Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    • Shafin Farko
    • Labarai

      Matatar Dangote Ta Ƙara Farashin Man Fetur

      March 3, 2026

      Doguwa Ya Yi Murabus Daga Muƙamin Kwamishinan Ruwa Na Kano

      March 3, 2026

      Amurka Na Da Isassun Makaman Yaƙi Da Za a Iya Amfani Da Su “Har Abada” – Trump 

      March 3, 2026

      ICPC Ta Bayyana Abubuwan Da Ta Samo Daga Gidan El-Rufai a Abuja

      March 3, 2026

      Ɗan Atiku Ya Ajiye Muƙamin Kwamishina a Gwamnatin Adamawa

      March 3, 2026
    • Siyasa

      Doguwa Ya Yi Murabus Daga Muƙamin Kwamishinan Ruwa Na Kano

      March 3, 2026

      Gwamnan Adamawa Ya Sauya Sheƙa Zuwa APC

      February 27, 2026

      NDLEA Ta Kama Wata Mata Mai Cikin Bogi Ɗauke da Hodar Iblis a Iyakar Seme

      February 22, 2026

      Jam’iyyun Adawa Sun Kaurace wa Zaɓen Kano, APC Ta Lashe Kujerun Majalisa a Rivers

      February 22, 2026

      Kotu Ta Umarci INEC Ta Yi Wa Jam’iyyar NDP Rajista

      February 19, 2026
    • Addini

      Bauchi Ta neman ƙarin Kujerun Hajji Daga Saudiyya

      February 16, 2026

      Sarkin Musulmi Ya Umarci Ƴan Najeriya Su Fara Duban Jinjirin Watan Ramadan Ranar Talata

      February 16, 2026

      Tinubu Ya Naɗa Ambasada Ismail Abba Yusuf a Matsayin Sabon Shugaban NAHCON

      February 11, 2026

      Sheikh Usman Kusfa Zaria (Rigi-rigi) Ya Rasu

      February 2, 2026

      Jigawa Ta Fara Gwajin Lafiya ga Maniyyatan Hajjin 2026

      January 28, 2026
    • Nishadi

      Oculus Founder Makes a VR Headset That Can Literally Kill You

      January 13, 2021
      85

      Braun Series 7 Electric Shaver Review: Quality at a Good Price

      January 13, 2021
      85

      Google Pixel 7, iPhone 14 Compared: Check Out 5 Major Differences

      January 13, 2021

      Why Apple Should Skip The MacBook Pro Launch

      January 12, 2021

      Apollo G2J Showcases Electric Sports Car

      January 12, 2021
    • Tsaro

      Ba a Fasa Bututun Mai Ko Ɗaya a Niger Delta a 2025 Ba – Sojoj

      January 20, 2026

      Sojojin Najeriya Sun Ƙwato lita 290,000 Na Man Fetur a Yankin Neja Delta

      October 21, 2025

      Ƴan Bindiga Sun Ƙwace Wayoyin Ƴan Sanda a Zamfara

      October 2, 2025

      Gwamnan Kano Ya Buƙaci Tinubu Ya Tsige Kwamishinan Ƴan Sandan Jihar

      October 1, 2025

      Will Using a VPN on Phone Helps Protect You from Ransomware?

      January 14, 2021
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    Home » Ministan Kuɗi Wale Edun Ya Tafi Birtaniya Don Neman Lafiya
    Featured

    Ministan Kuɗi Wale Edun Ya Tafi Birtaniya Don Neman Lafiya

    Abbass AbdurrahmanBy Abbass AbdurrahmanOctober 15, 2025No Comments2 Mins Read

    Ministan Kuɗi kuma Ministan Tsare-tsaren Tattalin Arziki na Ƙasa, Mista Wale Edun, ya tafi ƙasar Birtaniya domin samun kulawar likitoci, bayan ya yi rashin lafiya a kwanakin baya. Majiyoyi da dama daga fadar gwamnati sun tabbatar da hakan da safiyar Talata, inda suka bayyana cewa ministan ya bar Abuja zuwa Legas da daddare, daga nan kuma ya wuce Landan ta jirgin British Airways.

    Tun a ranar Lahadi, wasu jami’an gwamnati sun bayyana cewa Edun na karɓar magani a gidansa a Abuja karkashin kulawar likitocin Najeriya, suna mai ƙaryata jita-jitar cewa ya kamu da ciwon bugun jini. Sai dai daga baya, likitoci sun ba da shawarar a kai shi ƙasashen waje don ci gaba da jinya, wanda aka aiwatar a yanzu.

    Wani babban jami’in gwamnati ya tabbatar da cewa Edun na fama da rashin lafiya mai ɗan tsanani amma ba ciwon da zai hana shi aiki gaba ɗaya ba. Haka kuma, mai ba Shugaban Ƙasa shawara kan harkokin labarai, Bayo Onanuga, ya tabbatar da cewa Edun ba zai iya halartar taron shekara-shekara na Bankin Duniya da IMF da ke Washington, D.C. ba. Gwamnan Babban Bankin Najeriya, Olayemi Cardoso, ne zai jagoranci tawagar ƙasar.

    Edun, wanda aka naɗa a watan Agustan 2023, ya taka muhimmiyar rawa wajen aiwatar da manufofin tattalin arzikin gwamnatin Tinubu, ciki har da cire tallafin mai da daidaita farashin musayar kuɗi. Har yanzu Ma’aikatar Kuɗi ba ta fitar da wata sanarwa ta hukuma kan halin da ministan ke ciki ba.

    Birtaniya
    Share. Facebook Twitter WhatsApp Telegram
    Previous ArticleGwamna Mbah Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP Zuwa APC
    Next Article Za a Samu Ƙarancin Wutar Lantarki Na Tsawon Kwanaki 10 a Gombe – TCN
    Abbass Abdurrahman
    • Website

    Related Posts

    Featured

    Matatar Dangote Ta Ƙara Farashin Man Fetur

    March 3, 2026
    Featured

    Doguwa Ya Yi Murabus Daga Muƙamin Kwamishinan Ruwa Na Kano

    March 3, 2026
    Featured

    Amurka Na Da Isassun Makaman Yaƙi Da Za a Iya Amfani Da Su “Har Abada” – Trump 

    March 3, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    SABBIN LABARAI

    Gwamnatin Kano Ta Dakatar da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi

    October 1, 202544 Views

    Kotu Ta Yankewa Tsohon Firayim Ministan Mali Hukuncin Zaman Gidan Yari Sakamakon Rubutu a Shafin Sada Zumunta

    October 27, 202541 Views

    Dantawaye Ya Zama Sabon Kwamishinan Ƴansanda a Abuja

    October 17, 202532 Views

    NAFDAC Ta Yi Gargaɗi Kan Wani Kororon Roba Me Matuƙar Haɗari Ga Lafiya

    December 30, 202527 Views

    An Gano Motar Ofishin Mataimakin Gwamna Da Aka Sace

    November 12, 202527 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    • Telegram
    © 2026 Bechi Hausa News. Developed by: ENGRMKS & CO.
    • Shafin Farko
    • Game da Mu
    • Ƙarin Bayani
    • Manufar Sirri
    • Ka’idoji da Sharudda
    • Tuntuɓe Mu

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.