Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    • Shafin Farko
    • Labarai

      Jirage Marasa Matuƙa Sun Kai Hari Matatar Man Saudiyya

      March 2, 2026

      Najeriya Ta Buƙaci a Kawo Karshen Rikicin Gabas ta Tsakiya

      March 2, 2026

      Iran Ta Naɗa Ayatollah Arafi A Matsayin Jagoran Addini Na Riƙo

      March 1, 2026

      Majalisar Dattawa Ta Sha Alwashin Amincewa da Dokar Kafa ‘Yan Sandan Jihohi Kafin Ƙarshen 2026

      March 1, 2026

      Iran Ta Ayyana Zaman Makoki na Kwanaki 40 Bayan Mutuwar Jagora Ayatoullah Khamenei 

      March 1, 2026
    • Siyasa

      Gwamnan Adamawa Ya Sauya Sheƙa Zuwa APC

      February 27, 2026

      NDLEA Ta Kama Wata Mata Mai Cikin Bogi Ɗauke da Hodar Iblis a Iyakar Seme

      February 22, 2026

      Jam’iyyun Adawa Sun Kaurace wa Zaɓen Kano, APC Ta Lashe Kujerun Majalisa a Rivers

      February 22, 2026

      Kotu Ta Umarci INEC Ta Yi Wa Jam’iyyar NDP Rajista

      February 19, 2026

      Gwamnan Zamfara Ya Zargi Gwamnatin Tarayya da Nuna Masa Wariya Saboda Bambancin Jam’iyya

      February 18, 2026
    • Addini

      Bauchi Ta neman ƙarin Kujerun Hajji Daga Saudiyya

      February 16, 2026

      Sarkin Musulmi Ya Umarci Ƴan Najeriya Su Fara Duban Jinjirin Watan Ramadan Ranar Talata

      February 16, 2026

      Tinubu Ya Naɗa Ambasada Ismail Abba Yusuf a Matsayin Sabon Shugaban NAHCON

      February 11, 2026

      Sheikh Usman Kusfa Zaria (Rigi-rigi) Ya Rasu

      February 2, 2026

      Jigawa Ta Fara Gwajin Lafiya ga Maniyyatan Hajjin 2026

      January 28, 2026
    • Nishadi

      Oculus Founder Makes a VR Headset That Can Literally Kill You

      January 13, 2021
      85

      Braun Series 7 Electric Shaver Review: Quality at a Good Price

      January 13, 2021
      85

      Google Pixel 7, iPhone 14 Compared: Check Out 5 Major Differences

      January 13, 2021

      Why Apple Should Skip The MacBook Pro Launch

      January 12, 2021

      Apollo G2J Showcases Electric Sports Car

      January 12, 2021
    • Tsaro

      Ba a Fasa Bututun Mai Ko Ɗaya a Niger Delta a 2025 Ba – Sojoj

      January 20, 2026

      Sojojin Najeriya Sun Ƙwato lita 290,000 Na Man Fetur a Yankin Neja Delta

      October 21, 2025

      Ƴan Bindiga Sun Ƙwace Wayoyin Ƴan Sanda a Zamfara

      October 2, 2025

      Gwamnan Kano Ya Buƙaci Tinubu Ya Tsige Kwamishinan Ƴan Sandan Jihar

      October 1, 2025

      Will Using a VPN on Phone Helps Protect You from Ransomware?

      January 14, 2021
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    Home » Ƴan Ta’adda Sun Yi Garkuwa Da Mata 8 a Tsanyawa
    Featured

    Ƴan Ta’adda Sun Yi Garkuwa Da Mata 8 a Tsanyawa

    Abbass AbdurrahmanBy Abbass AbdurrahmanNovember 25, 2025No Comments2 Mins Read

    An cika da fargaba a daren Litinin 25 ga Nuwamba 2025, tsakanin ƙarfe 11 na dare zuwa 12 na tsakar dare, lokacin da ‘yan bindiga suka afka ƙauyen Biresawa da ke ƙaramar hukumar Tsanyawa a jihar Kano suka kuma yi garkuwa da mutane akalla takwas. Maza biyu da mata shida ne aka tabbatar da sacewa, inda al’ummar yankin suka ce ba a samu labarin inda aka tafi da su ba har yanzu. Shaidu sun bayyana cewa maharan sun shigo ƙauyen ne a ƙafa, dauke da bindigogi, tare da yin barazana ga mazauna wurin.

    Wasu mazauna sun ce an shaida motsin barayin tun kafin kai farmakin, inda aka sanar da jami’an tsaro amma ba a samu dakatar da su ba. A Yankibi, Sarmawa da Gano – dukkansu a cikin Tsanyawa – maharan da ake kiyasta fiye da 50, dauke da babura, sun yi harbe-harbe tare da sace mutane fiye da goma, yawanci mata. Kakakin al’umma, Kabiru Usman, ya ce matarsa, diyarsa mai shekara 17, da matan ‘yan uwansa na cikin wadanda aka tafi da su.

    Rahotanni sun nuna cewa mazauna yankin da jami’an sa-kai sun yi ƙoƙarin bin sawun maharan, amma suka gaza gano inda suka nufa bayan sun tsallaka zuwa jihar Katsina. Yayin da hare-haren baya-bayan nan ke ci gaba a Shanono da Bagwai, al’ummomi da dama na tserewa gidajensu, wasu na kwana a jeji ko ƙauyuka daban don gujewa kama su da daddare. Wasu mazauna sun bayyana cewa tsoro da damuwa sun yi katutu, musamman ma saboda hare-haren da suka saba a yankin da suka hada da sace mata biyar a Yan Kwada makonni kadan da suka gabata.

    Yayin da ake ci gaba da neman bayani, Kakakin Rundunar ‘Yan Sandan Kano, SP Abdullahi Kiyawa, bai amsa kiran manema labarai ba har zuwa lokacin kammala rahoton. Al’ummar yankin na roƙon gwamnati da hukumomin tsaro da su ɗauki matakai na gaggawa don kare rayuka da dukiyoyi, tare da dawo da mutanen da aka sace cikin gaggawa.

    Tsanyawa
    Share. Facebook Twitter WhatsApp Telegram
    Previous ArticleGanduje Zai Kafa Hukumar Hisbah Mai Zaman Kanta a Kano
    Next Article Da Ɗumi-ɗumi : An Ceto Ɗalibai Mata 24 Da Aka Sace a Kebbi
    Abbass Abdurrahman
    • Website

    Related Posts

    Featured

    Jirage Marasa Matuƙa Sun Kai Hari Matatar Man Saudiyya

    March 2, 2026
    Featured

    Najeriya Ta Buƙaci a Kawo Karshen Rikicin Gabas ta Tsakiya

    March 2, 2026
    Featured

    Iran Ta Naɗa Ayatollah Arafi A Matsayin Jagoran Addini Na Riƙo

    March 1, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    SABBIN LABARAI

    Gwamnatin Kano Ta Dakatar da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi

    October 1, 202543 Views

    Kotu Ta Yankewa Tsohon Firayim Ministan Mali Hukuncin Zaman Gidan Yari Sakamakon Rubutu a Shafin Sada Zumunta

    October 27, 202541 Views

    Dantawaye Ya Zama Sabon Kwamishinan Ƴansanda a Abuja

    October 17, 202532 Views

    NAFDAC Ta Yi Gargaɗi Kan Wani Kororon Roba Me Matuƙar Haɗari Ga Lafiya

    December 30, 202527 Views

    An Gano Motar Ofishin Mataimakin Gwamna Da Aka Sace

    November 12, 202527 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    • Telegram
    © 2026 Bechi Hausa News. Developed by: ENGRMKS & CO.
    • Shafin Farko
    • Game da Mu
    • Ƙarin Bayani
    • Manufar Sirri
    • Ka’idoji da Sharudda
    • Tuntuɓe Mu

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.