Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    • Shafin Farko
    • Labarai

      Iran Ta Naɗa Ayatollah Arafi A Matsayin Jagoran Addini Na Riƙo

      March 1, 2026

      Majalisar Dattawa Ta Sha Alwashin Amincewa da Dokar Kafa ‘Yan Sandan Jihohi Kafin Ƙarshen 2026

      March 1, 2026

      Iran Ta Ayyana Zaman Makoki na Kwanaki 40 Bayan Mutuwar Jagora Ayatoullah Khamenei 

      March 1, 2026

      Mutum 40 Sun Mutu a Harin da Aka Kai Makarantar Ƴanmata a Iran

      February 28, 2026

      Iran Ta Sha Alwashin Kare Kanta Daga Hare-haren Amurka da Isra’ila

      February 28, 2026
    • Siyasa

      Gwamnan Adamawa Ya Sauya Sheƙa Zuwa APC

      February 27, 2026

      NDLEA Ta Kama Wata Mata Mai Cikin Bogi Ɗauke da Hodar Iblis a Iyakar Seme

      February 22, 2026

      Jam’iyyun Adawa Sun Kaurace wa Zaɓen Kano, APC Ta Lashe Kujerun Majalisa a Rivers

      February 22, 2026

      Kotu Ta Umarci INEC Ta Yi Wa Jam’iyyar NDP Rajista

      February 19, 2026

      Gwamnan Zamfara Ya Zargi Gwamnatin Tarayya da Nuna Masa Wariya Saboda Bambancin Jam’iyya

      February 18, 2026
    • Addini

      Bauchi Ta neman ƙarin Kujerun Hajji Daga Saudiyya

      February 16, 2026

      Sarkin Musulmi Ya Umarci Ƴan Najeriya Su Fara Duban Jinjirin Watan Ramadan Ranar Talata

      February 16, 2026

      Tinubu Ya Naɗa Ambasada Ismail Abba Yusuf a Matsayin Sabon Shugaban NAHCON

      February 11, 2026

      Sheikh Usman Kusfa Zaria (Rigi-rigi) Ya Rasu

      February 2, 2026

      Jigawa Ta Fara Gwajin Lafiya ga Maniyyatan Hajjin 2026

      January 28, 2026
    • Nishadi

      Oculus Founder Makes a VR Headset That Can Literally Kill You

      January 13, 2021
      85

      Braun Series 7 Electric Shaver Review: Quality at a Good Price

      January 13, 2021
      85

      Google Pixel 7, iPhone 14 Compared: Check Out 5 Major Differences

      January 13, 2021

      Why Apple Should Skip The MacBook Pro Launch

      January 12, 2021

      Apollo G2J Showcases Electric Sports Car

      January 12, 2021
    • Tsaro

      Ba a Fasa Bututun Mai Ko Ɗaya a Niger Delta a 2025 Ba – Sojoj

      January 20, 2026

      Sojojin Najeriya Sun Ƙwato lita 290,000 Na Man Fetur a Yankin Neja Delta

      October 21, 2025

      Ƴan Bindiga Sun Ƙwace Wayoyin Ƴan Sanda a Zamfara

      October 2, 2025

      Gwamnan Kano Ya Buƙaci Tinubu Ya Tsige Kwamishinan Ƴan Sandan Jihar

      October 1, 2025

      Will Using a VPN on Phone Helps Protect You from Ransomware?

      January 14, 2021
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    Home » Janye Ƴansanda Daga Bawa Manyan Mutane Kariya Zai Jefa Rayuwarmu Cikin Haɗari – Sanatoci
    Featured

    Janye Ƴansanda Daga Bawa Manyan Mutane Kariya Zai Jefa Rayuwarmu Cikin Haɗari – Sanatoci

    Abbass AbdurrahmanBy Abbass AbdurrahmanNovember 27, 2025No Comments2 Mins Read

    Wasu Sanatoci a Majalisar Dattawan Najeriya sun nuna damuwa kan umarnin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na janye jami’an ’yan sanda da ke tsaron manyan mutane (VIPs), inda suka ce matakin na iya barin su cikin barazana ta tsaro a lokacin da hare-hare da garkuwa da mutane ke ƙaruwa a faɗin ƙasar. A zaman su na ranar Laraba26 ga Nuwamba, Sanatoci da dama sun bayyana cewa su ne manyan abubuwan da ’yan bindiga da ’yan ta’adda ke nema, don haka janye musu tsaro a wannan lokaci ba dai-dai ba ne. Sun kuma ce su kan yi zirga-zirga zuwa yankuna masu hadari a lokacin gudanar da ayyukan mazabu da sa ido, abin da ke kara musu bukatar tsaro.

    Rahoton ya ce tattaunawar ta samo asali ne daga maganar da Sanata Oyelola Ashiru kan bukatar gaggawar shirin gwamnatin tarayya don dakile matsalar tsaro da ke kara ta’azzara. Sanatoci da dama ciki har da Aliyu Wamakko da Tahir Monguno sun bayyana cewa janye tsaro zai kara bude kofar hare-hare, yayin da wasu suka nemi a sake duba tsarin saboda matsayin kasar a halin yanzu. A sakamakon haka, Majalisar Dattawa ta amince da tattaunawa da Shugaban Kasa da hukumomin ’yan sanda don neman a gyara ko sassauta tsarin.

    Majalisar ta kuma tattauna batun dokar yaki da garkuwa da mutane, inda ta amince cewa a daidaita ta ta yadda satar mutane za ta zama laifin ta’addanci tare da hukuncin kisa idan an sabunta dokar. Sanatoci sun yi nuni da cewa ’yan bindiga na kara samun karfin gwiwa, yayin da wasu suka bukaci a hana tattaunawa ko biyan kudin fansa ga masu garkuwa da mutane. Har ila yau, Majalisar ta bukaci a kafa rundunar haɗin gwiwa a yankin Kwara–Kogi da kuma gudanar da bincike kan janye sojoji a Kebbi kafin sace dalibai.

    A wani bangare, Majalisar ta tattauna yiwuwar sake duba dokar mallakar bindiga domin bai wa ’yan kasa masu kwarewa damar mallakar kayan kariya. Mataimakin Shugaban Majalisar, Barau Jibrin, ya ce gwamnatocin jihohi dole su kara hadin kai da hukumomin tsaro na tarayya domin magance matsalar tsaro. Ya kara da cewa Shugaba Tinubu na daukar matakai, amma ana bukatar karin jari, kayan aiki da inganta rundunar ’yan sanda fiye da canza suna. Ana sa ran Majalisar za ta mika sakamakon tattaunawar ga Shugaban Kasa tare da samun martani cikin mako guda.

    Ƴansanda
    Share. Facebook Twitter WhatsApp Telegram
    Previous ArticleSama Da Mutane Miliyan Ɗaya Sun Kammala Rijistar Katin Zaɓe – INEC
    Next Article Saura Ƙiris Mu Daƙile Matsalar Tsaro a Najeriya – Badaru Abubakar
    Abbass Abdurrahman
    • Website

    Related Posts

    Featured

    Iran Ta Naɗa Ayatollah Arafi A Matsayin Jagoran Addini Na Riƙo

    March 1, 2026
    Featured

    Majalisar Dattawa Ta Sha Alwashin Amincewa da Dokar Kafa ‘Yan Sandan Jihohi Kafin Ƙarshen 2026

    March 1, 2026
    Featured

    Iran Ta Ayyana Zaman Makoki na Kwanaki 40 Bayan Mutuwar Jagora Ayatoullah Khamenei 

    March 1, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    SABBIN LABARAI

    Gwamnatin Kano Ta Dakatar da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi

    October 1, 202543 Views

    Kotu Ta Yankewa Tsohon Firayim Ministan Mali Hukuncin Zaman Gidan Yari Sakamakon Rubutu a Shafin Sada Zumunta

    October 27, 202541 Views

    Dantawaye Ya Zama Sabon Kwamishinan Ƴansanda a Abuja

    October 17, 202532 Views

    NAFDAC Ta Yi Gargaɗi Kan Wani Kororon Roba Me Matuƙar Haɗari Ga Lafiya

    December 30, 202527 Views

    An Gano Motar Ofishin Mataimakin Gwamna Da Aka Sace

    November 12, 202527 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    • Telegram
    © 2026 Bechi Hausa News. Developed by: ENGRMKS & CO.
    • Shafin Farko
    • Game da Mu
    • Ƙarin Bayani
    • Manufar Sirri
    • Ka’idoji da Sharudda
    • Tuntuɓe Mu

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.