Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    • Shafin Farko
    • Labarai

      Iran Ta Naɗa Ayatollah Arafi A Matsayin Jagoran Addini Na Riƙo

      March 1, 2026

      Majalisar Dattawa Ta Sha Alwashin Amincewa da Dokar Kafa ‘Yan Sandan Jihohi Kafin Ƙarshen 2026

      March 1, 2026

      Iran Ta Ayyana Zaman Makoki na Kwanaki 40 Bayan Mutuwar Jagora Ayatoullah Khamenei 

      March 1, 2026

      Mutum 40 Sun Mutu a Harin da Aka Kai Makarantar Ƴanmata a Iran

      February 28, 2026

      Iran Ta Sha Alwashin Kare Kanta Daga Hare-haren Amurka da Isra’ila

      February 28, 2026
    • Siyasa

      Gwamnan Adamawa Ya Sauya Sheƙa Zuwa APC

      February 27, 2026

      NDLEA Ta Kama Wata Mata Mai Cikin Bogi Ɗauke da Hodar Iblis a Iyakar Seme

      February 22, 2026

      Jam’iyyun Adawa Sun Kaurace wa Zaɓen Kano, APC Ta Lashe Kujerun Majalisa a Rivers

      February 22, 2026

      Kotu Ta Umarci INEC Ta Yi Wa Jam’iyyar NDP Rajista

      February 19, 2026

      Gwamnan Zamfara Ya Zargi Gwamnatin Tarayya da Nuna Masa Wariya Saboda Bambancin Jam’iyya

      February 18, 2026
    • Addini

      Bauchi Ta neman ƙarin Kujerun Hajji Daga Saudiyya

      February 16, 2026

      Sarkin Musulmi Ya Umarci Ƴan Najeriya Su Fara Duban Jinjirin Watan Ramadan Ranar Talata

      February 16, 2026

      Tinubu Ya Naɗa Ambasada Ismail Abba Yusuf a Matsayin Sabon Shugaban NAHCON

      February 11, 2026

      Sheikh Usman Kusfa Zaria (Rigi-rigi) Ya Rasu

      February 2, 2026

      Jigawa Ta Fara Gwajin Lafiya ga Maniyyatan Hajjin 2026

      January 28, 2026
    • Nishadi

      Oculus Founder Makes a VR Headset That Can Literally Kill You

      January 13, 2021
      85

      Braun Series 7 Electric Shaver Review: Quality at a Good Price

      January 13, 2021
      85

      Google Pixel 7, iPhone 14 Compared: Check Out 5 Major Differences

      January 13, 2021

      Why Apple Should Skip The MacBook Pro Launch

      January 12, 2021

      Apollo G2J Showcases Electric Sports Car

      January 12, 2021
    • Tsaro

      Ba a Fasa Bututun Mai Ko Ɗaya a Niger Delta a 2025 Ba – Sojoj

      January 20, 2026

      Sojojin Najeriya Sun Ƙwato lita 290,000 Na Man Fetur a Yankin Neja Delta

      October 21, 2025

      Ƴan Bindiga Sun Ƙwace Wayoyin Ƴan Sanda a Zamfara

      October 2, 2025

      Gwamnan Kano Ya Buƙaci Tinubu Ya Tsige Kwamishinan Ƴan Sandan Jihar

      October 1, 2025

      Will Using a VPN on Phone Helps Protect You from Ransomware?

      January 14, 2021
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    Home » PDP Zata Wargaje Matuƙar Aka Daina Shawara Da Ni – Wike
    Featured

    PDP Zata Wargaje Matuƙar Aka Daina Shawara Da Ni – Wike

    Abbass AbdurrahmanBy Abbass AbdurrahmanOctober 25, 2025No Comments2 Mins Read

    Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya yi gargaɗin cewa jam’iyyar PDP za ta lalace idan gwamnoninta suka ci gaba da watsi da shi daga muhimman shawarwarin jam’iyyar. Yayin wata tattaunawa da manema labarai a Abuja, Wike ya bayyana takaicinsa kan yadda ake ware shi daga tattaunawa da yanke shawara, duk da irin rawar da ya taka wajen gina jam’iyyar.

    Wike ya ce ba wai jam’iyyar APC bace ke haddasa matsalolin PDP ba, illa dai kuskuren da shugabannin jam’iyyar ke yi da kansu. Ya yi zargin cewa wasu gwamnonin jam’iyyar suna son mamaye harkokin PDP ta hanyar amfani da kuɗaɗen gwamnati, abin da ya kira “hanyar lalata jam’iyyar daga ciki.” Ya kuma bayyana cewa idan aka shirya babban taron jam’iyyar ba bisa ka’ida ba, to ba zai halarta ba, sai dai idan an bi doka da tsarin jam’iyya.

    A gefe guda, Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya kira ‘ya’yan jam’iyyar da su hada kai don sake gina PDP a gabannin babban taron jam’iyyar da za a gudanar a Ibadan a watan Nuwamba. Ya ce duk da matsalolin da jam’iyyar ke fuskanta, PDP na da damar dawo da mulki a 2027 idan shugabanninta suka fifita hadin kai da gaskiya a kan son zuciya.

    Sai dai a yankin Arewa maso Yamma, wasu dattawan PDP sun zargi Ministan Tsaron Ƙasa, Mohammed Bello Matawalle, da tilasta wa magoya bayan PDP komawa jam’iyyar APC ta hanyar amfani da mukamai da dukiya. Sun ce wannan lamari na iya lalata tsarin dimokuraɗiyya da kuma raunana jam’iyyar adawa a shiyyar Arewa maso Yamma, suna roƙon Shugaba Bola Tinubu da ya ja kunnen ministan.

    APC Bello Matawalle Bola Ahmed Tinubu Nyesom Wike PAdp Zamfara
    Share. Facebook Twitter WhatsApp Telegram
    Previous ArticleƳan Sanda Sun Kama Ƴan Ta’adda 10 a Neja
    Next Article Gwamnonin PDP Sun Zaɓi Tanimu Turaki a Matsayin Ɗan Takararsu a Zaɓen Shugabancin Jam’iyya
    Abbass Abdurrahman
    • Website

    Related Posts

    Featured

    Iran Ta Naɗa Ayatollah Arafi A Matsayin Jagoran Addini Na Riƙo

    March 1, 2026
    Featured

    Majalisar Dattawa Ta Sha Alwashin Amincewa da Dokar Kafa ‘Yan Sandan Jihohi Kafin Ƙarshen 2026

    March 1, 2026
    Featured

    Iran Ta Ayyana Zaman Makoki na Kwanaki 40 Bayan Mutuwar Jagora Ayatoullah Khamenei 

    March 1, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    SABBIN LABARAI

    Gwamnatin Kano Ta Dakatar da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi

    October 1, 202543 Views

    Kotu Ta Yankewa Tsohon Firayim Ministan Mali Hukuncin Zaman Gidan Yari Sakamakon Rubutu a Shafin Sada Zumunta

    October 27, 202541 Views

    Dantawaye Ya Zama Sabon Kwamishinan Ƴansanda a Abuja

    October 17, 202532 Views

    NAFDAC Ta Yi Gargaɗi Kan Wani Kororon Roba Me Matuƙar Haɗari Ga Lafiya

    December 30, 202527 Views

    An Gano Motar Ofishin Mataimakin Gwamna Da Aka Sace

    November 12, 202527 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    • Telegram
    © 2026 Bechi Hausa News. Developed by: ENGRMKS & CO.
    • Shafin Farko
    • Game da Mu
    • Ƙarin Bayani
    • Manufar Sirri
    • Ka’idoji da Sharudda
    • Tuntuɓe Mu

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.