Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta sanar da cewa an riga an sayar da dukkan gurabe 3,050 da aka ware wa jihar domin gudanar da aikin Hajjin shekarar 2027.
Babban Daraktan hukumar, Abubakar Ibrahim Matawalle, ya ce sama da mahajjata 200 suna cikin jerin masu jiran gurbin da zai samu, bayan sun kammala biyan kuɗin Hajji tare da samun fasfo ɗinsu na ƙasashen waje.
Ya kuma gargaɗi waɗanda suka biya kuɗin Hajji amma ba su miƙa fasfo ɗinsu na e-passport ba da su gaggauta yin hakan kafin ranar 5 ga watan Satumba, yana mai cewa waɗanda suka gaza za su iya rasa gurabensu.
Matawalle ya ce hukumar na shirin inganta tsarin kula da mahajjatan Kano, musamman wajen masauki da sauran ayyukan jin daɗinsu. Ya ce za a rage yawan gidajen da ake amfani da su wajen saukar da mahajjata domin sauƙaƙa sa ido da samar da abinci, kula da lafiya da sauran hidimomi.

