na fuskantar rikice-rikicen siyasa tun bayan samun ’yancin kai, inda aka yi nasarar juyin mulki fiye da hudu. Kungiyoyin ECOWAS da AU sun yi fatali da matakin, suna mai cewa ba za su amince da karɓar mulki ta hanyar da ta sabawa kundin tsarin mulki ba. Kasashen duniya ciki har da MDD da Portugal sun bukaci a yi hattara, tare da kare ’yancin jama’a da ’yancin manema labarai. Najeriya ta ce za ta ci gaba da aiki da abokan hulɗa domin tabbatar da dawo da zaman lafiya da tsarin mulki a Guinea-Bissau.

    Guinea-Bissau
    Share. Facebook Twitter WhatsApp Telegram
    Previous ArticleEFCC Ta Gayyaci Tsohon Ministan Shari’a Abubakar Malami
    Next Article Kamata Yayi Kuɗin Da Ake Kashewa Ƴan Majalisa a Tura Su Ɓangaren Tsaro – Ndume
    Abbass Abdurrahman
    • Website

    Related Posts

    Featured

    Ba Za Mu Bayar da Tabbacin Sahihin Zaɓe a 2027 Ba – Amupitan

    March 2, 2026
    Featured

    Jirage Marasa Matuƙa Sun Kai Hari Matatar Man Saudiyya

    March 2, 2026
    Featured

    Najeriya Ta Buƙaci a Kawo Karshen Rikicin Gabas ta Tsakiya

    March 2, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    SABBIN LABARAI

    Gwamnatin Kano Ta Dakatar da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi

    October 1, 202543 Views

    Kotu Ta Yankewa Tsohon Firayim Ministan Mali Hukuncin Zaman Gidan Yari Sakamakon Rubutu a Shafin Sada Zumunta

    October 27, 202541 Views

    Dantawaye Ya Zama Sabon Kwamishinan Ƴansanda a Abuja

    October 17, 202532 Views

    NAFDAC Ta Yi Gargaɗi Kan Wani Kororon Roba Me Matuƙar Haɗari Ga Lafiya

    December 30, 202527 Views

    An Gano Motar Ofishin Mataimakin Gwamna Da Aka Sace

    November 12, 202527 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    • Telegram
    © 2026 Bechi Hausa News. Developed by: ENGRMKS & CO.
    • Shafin Farko
    • Game da Mu
    • Ƙarin Bayani
    • Manufar Sirri
    • Ka’idoji da Sharudda
    • Tuntuɓe Mu

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.