Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    • Shafin Farko
    • Labarai

      Mutane 4 Sun Mutu a Turmutsutsun Karɓar Sadaka a Katsina

      March 2, 2026

      Ba Za Mu Bayar da Tabbacin Sahihin Zaɓe a 2027 Ba – Amupitan

      March 2, 2026

      Jirage Marasa Matuƙa Sun Kai Hari Matatar Man Saudiyya

      March 2, 2026

      Najeriya Ta Buƙaci a Kawo Karshen Rikicin Gabas ta Tsakiya

      March 2, 2026

      Iran Ta Naɗa Ayatollah Arafi A Matsayin Jagoran Addini Na Riƙo

      March 1, 2026
    • Siyasa

      Gwamnan Adamawa Ya Sauya Sheƙa Zuwa APC

      February 27, 2026

      NDLEA Ta Kama Wata Mata Mai Cikin Bogi Ɗauke da Hodar Iblis a Iyakar Seme

      February 22, 2026

      Jam’iyyun Adawa Sun Kaurace wa Zaɓen Kano, APC Ta Lashe Kujerun Majalisa a Rivers

      February 22, 2026

      Kotu Ta Umarci INEC Ta Yi Wa Jam’iyyar NDP Rajista

      February 19, 2026

      Gwamnan Zamfara Ya Zargi Gwamnatin Tarayya da Nuna Masa Wariya Saboda Bambancin Jam’iyya

      February 18, 2026
    • Addini

      Bauchi Ta neman ƙarin Kujerun Hajji Daga Saudiyya

      February 16, 2026

      Sarkin Musulmi Ya Umarci Ƴan Najeriya Su Fara Duban Jinjirin Watan Ramadan Ranar Talata

      February 16, 2026

      Tinubu Ya Naɗa Ambasada Ismail Abba Yusuf a Matsayin Sabon Shugaban NAHCON

      February 11, 2026

      Sheikh Usman Kusfa Zaria (Rigi-rigi) Ya Rasu

      February 2, 2026

      Jigawa Ta Fara Gwajin Lafiya ga Maniyyatan Hajjin 2026

      January 28, 2026
    • Nishadi

      Oculus Founder Makes a VR Headset That Can Literally Kill You

      January 13, 2021
      85

      Braun Series 7 Electric Shaver Review: Quality at a Good Price

      January 13, 2021
      85

      Google Pixel 7, iPhone 14 Compared: Check Out 5 Major Differences

      January 13, 2021

      Why Apple Should Skip The MacBook Pro Launch

      January 12, 2021

      Apollo G2J Showcases Electric Sports Car

      January 12, 2021
    • Tsaro

      Ba a Fasa Bututun Mai Ko Ɗaya a Niger Delta a 2025 Ba – Sojoj

      January 20, 2026

      Sojojin Najeriya Sun Ƙwato lita 290,000 Na Man Fetur a Yankin Neja Delta

      October 21, 2025

      Ƴan Bindiga Sun Ƙwace Wayoyin Ƴan Sanda a Zamfara

      October 2, 2025

      Gwamnan Kano Ya Buƙaci Tinubu Ya Tsige Kwamishinan Ƴan Sandan Jihar

      October 1, 2025

      Will Using a VPN on Phone Helps Protect You from Ransomware?

      January 14, 2021
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    Home » Matsalar Tsaro: Abin Kunya Ne Yadda Ake Rufe Makarantu a Najeriya – Buba Galadima
    Featured

    Matsalar Tsaro: Abin Kunya Ne Yadda Ake Rufe Makarantu a Najeriya – Buba Galadima

    Abbass AbdurrahmanBy Abbass AbdurrahmanNovember 25, 2025No Comments2 Mins Read

    Fitaccen jigo a jam’iyyar NNPP, Buba Galadima, ya caccaki matakin rufe makarantu a wasu sassan Arewacin Najeriya sakamakon tabarbarewar tsaro, yana kiran hukuncin a matsayin abin kunya da gazawar shugabanni wajen kare rayuka da dukiyoyin al’umma. Ya bayyana hakan ne a shirin Prime Time na ARISE News, inda ya danganta yawaitar sace-sacen dalibai a Jihar Neja da sauran yankuna da gazawar gwamnati wajen daukar tsaro da muhimmanci.

    Galadima ya jaddada cewa rufe makarantu ba mafita ba ce, yana mai cewa abin da ya dace shi ne karfafa tsaro da kare wuraren ilimi daga miyagu, ba mika su hannun ’yan bindiga ba. Ya zargi shugabanni da daukar mulki da wasa tare da ware fiye da 90 cikin 100 na lokacinsu ga siyasa maimakon yaki da rashin tsaro. Ya kuma soki dabarar gwamnati ta amfani da karfi ba tare da ingantaccen leken asiri ba, yana shawartar amfani da fasaha, basira da dabarun zamani wajen gano barazana kafin ta afku.

    Galadima ya yi ikirarin cewa jami’an tsaro sun samu bayanan sirri kafin harin da aka kai a Neja amma suka kasa daukar mataki cikin gaggawa. Ya yi tir da zargin cewa sojojin da aka tura wurin makarantar sun bar aikinsu, yana mai cewa ya dace a hukunta su bisa ka’ida. Ya kuma kwatanta tsarin tsaron Najeriya da na kasashen da ke amfani da CCTV da fasahohin sa ido wajen gano bata-garin cikin kankanin lokaci.

    A halin da ake ciki, rahotanni sun tabbatar da cewa aƙalla jihohi biyar a Arewacin Najeriya sun rufe makarantu saboda karuwar hare-haren sace mutane, yayin da wasu kuma suka umarci daliban kwana su koma gidajensu. Galadima ya nanata cewa Najeriya ta kai wani mataki da ya wuce dogaro da karfin sojoji kawai, yana kira ga gwamnatin tarayya ta sabunta dabarunta cikin gaggawa domin kare ’yan kasa da tabbatar da cigaban ilimi ba tare da katsewa ba.

    Buba Galadima
    Share. Facebook Twitter WhatsApp Telegram
    Previous ArticleASUU Na Duba Yiwuwar Sake Tsunduma Yajin Aiki
    Next Article Ganduje Zai Kafa Hukumar Hisbah Mai Zaman Kanta a Kano
    Abbass Abdurrahman
    • Website

    Related Posts

    Featured

    Mutane 4 Sun Mutu a Turmutsutsun Karɓar Sadaka a Katsina

    March 2, 2026
    Featured

    Ba Za Mu Bayar da Tabbacin Sahihin Zaɓe a 2027 Ba – Amupitan

    March 2, 2026
    Featured

    Jirage Marasa Matuƙa Sun Kai Hari Matatar Man Saudiyya

    March 2, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    SABBIN LABARAI

    Gwamnatin Kano Ta Dakatar da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi

    October 1, 202543 Views

    Kotu Ta Yankewa Tsohon Firayim Ministan Mali Hukuncin Zaman Gidan Yari Sakamakon Rubutu a Shafin Sada Zumunta

    October 27, 202541 Views

    Dantawaye Ya Zama Sabon Kwamishinan Ƴansanda a Abuja

    October 17, 202532 Views

    NAFDAC Ta Yi Gargaɗi Kan Wani Kororon Roba Me Matuƙar Haɗari Ga Lafiya

    December 30, 202527 Views

    An Gano Motar Ofishin Mataimakin Gwamna Da Aka Sace

    November 12, 202527 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    • Telegram
    © 2026 Bechi Hausa News. Developed by: ENGRMKS & CO.
    • Shafin Farko
    • Game da Mu
    • Ƙarin Bayani
    • Manufar Sirri
    • Ka’idoji da Sharudda
    • Tuntuɓe Mu

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.