Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    • Shafin Farko
    • Labarai

      Mutane 4 Sun Mutu a Turmutsutsun Karɓar Sadaka a Katsina

      March 2, 2026

      Ba Za Mu Bayar da Tabbacin Sahihin Zaɓe a 2027 Ba – Amupitan

      March 2, 2026

      Jirage Marasa Matuƙa Sun Kai Hari Matatar Man Saudiyya

      March 2, 2026

      Najeriya Ta Buƙaci a Kawo Karshen Rikicin Gabas ta Tsakiya

      March 2, 2026

      Iran Ta Naɗa Ayatollah Arafi A Matsayin Jagoran Addini Na Riƙo

      March 1, 2026
    • Siyasa

      Gwamnan Adamawa Ya Sauya Sheƙa Zuwa APC

      February 27, 2026

      NDLEA Ta Kama Wata Mata Mai Cikin Bogi Ɗauke da Hodar Iblis a Iyakar Seme

      February 22, 2026

      Jam’iyyun Adawa Sun Kaurace wa Zaɓen Kano, APC Ta Lashe Kujerun Majalisa a Rivers

      February 22, 2026

      Kotu Ta Umarci INEC Ta Yi Wa Jam’iyyar NDP Rajista

      February 19, 2026

      Gwamnan Zamfara Ya Zargi Gwamnatin Tarayya da Nuna Masa Wariya Saboda Bambancin Jam’iyya

      February 18, 2026
    • Addini

      Bauchi Ta neman ƙarin Kujerun Hajji Daga Saudiyya

      February 16, 2026

      Sarkin Musulmi Ya Umarci Ƴan Najeriya Su Fara Duban Jinjirin Watan Ramadan Ranar Talata

      February 16, 2026

      Tinubu Ya Naɗa Ambasada Ismail Abba Yusuf a Matsayin Sabon Shugaban NAHCON

      February 11, 2026

      Sheikh Usman Kusfa Zaria (Rigi-rigi) Ya Rasu

      February 2, 2026

      Jigawa Ta Fara Gwajin Lafiya ga Maniyyatan Hajjin 2026

      January 28, 2026
    • Nishadi

      Oculus Founder Makes a VR Headset That Can Literally Kill You

      January 13, 2021
      85

      Braun Series 7 Electric Shaver Review: Quality at a Good Price

      January 13, 2021
      85

      Google Pixel 7, iPhone 14 Compared: Check Out 5 Major Differences

      January 13, 2021

      Why Apple Should Skip The MacBook Pro Launch

      January 12, 2021

      Apollo G2J Showcases Electric Sports Car

      January 12, 2021
    • Tsaro

      Ba a Fasa Bututun Mai Ko Ɗaya a Niger Delta a 2025 Ba – Sojoj

      January 20, 2026

      Sojojin Najeriya Sun Ƙwato lita 290,000 Na Man Fetur a Yankin Neja Delta

      October 21, 2025

      Ƴan Bindiga Sun Ƙwace Wayoyin Ƴan Sanda a Zamfara

      October 2, 2025

      Gwamnan Kano Ya Buƙaci Tinubu Ya Tsige Kwamishinan Ƴan Sandan Jihar

      October 1, 2025

      Will Using a VPN on Phone Helps Protect You from Ransomware?

      January 14, 2021
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    Home » Mutane Miliyan 24 Na Fama Da Ciwon Suga a Afrika – WHO
    Featured

    Mutane Miliyan 24 Na Fama Da Ciwon Suga a Afrika – WHO

    Abbass AbdurrahmanBy Abbass AbdurrahmanNovember 11, 2025No Comments2 Mins Read

    Hukumar Lafiya ta Duniya WHO ta bayyana cewa akalla mutane miliyan 24 masu shekaru tsakanin 20 zuwa 79 suna fama da ciwon suga a nahiyar Afirka. Rahoton ya nuna cewa rabin wannan adadi, kusan miliyan 12, ba su ma san suna da cutar ba, lamarin da ke ƙara haɗarin samun nakasa, rikicewar jiki ko mutuwa kafin lokaci. WHO ta yi gargadin cewa idan ba a dauki matakin gaggawa ba, yawan masu ciwon suga zai kai miliyan 60 nan da shekara ta 2050.

    Daraktan WHO na yankin Afirka, Dr. Mohamed Janabi, ya ce wannan ƙaruwa tana da nasaba da sabuwar rayuwa ta zamani, rashin motsa jiki, yawaitar kiba, da kuma ƙarancin samun kulawa a asibitoci. Ya bayyana cewa ciwon suga kan iya lalata zuciya, koda, idanu da jijiyoyi, wanda hakan ke jefa iyalai da al’umma cikin tashin hankali da karin nauyin kashe kuɗin jinya.

    Ya ce taken bikin Ranar Ciwon Suga ta bana shi ne “Diabetes Across Life Stages” wato ciwon suga ba ya barin kowa; yara, matasa, manya da tsofaffi na iya kamuwa da shi. Don haka ya ce ana bukatar kulawa daga matakin rigakafi har zuwa gano cuta da kula da ita na tsawon rayuwa. Ya kuma tunatar da cewa kasashen Afirka sun amince su daidaita tsarin yaki da cutar tun shekarar 2024.

    Janabi ya ce WHO na tallafa wa kasashe wajen aiwatar da hanyoyin kula da marasa lafiya a matakin cibiyoyin kiwon lafiya na farko, musamman ta hanyar shirin WHO PEN da PEN-Plus da ake amfani da su a ƙasashe da dama. Ya bukaci gwamnati a nahiyar ta karfafa kasafin kudi ga cututtukan da ba sa yaduwa, da kuma haɗa yaki da ciwon suga cikin shirin lafiya na kasa domin kare rayuka da inganta lafiya baki daya.

    WHO
    Share. Facebook Twitter WhatsApp Telegram
    Previous ArticleEFCC Na Neman Tsohon Gwamnan Bayelsa Ruwa-a-Jallo
    Next Article Masu Zanga-zanga Sun Isa Majalisar Dokoki Dan Neman Tabbatar Da Ramat a Matsayin Shugaban NERC
    Abbass Abdurrahman
    • Website

    Related Posts

    Featured

    Mutane 4 Sun Mutu a Turmutsutsun Karɓar Sadaka a Katsina

    March 2, 2026
    Featured

    Ba Za Mu Bayar da Tabbacin Sahihin Zaɓe a 2027 Ba – Amupitan

    March 2, 2026
    Featured

    Jirage Marasa Matuƙa Sun Kai Hari Matatar Man Saudiyya

    March 2, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    SABBIN LABARAI

    Gwamnatin Kano Ta Dakatar da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi

    October 1, 202543 Views

    Kotu Ta Yankewa Tsohon Firayim Ministan Mali Hukuncin Zaman Gidan Yari Sakamakon Rubutu a Shafin Sada Zumunta

    October 27, 202541 Views

    Dantawaye Ya Zama Sabon Kwamishinan Ƴansanda a Abuja

    October 17, 202532 Views

    NAFDAC Ta Yi Gargaɗi Kan Wani Kororon Roba Me Matuƙar Haɗari Ga Lafiya

    December 30, 202527 Views

    An Gano Motar Ofishin Mataimakin Gwamna Da Aka Sace

    November 12, 202527 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    • Telegram
    © 2026 Bechi Hausa News. Developed by: ENGRMKS & CO.
    • Shafin Farko
    • Game da Mu
    • Ƙarin Bayani
    • Manufar Sirri
    • Ka’idoji da Sharudda
    • Tuntuɓe Mu

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.