Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    • Shafin Farko
    • Labarai

      Gwamnatin Kano Ta Shiryawa Ƴan Jaridar Yanar Gizo Horo Na Yini Biyu a Jigawa

      January 15, 2026

      Tanka Ta Murƙushe Mutane 5 a Gombe

      January 12, 2026

      Babu Siyasa a Binciken Da Ake Yi Wa Malami – EFCC

      January 12, 2026

      Ƴan Bindiga Sun Kashe Soja Da Jam’in NSCDC a Benue

      January 12, 2026

      Manyan Jiga-jigan APC 3 a Kogi Sun Mutu

      January 12, 2026
    • Siyasa

      Manyan Jiga-jigan APC 3 a Kogi Sun Mutu

      January 12, 2026

      Ganduje Zai Gana Da Masu Ruwa-da-tsaki Na APC

      January 11, 2026

      Datti Baba-Ahmed Ya Musanta Batun Tsayawa Takarar Shugaban Ƙasa

      January 9, 2026

      Fubara Barazana Ne Ga Demokaraɗiyya – Kakakin Majalisar Rivers

      January 9, 2026

      Kotu Ta Ƙi Bayar da Belin Kwamishinan Kuɗi Na Bauchi

      January 6, 2026
    • Addini

      Kano: Hisbah Ta Karɓi Ƙorafe-Ƙorafe Sama da 12,000 a 2025

      January 2, 2026

      Da Ɗumi-ɗumi : Sheikh Dahiru Bauchi Ya rasu

      November 27, 2025

      Zakaran Gwajin Dafi : Hajji 2025 Karkashin Farfesa Saleh Pakistan  

      November 24, 2025

      Hajji Da Shugabanci Nagari Ƙarƙashin Jagorancin Farfesa Pakistan

      November 17, 2025

      Hukumar NAHCON Ta Sanar Da Rage Kudin Aikin Hajjin 2026

      November 10, 2025
    • Nishadi

      Oculus Founder Makes a VR Headset That Can Literally Kill You

      January 13, 2021
      85

      Braun Series 7 Electric Shaver Review: Quality at a Good Price

      January 13, 2021
      85

      Google Pixel 7, iPhone 14 Compared: Check Out 5 Major Differences

      January 13, 2021

      Why Apple Should Skip The MacBook Pro Launch

      January 12, 2021

      Apollo G2J Showcases Electric Sports Car

      January 12, 2021
    • Tsaro

      Sojojin Najeriya Sun Ƙwato lita 290,000 Na Man Fetur a Yankin Neja Delta

      October 21, 2025

      Ƴan Bindiga Sun Ƙwace Wayoyin Ƴan Sanda a Zamfara

      October 2, 2025

      Gwamnan Kano Ya Buƙaci Tinubu Ya Tsige Kwamishinan Ƴan Sandan Jihar

      October 1, 2025

      Will Using a VPN on Phone Helps Protect You from Ransomware?

      January 14, 2021

      Popular New Xbox Game Pass Game Being Review Bombed With “0s”

      January 14, 2021
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    Home » Janye Ƴansanda Daga Bawa Manyan Mutane Kariya Zai Jefa Rayuwarmu Cikin Haɗari – Sanatoci
    Featured

    Janye Ƴansanda Daga Bawa Manyan Mutane Kariya Zai Jefa Rayuwarmu Cikin Haɗari – Sanatoci

    Abbass AbdurrahmanBy Abbass AbdurrahmanNovember 27, 2025No Comments2 Mins Read

    Wasu Sanatoci a Majalisar Dattawan Najeriya sun nuna damuwa kan umarnin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na janye jami’an ’yan sanda da ke tsaron manyan mutane (VIPs), inda suka ce matakin na iya barin su cikin barazana ta tsaro a lokacin da hare-hare da garkuwa da mutane ke ƙaruwa a faɗin ƙasar. A zaman su na ranar Laraba26 ga Nuwamba, Sanatoci da dama sun bayyana cewa su ne manyan abubuwan da ’yan bindiga da ’yan ta’adda ke nema, don haka janye musu tsaro a wannan lokaci ba dai-dai ba ne. Sun kuma ce su kan yi zirga-zirga zuwa yankuna masu hadari a lokacin gudanar da ayyukan mazabu da sa ido, abin da ke kara musu bukatar tsaro.

    Rahoton ya ce tattaunawar ta samo asali ne daga maganar da Sanata Oyelola Ashiru kan bukatar gaggawar shirin gwamnatin tarayya don dakile matsalar tsaro da ke kara ta’azzara. Sanatoci da dama ciki har da Aliyu Wamakko da Tahir Monguno sun bayyana cewa janye tsaro zai kara bude kofar hare-hare, yayin da wasu suka nemi a sake duba tsarin saboda matsayin kasar a halin yanzu. A sakamakon haka, Majalisar Dattawa ta amince da tattaunawa da Shugaban Kasa da hukumomin ’yan sanda don neman a gyara ko sassauta tsarin.

    Majalisar ta kuma tattauna batun dokar yaki da garkuwa da mutane, inda ta amince cewa a daidaita ta ta yadda satar mutane za ta zama laifin ta’addanci tare da hukuncin kisa idan an sabunta dokar. Sanatoci sun yi nuni da cewa ’yan bindiga na kara samun karfin gwiwa, yayin da wasu suka bukaci a hana tattaunawa ko biyan kudin fansa ga masu garkuwa da mutane. Har ila yau, Majalisar ta bukaci a kafa rundunar haɗin gwiwa a yankin Kwara–Kogi da kuma gudanar da bincike kan janye sojoji a Kebbi kafin sace dalibai.

    A wani bangare, Majalisar ta tattauna yiwuwar sake duba dokar mallakar bindiga domin bai wa ’yan kasa masu kwarewa damar mallakar kayan kariya. Mataimakin Shugaban Majalisar, Barau Jibrin, ya ce gwamnatocin jihohi dole su kara hadin kai da hukumomin tsaro na tarayya domin magance matsalar tsaro. Ya kara da cewa Shugaba Tinubu na daukar matakai, amma ana bukatar karin jari, kayan aiki da inganta rundunar ’yan sanda fiye da canza suna. Ana sa ran Majalisar za ta mika sakamakon tattaunawar ga Shugaban Kasa tare da samun martani cikin mako guda.

    Ƴansanda
    Share. Facebook Twitter WhatsApp Telegram
    Previous ArticleSama Da Mutane Miliyan Ɗaya Sun Kammala Rijistar Katin Zaɓe – INEC
    Next Article Saura Ƙiris Mu Daƙile Matsalar Tsaro a Najeriya – Badaru Abubakar
    Abbass Abdurrahman
    • Website

    Related Posts

    Featured

    Gwamnatin Kano Ta Shiryawa Ƴan Jaridar Yanar Gizo Horo Na Yini Biyu a Jigawa

    January 15, 2026
    Featured

    Tanka Ta Murƙushe Mutane 5 a Gombe

    January 12, 2026
    Featured

    Babu Siyasa a Binciken Da Ake Yi Wa Malami – EFCC

    January 12, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    SABBIN LABARAI

    Gwamnatin Kano Ta Dakatar da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi

    October 1, 202542 Views

    Kotu Ta Yankewa Tsohon Firayim Ministan Mali Hukuncin Zaman Gidan Yari Sakamakon Rubutu a Shafin Sada Zumunta

    October 27, 202541 Views

    Dantawaye Ya Zama Sabon Kwamishinan Ƴansanda a Abuja

    October 17, 202532 Views

    An Gano Motar Ofishin Mataimakin Gwamna Da Aka Sace

    November 12, 202527 Views

    NAFDAC Ta Yi Gargaɗi Kan Wani Kororon Roba Me Matuƙar Haɗari Ga Lafiya

    December 30, 202525 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    • Telegram
    © 2026 Bechi Hausa News. Developed by: ENGRMKS & CO.
    • Shafin Farko
    • Game da Mu
    • Ƙarin Bayani
    • Manufar Sirri
    • Ka’idoji da Sharudda
    • Tuntuɓe Mu

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.