Amurka ta turo ƙananan rundunar sojoji zuwa Najeriya, wanda shi ne karo na farko da aka samu sahihin sojojin Amurka a ƙasa tun bayan hare-haren sama da aka kai wa ’yan ta’adda a ranar Kirsimeti ta shekarar 2025. Harin ya biyo bayan umarnin Shugaba Donald Trump kan wuraren da ya bayyana a matsayin sansanonin Ƙungiyar Islamic State a Najeriya.
Rahoton Reuters ya bayyana cewa tun daga ƙarshen watan Nuwamba 2025, Amurka ke amfani da jiragen leƙen asiri daga ƙasar Ghana domin tattara bayanai kafin kai hare-haren. Haka kuma, Trump ya nuna cewa akwai yiyuwar ƙarin matakan soji daga Amurka a nan gaba idan bukatar hakan ta taso.
Shugaban rundunar sojin Amurka a Afirka, Janar Dagvin R. M. Anderson, ya ce an cimma yarjejeniya tsakanin gwamnatocin Najeriya da Amurka domin ƙarfafa haɗin gwiwa kan yaƙi da ta’addanci. Ya bayyana cewa rundunar za ta taimaka wajen ayyukan yaƙi da ƙungiyoyi irin su Boko Haram da ISWAP, kodayake ba a bayyana adadin sojojin ko cikakken rawar da za su taka ba.

