Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    • Shafin Farko
    • Labarai

      Ba Za Mu Bayar da Tabbacin Sahihin Zaɓe a 2027 Ba – Amupitan

      March 2, 2026

      Jirage Marasa Matuƙa Sun Kai Hari Matatar Man Saudiyya

      March 2, 2026

      Najeriya Ta Buƙaci a Kawo Karshen Rikicin Gabas ta Tsakiya

      March 2, 2026

      Iran Ta Naɗa Ayatollah Arafi A Matsayin Jagoran Addini Na Riƙo

      March 1, 2026

      Majalisar Dattawa Ta Sha Alwashin Amincewa da Dokar Kafa ‘Yan Sandan Jihohi Kafin Ƙarshen 2026

      March 1, 2026
    • Siyasa

      Gwamnan Adamawa Ya Sauya Sheƙa Zuwa APC

      February 27, 2026

      NDLEA Ta Kama Wata Mata Mai Cikin Bogi Ɗauke da Hodar Iblis a Iyakar Seme

      February 22, 2026

      Jam’iyyun Adawa Sun Kaurace wa Zaɓen Kano, APC Ta Lashe Kujerun Majalisa a Rivers

      February 22, 2026

      Kotu Ta Umarci INEC Ta Yi Wa Jam’iyyar NDP Rajista

      February 19, 2026

      Gwamnan Zamfara Ya Zargi Gwamnatin Tarayya da Nuna Masa Wariya Saboda Bambancin Jam’iyya

      February 18, 2026
    • Addini

      Bauchi Ta neman ƙarin Kujerun Hajji Daga Saudiyya

      February 16, 2026

      Sarkin Musulmi Ya Umarci Ƴan Najeriya Su Fara Duban Jinjirin Watan Ramadan Ranar Talata

      February 16, 2026

      Tinubu Ya Naɗa Ambasada Ismail Abba Yusuf a Matsayin Sabon Shugaban NAHCON

      February 11, 2026

      Sheikh Usman Kusfa Zaria (Rigi-rigi) Ya Rasu

      February 2, 2026

      Jigawa Ta Fara Gwajin Lafiya ga Maniyyatan Hajjin 2026

      January 28, 2026
    • Nishadi

      Oculus Founder Makes a VR Headset That Can Literally Kill You

      January 13, 2021
      85

      Braun Series 7 Electric Shaver Review: Quality at a Good Price

      January 13, 2021
      85

      Google Pixel 7, iPhone 14 Compared: Check Out 5 Major Differences

      January 13, 2021

      Why Apple Should Skip The MacBook Pro Launch

      January 12, 2021

      Apollo G2J Showcases Electric Sports Car

      January 12, 2021
    • Tsaro

      Ba a Fasa Bututun Mai Ko Ɗaya a Niger Delta a 2025 Ba – Sojoj

      January 20, 2026

      Sojojin Najeriya Sun Ƙwato lita 290,000 Na Man Fetur a Yankin Neja Delta

      October 21, 2025

      Ƴan Bindiga Sun Ƙwace Wayoyin Ƴan Sanda a Zamfara

      October 2, 2025

      Gwamnan Kano Ya Buƙaci Tinubu Ya Tsige Kwamishinan Ƴan Sandan Jihar

      October 1, 2025

      Will Using a VPN on Phone Helps Protect You from Ransomware?

      January 14, 2021
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    Home » Tsaron Da Ake Bawa Seyi Tinubu Yayi Yawa – Wole Soyinka
    Featured

    Tsaron Da Ake Bawa Seyi Tinubu Yayi Yawa – Wole Soyinka

    Abbass AbdurrahmanBy Abbass AbdurrahmanDecember 10, 2025No Comments2 Mins Read

    Fitaccen marubucin nan Farfesa Wole Soyinka ya bayyana rashin jin daɗinsa game da yadda ake amfani da jami’an tsaro wajen kare wasu manyan ‘ya’yan gwamnati, musamman Seyi Tinubu, ɗan shugaban ƙasa. Ya yi wannan jawabi ne a wajen bikin bayar da lambar yabo ta Wole Soyinka Centre for Investigative Journalism da aka gudanar a Legas.

    Soyinka ya ce abin da ya gani a wani otel da yake zaune a Ikoyi ya ba shi mamaki, inda ya hango rakiyar tsaro mai yawa da ya ce “ta isa ta kwace ƙasa”. Bayan ya bincika, sai aka tabbatar masa cewa rakiyar ta ɗan shugaban ƙasa ce. Soyinka yace hatta mai ba shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro, Nuhu Ribadu, ya nemi karin bayani kan wannan al’amari, yana mai cewa wannan dabi’a ta nuna amfani da iko fiye da kima.

    A cikin jawabin nasa, Soyinka ya jaddada cewa “’ya’yan shugabanni ba zababbun jagorori ba ne, don haka ba su da hurumin amfani da tsaron gwamnati irin na manyan jami’ai.” Ya yi ishara da cewa kasar na fama da hare-haren ‘yan bindiga, sace mutane, da rikice-rikicen karkara, don haka bai dace a tara rundunar tsaro a kan mutum ɗaya ba.

    Farfesan ya kuma yi tsokaci kan batutuwan yankin, ciki har da tsoma bakin Najeriya wajen dakile juyin mulki a Jamhuriyar Benin, yana mai cewa hakan na iya janyo barazana ga tsaron cikin gida. Ya yi suka kan rusau a Legas, yana mai cewa ko da gwamnati na yin gyare-gyaren birni, ya kamata a kula da mutuncin jama’ar da abin ya shafa. Haka kuma, ya gargadi manema labarai da su kara taka tsantsan da tantance gaskiya domin kaucewa yada bayanan karya.

    Wole Soyinka
    Share. Facebook Twitter WhatsApp Telegram
    Previous ArticleGwamnatin Enugu Ta Hana Masu Keke Napep Hawa Manyan Tituna
    Next Article EFCC Ta Kama Tsohon Minista Ƙwadago
    Abbass Abdurrahman
    • Website

    Related Posts

    Featured

    Ba Za Mu Bayar da Tabbacin Sahihin Zaɓe a 2027 Ba – Amupitan

    March 2, 2026
    Featured

    Jirage Marasa Matuƙa Sun Kai Hari Matatar Man Saudiyya

    March 2, 2026
    Featured

    Najeriya Ta Buƙaci a Kawo Karshen Rikicin Gabas ta Tsakiya

    March 2, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    SABBIN LABARAI

    Gwamnatin Kano Ta Dakatar da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi

    October 1, 202543 Views

    Kotu Ta Yankewa Tsohon Firayim Ministan Mali Hukuncin Zaman Gidan Yari Sakamakon Rubutu a Shafin Sada Zumunta

    October 27, 202541 Views

    Dantawaye Ya Zama Sabon Kwamishinan Ƴansanda a Abuja

    October 17, 202532 Views

    NAFDAC Ta Yi Gargaɗi Kan Wani Kororon Roba Me Matuƙar Haɗari Ga Lafiya

    December 30, 202527 Views

    An Gano Motar Ofishin Mataimakin Gwamna Da Aka Sace

    November 12, 202527 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    • Telegram
    © 2026 Bechi Hausa News. Developed by: ENGRMKS & CO.
    • Shafin Farko
    • Game da Mu
    • Ƙarin Bayani
    • Manufar Sirri
    • Ka’idoji da Sharudda
    • Tuntuɓe Mu

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.