Akalla mutane biyu ne aka tabbatar sun mutu yayin da wasu takwas suka jikkata sakamakon harin da mayakan Boko Haram suka kai a garin Geidam, hedikwatar Karamar Hukumar Geidam a Jihar Yobe. Maharan sun kutsa cikin garin ne da misalin karfe 8:00 na daren Litinin inda suka kai hari a sansanin ‘yan sa-kai da ke Fanfon Nuri.
Majiyoyi da dama sun shaida cewa maharan sun kashe wani dan sa-kai nan take tare da harbe wani farar hula da ke kasuwar Fanfon Nuri yana sayayya. An ce sun ajiye motocinsu a cikin daji domin su shigo cikin garin ba tare da an lura da su ba, lamarin da ya sa suka yi illa sosai.
Sai dai wata majiya ta ce farar hular bai mutu kai tsaye ta harbin maharan ba, illa dai ya rasu ne sakamakon turmutsitsin da ya biyo bayan harin. Kokarin jin ta bakin jami’in hulda da jama’a na rundunar Operation Hadin Kai, Sashen 2 da ke Damaturu, bai yi nasara ba zuwa lokacin hada wannan rahoto.

