Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar ADC a zaɓen 2027, Atiku Abubakar, ya soki tafiyar da Shugaba Bola Tinubu ya yi zuwa Turai na tsawon makwanni uku, yana mai cewa shugaban ya zaɓi yin hutu a daidai lokacin da ƙasar ke cikin mawuyacin hali.
Atiku ya ce duk da cewa shi ma ya taɓa yin tafiye-tafiye da zama a ƙasashen waje, akwai babban bambanci tsakanin tafiyar mutum mai zaman kansa da ta shugaban ƙasa mai ci. Ya ce shugabanci na buƙatar sanin lokacin da ƙasa ke buƙatar shugabanta ya kasance a gida.
A cewarsa, ‘yan Najeriya na fama da tsadar rayuwa, tsadar man fetur, abinci da sufuri, yayin da matsalar tsaro ke ci gaba da jefa rayukan jama’a cikin haɗari. Ya ce abin mamaki ne yadda Tinubu ya bar ƙasar zuwa Turai a lokacin da Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, shi ma yake wata tafiya ta aiki a ƙetare.
Atiku ya kuma zargi gwamnatin Tinubu da gaza fahimtar irin wahalhalun da ‘yan ƙasa ke ciki, yana mai cewa idan aka ba shi dama, zai mayar da hankali wajen sanya Najeriya ta zama ƙasa mai sauƙin rayuwa ga jama’arta.

