Gwamnatin Jihar Kano ta fara raba takardun filaye ga masu taimaka wa Gwamna Abba Kabir Yusuf 2,500, ciki har da manyan masu ba shi shawara da na musamman, masu ba da rahoto da kuma wakilan rumfunan zaɓe da aka fi sani da “’Yan Akwatu”.
Kwamishinan Filaye da Tsare-tsaren Birane, Abduljabbar Muhammad Umar Garko, ya ce shirin na da nufin taimaka wa waɗanda suka amfana su mallaki gidaje, tare da rage gibin gidaje da kuma inganta tsarin gine-gine a jihar. Ya kuma gargaɗe su da kada su sayar da filayen ko su bari masu kwace filaye su karɓe su.
Garko ya ce an tsara wuraren da aka ware filayen tare da samar da muhimman abubuwan more rayuwa kamar masallatai, makarantu, tashoshin kashe gobara da wuraren tsaro. Ya ƙara da cewa gwamnati na sabunta tsarin kula da filaye ta hanyar amfani da fasahar zamani a Ma’aikatar Filaye da Tsare-tsaren Birane da kuma KANGIS.
Da yake wakiltar Gwamna Abba Kabir Yusuf, Sakataren Gwamnatin Jihar Kano, Umar Faruk Ibrahim, ya ce rabon filayen na daga cikin matakan gwamnati na inganta jin daɗin ma’aikata da ƙara damar mallakar filaye. Ya ce gwamnati ta kuma aiwatar da wasu shirye-shirye a fannonin ilimi, hanyoyi, noma, ruwa, gidaje da gyaran tsarin mallakar filaye.

