Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    • Shafin Farko
    • Labarai

      Iran Ta Naɗa Ayatollah Arafi A Matsayin Jagoran Addini Na Riƙo

      March 1, 2026

      Majalisar Dattawa Ta Sha Alwashin Amincewa da Dokar Kafa ‘Yan Sandan Jihohi Kafin Ƙarshen 2026

      March 1, 2026

      Iran Ta Ayyana Zaman Makoki na Kwanaki 40 Bayan Mutuwar Jagora Ayatoullah Khamenei 

      March 1, 2026

      Mutum 40 Sun Mutu a Harin da Aka Kai Makarantar Ƴanmata a Iran

      February 28, 2026

      Iran Ta Sha Alwashin Kare Kanta Daga Hare-haren Amurka da Isra’ila

      February 28, 2026
    • Siyasa

      Gwamnan Adamawa Ya Sauya Sheƙa Zuwa APC

      February 27, 2026

      NDLEA Ta Kama Wata Mata Mai Cikin Bogi Ɗauke da Hodar Iblis a Iyakar Seme

      February 22, 2026

      Jam’iyyun Adawa Sun Kaurace wa Zaɓen Kano, APC Ta Lashe Kujerun Majalisa a Rivers

      February 22, 2026

      Kotu Ta Umarci INEC Ta Yi Wa Jam’iyyar NDP Rajista

      February 19, 2026

      Gwamnan Zamfara Ya Zargi Gwamnatin Tarayya da Nuna Masa Wariya Saboda Bambancin Jam’iyya

      February 18, 2026
    • Addini

      Bauchi Ta neman ƙarin Kujerun Hajji Daga Saudiyya

      February 16, 2026

      Sarkin Musulmi Ya Umarci Ƴan Najeriya Su Fara Duban Jinjirin Watan Ramadan Ranar Talata

      February 16, 2026

      Tinubu Ya Naɗa Ambasada Ismail Abba Yusuf a Matsayin Sabon Shugaban NAHCON

      February 11, 2026

      Sheikh Usman Kusfa Zaria (Rigi-rigi) Ya Rasu

      February 2, 2026

      Jigawa Ta Fara Gwajin Lafiya ga Maniyyatan Hajjin 2026

      January 28, 2026
    • Nishadi

      Oculus Founder Makes a VR Headset That Can Literally Kill You

      January 13, 2021
      85

      Braun Series 7 Electric Shaver Review: Quality at a Good Price

      January 13, 2021
      85

      Google Pixel 7, iPhone 14 Compared: Check Out 5 Major Differences

      January 13, 2021

      Why Apple Should Skip The MacBook Pro Launch

      January 12, 2021

      Apollo G2J Showcases Electric Sports Car

      January 12, 2021
    • Tsaro

      Ba a Fasa Bututun Mai Ko Ɗaya a Niger Delta a 2025 Ba – Sojoj

      January 20, 2026

      Sojojin Najeriya Sun Ƙwato lita 290,000 Na Man Fetur a Yankin Neja Delta

      October 21, 2025

      Ƴan Bindiga Sun Ƙwace Wayoyin Ƴan Sanda a Zamfara

      October 2, 2025

      Gwamnan Kano Ya Buƙaci Tinubu Ya Tsige Kwamishinan Ƴan Sandan Jihar

      October 1, 2025

      Will Using a VPN on Phone Helps Protect You from Ransomware?

      January 14, 2021
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    Home » Majalisar Dattawa Na Duba Yiwuwar Baiwa Ƴan Najeriya Damar Riƙe Bindiga
    Featured

    Majalisar Dattawa Na Duba Yiwuwar Baiwa Ƴan Najeriya Damar Riƙe Bindiga

    Abbass AbdurrahmanBy Abbass AbdurrahmanNovember 27, 2025No Comments2 Mins Read

    Majalisar Dattawan Najeriya ta amince da kudiri na neman gwamnatin tarayya ta sake duba dokar mallakar bindiga domin bawa ɗaiɗaikun ‘yan kasa masu bin doka damar mallaka, sakamakon ƙarin tabarbarewar tsaro a jihohin Kwara, Kebbi da Neja. Dalilin kudirin ya biyo bayan hare-hare da garkuwa da mutane a makarantu, coci-coci da kauyuka, ciki har da harin da aka kai cocin CAC a Eruku ranar 18 ga Nuwamba, inda aka kashe mutane biyu aka yi garkuwa da 38 waɗanda daga bisani aka sako su. Sanatoci da dama sun jaddada buƙatar ɗaukar matakin gaggawa don dakile ta’addanci, fashi da makami, da yawaitar sace ɗalibai da ke tilasta rufe makarantu da dubban yara ke karatu.

    A yayin muhawara, sanatoci sun yaba wa shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu bisa soke tafiyarsa zuwa kasashen waje don jagorantar martanin tsaro wanda ya taimaka wajen kubutar da waɗanda aka yi garkuwa da su a Kwara da kuma ‘yan matan makaranta 24 na Kebbi. Sai dai wasu sanatocin sun bukaci bayyana wanda ya bayar da umarnin janye sojoji kafin sace ɗalibai a Maga, inda suka bayyana hakan a matsayin alamar matsalar cikin gida a hukumomin tsaro. Wasu kuma sun nuna damuwa kan kisan Brig-Gen Musa Uba da suka ce ya kara nuna tabarbarewar amincewa da dabarun tsaron kasa.

    Shugaban marasa rinjaye da wasu sanatoci sun yi kira da a binciki yiwuwar masu fallasa tsari a cikin jami’an tsaro tare da tabbatar da sake fasalin tsarin tsaro cikin gaggawa domin karya karfin ‘yan ta’adda. Sanata Barau Jibrin ya jaddada cewa lamarin tsaro ba na gwamnatin tarayya kaɗai ba ne, inda ya bukaci gwamnatocin jihohi, kamfanoni, da al’umma su mara baya domin saurin shawo kan kalubalen tsaro. Ya kuma nemi jihohi su zuba jari a kayan sa-ido da hanyoyin tattara bayanan sirri domin taimakawa rundunonin tsaro su fi saurin daukar mataki.

    Majalisar Dattawa ta kuma kada kuri’ar bukatar a yi gyara ga dokar bindiga domin ta dace da kalubalen tsaro na yanzu, kamar yadda kasashe sama da 175 ke ba da damar mallakar bindiga ga ‘yan kasa masu bin doka. Sanatoci sun ce lokaci yana kurewa, kuma dole ne gwamnati ta dauki tsattsauran mataki kan ‘yan bindiga, masu garkuwa da mutane, da miyagu da ke addabar al’umma. Sun ce rayuka na salwanta kuma wannan ba lokacin wasa ko nuna siyasa ba ne, domin matsalar na bukatar dabaru, kwarewa, da himma gaba ɗaya domin mayar da kasar kan turbar zaman lafiya.

    Majalisar Dattawa
    Share. Facebook Twitter WhatsApp Telegram
    Previous ArticleDa Ɗumi-ɗumi : Sheikh Dahiru Bauchi Ya rasu
    Next Article Sama Da Mutane Miliyan Ɗaya Sun Kammala Rijistar Katin Zaɓe – INEC
    Abbass Abdurrahman
    • Website

    Related Posts

    Featured

    Iran Ta Naɗa Ayatollah Arafi A Matsayin Jagoran Addini Na Riƙo

    March 1, 2026
    Featured

    Majalisar Dattawa Ta Sha Alwashin Amincewa da Dokar Kafa ‘Yan Sandan Jihohi Kafin Ƙarshen 2026

    March 1, 2026
    Featured

    Iran Ta Ayyana Zaman Makoki na Kwanaki 40 Bayan Mutuwar Jagora Ayatoullah Khamenei 

    March 1, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    SABBIN LABARAI

    Gwamnatin Kano Ta Dakatar da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi

    October 1, 202543 Views

    Kotu Ta Yankewa Tsohon Firayim Ministan Mali Hukuncin Zaman Gidan Yari Sakamakon Rubutu a Shafin Sada Zumunta

    October 27, 202541 Views

    Dantawaye Ya Zama Sabon Kwamishinan Ƴansanda a Abuja

    October 17, 202532 Views

    NAFDAC Ta Yi Gargaɗi Kan Wani Kororon Roba Me Matuƙar Haɗari Ga Lafiya

    December 30, 202527 Views

    An Gano Motar Ofishin Mataimakin Gwamna Da Aka Sace

    November 12, 202527 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    • Telegram
    © 2026 Bechi Hausa News. Developed by: ENGRMKS & CO.
    • Shafin Farko
    • Game da Mu
    • Ƙarin Bayani
    • Manufar Sirri
    • Ka’idoji da Sharudda
    • Tuntuɓe Mu

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.