Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    • Shafin Farko
    • Labarai

      Ba Kama Gbajabiamila Muka Yi Ba Gayyatarsa Muka Yi – ICPC

      July 21, 2026

      Tinubu Ya Naɗa Sabbin Shugabanni Da Mambobi 26 a Hukumomi Da Kwamitocin Gwamnatin Tarayya

      July 21, 2026

      An Zargi Likitan El-Rufai Da Bayar da Rahoton Jinya Na Bogi

      July 21, 2026

      Guguwa Da Ruwan Sama Mai Ƙarfi Sun Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutane Huɗu a Sakkwato

      July 21, 2026

      Mamakon Ruwan Sama Ya Lalata Gidaje Da Gonaki a Filato

      July 20, 2026
    • Siyasa

      Kotu Ta Yi Watsi da Ƙarar da Tsagin Tanimu Turaki Suka Shigar Kan Rikicin Shugabancin PDP

      July 18, 2026

      Ya Kamata Majalisa Ta Yi Bincike Kan Ingancin Lafiyar Tinubu – ADC

      July 17, 2026

      Gwamna Yusuf Ya Zaɓi Garo a Matsayin Mataimakinsa a Zaɓen 2027

      July 13, 2026

      INEC Ta Ƙara Wa’adin Miƙa Sunayen ‘Yan Takarar Zaɓen 2027

      July 12, 2026

      Sauye-sauyen Gwamnatina Sun Inganta Ayyuka Da Tattalin Arziki a Kaduna – Gwamna Uba Sani 

      July 10, 2026
    • Addini

      An Rufe Birnin Tehran Domin Jana’izar Ayatollah Ali Khamenei

      July 1, 2026

      Kotu Ta Buƙaci a Gabatar Da Litattafan Da Sheikh Abduljabbar Ya Yi Amfani Da Su

      June 29, 2026

      NAHCON Ta Kammala Dawo Da Alhazan Najeriya Daga Saudiyya

      June 23, 2026

      Sarkin Musulmi Ya Buƙaci Hukumomi Su Gaggauta Ɗaukar Matakai Domin Magance Matsalar Tsaro

      June 17, 2026

      Gwamnatin Kano Za Ta Kashe Naira Biliyan 1.5 Domin Shirin ‘Auren Gata’

      June 15, 2026
    • Nishadi

      Oculus Founder Makes a VR Headset That Can Literally Kill You

      January 13, 2021
      85

      Braun Series 7 Electric Shaver Review: Quality at a Good Price

      January 13, 2021
      85

      Google Pixel 7, iPhone 14 Compared: Check Out 5 Major Differences

      January 13, 2021

      Why Apple Should Skip The MacBook Pro Launch

      January 12, 2021

      Apollo G2J Showcases Electric Sports Car

      January 12, 2021
    • Tsaro

      Sojoji Sun Kama Ƴan Ƙasashen Waje Da Ake Zargin Suna da Hannu a Matsalar Tsaron Najeriya – Bwala

      July 18, 2026

      ‘Yan Sanda Sun Fara Kwato Makaman Da Ke Hannun Jama’a Ba Bisa Ka’ida Ba – IGP Disu 

      July 17, 2026

      Sojoji Sun Gano Ƴan Ƙasashen Waje Uku Cikin Mayaƙan ISWAP a Borno

      July 13, 2026

      An Kashe Fitaccen Jagoran ‘Yan Bindiga Sani Yellow a Zamfara

      July 12, 2026

      Matasa a Borno Sun Gudanar Da Zanga-Zanga Kan Rashin Tsaro

      July 12, 2026
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    Home » Majalisar Dattawa Na Duba Yiwuwar Baiwa Ƴan Najeriya Damar Riƙe Bindiga
    Featured

    Majalisar Dattawa Na Duba Yiwuwar Baiwa Ƴan Najeriya Damar Riƙe Bindiga

    Abbass AbdurrahmanBy Abbass AbdurrahmanNovember 27, 2025No Comments2 Mins Read

    Majalisar Dattawan Najeriya ta amince da kudiri na neman gwamnatin tarayya ta sake duba dokar mallakar bindiga domin bawa ɗaiɗaikun ‘yan kasa masu bin doka damar mallaka, sakamakon ƙarin tabarbarewar tsaro a jihohin Kwara, Kebbi da Neja. Dalilin kudirin ya biyo bayan hare-hare da garkuwa da mutane a makarantu, coci-coci da kauyuka, ciki har da harin da aka kai cocin CAC a Eruku ranar 18 ga Nuwamba, inda aka kashe mutane biyu aka yi garkuwa da 38 waɗanda daga bisani aka sako su. Sanatoci da dama sun jaddada buƙatar ɗaukar matakin gaggawa don dakile ta’addanci, fashi da makami, da yawaitar sace ɗalibai da ke tilasta rufe makarantu da dubban yara ke karatu.

    A yayin muhawara, sanatoci sun yaba wa shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu bisa soke tafiyarsa zuwa kasashen waje don jagorantar martanin tsaro wanda ya taimaka wajen kubutar da waɗanda aka yi garkuwa da su a Kwara da kuma ‘yan matan makaranta 24 na Kebbi. Sai dai wasu sanatocin sun bukaci bayyana wanda ya bayar da umarnin janye sojoji kafin sace ɗalibai a Maga, inda suka bayyana hakan a matsayin alamar matsalar cikin gida a hukumomin tsaro. Wasu kuma sun nuna damuwa kan kisan Brig-Gen Musa Uba da suka ce ya kara nuna tabarbarewar amincewa da dabarun tsaron kasa.

    Shugaban marasa rinjaye da wasu sanatoci sun yi kira da a binciki yiwuwar masu fallasa tsari a cikin jami’an tsaro tare da tabbatar da sake fasalin tsarin tsaro cikin gaggawa domin karya karfin ‘yan ta’adda. Sanata Barau Jibrin ya jaddada cewa lamarin tsaro ba na gwamnatin tarayya kaɗai ba ne, inda ya bukaci gwamnatocin jihohi, kamfanoni, da al’umma su mara baya domin saurin shawo kan kalubalen tsaro. Ya kuma nemi jihohi su zuba jari a kayan sa-ido da hanyoyin tattara bayanan sirri domin taimakawa rundunonin tsaro su fi saurin daukar mataki.

    Majalisar Dattawa ta kuma kada kuri’ar bukatar a yi gyara ga dokar bindiga domin ta dace da kalubalen tsaro na yanzu, kamar yadda kasashe sama da 175 ke ba da damar mallakar bindiga ga ‘yan kasa masu bin doka. Sanatoci sun ce lokaci yana kurewa, kuma dole ne gwamnati ta dauki tsattsauran mataki kan ‘yan bindiga, masu garkuwa da mutane, da miyagu da ke addabar al’umma. Sun ce rayuka na salwanta kuma wannan ba lokacin wasa ko nuna siyasa ba ne, domin matsalar na bukatar dabaru, kwarewa, da himma gaba ɗaya domin mayar da kasar kan turbar zaman lafiya.

    Majalisar Dattawa
    Share. Facebook Twitter WhatsApp Telegram
    Previous ArticleDa Ɗumi-ɗumi : Sheikh Dahiru Bauchi Ya rasu
    Next Article Sama Da Mutane Miliyan Ɗaya Sun Kammala Rijistar Katin Zaɓe – INEC
    Abbass Abdurrahman
    • Website

    Related Posts

    Featured

    Ba Kama Gbajabiamila Muka Yi Ba Gayyatarsa Muka Yi – ICPC

    July 21, 2026
    Featured

    Tinubu Ya Naɗa Sabbin Shugabanni Da Mambobi 26 a Hukumomi Da Kwamitocin Gwamnatin Tarayya

    July 21, 2026
    Featured

    An Zargi Likitan El-Rufai Da Bayar da Rahoton Jinya Na Bogi

    July 21, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    SABBIN LABARAI

    Ba Don Gudunmawar Masu Yiwa Ƙasa Hidima Ba Da Jihohi Dayawa Basu Kai Yadda Suke a Yanzu Ba – Minista

    December 8, 2025150 Views

    Sabon Rikici Ya Kunno Kai a NDC : Ƴan Takara Sun Kai Ƙara Kan Zaɓen Fidda-gwani a Kano

    June 30, 202679 Views

    Gwamnatin Kano Ta Dakatar da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi

    October 1, 202546 Views

    Kotu Ta Yankewa Tsohon Firayim Ministan Mali Hukuncin Zaman Gidan Yari Sakamakon Rubutu a Shafin Sada Zumunta

    October 27, 202541 Views

    Dantawaye Ya Zama Sabon Kwamishinan Ƴansanda a Abuja

    October 17, 202533 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    • Telegram
    © 2026 Bechi Hausa News. Developed by: ENGRMKS & CO.
    • Shafin Farko
    • Game da Mu
    • Ƙarin Bayani
    • Manufar Sirri
    • Ka’idoji da Sharudda
    • Tuntuɓe Mu

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.