Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    • Shafin Farko
    • Labarai

      Gwamnatin Kano Ta Shiryawa Ƴan Jaridar Yanar Gizo Horo Na Yini Biyu a Jigawa

      January 15, 2026

      Tanka Ta Murƙushe Mutane 5 a Gombe

      January 12, 2026

      Babu Siyasa a Binciken Da Ake Yi Wa Malami – EFCC

      January 12, 2026

      Ƴan Bindiga Sun Kashe Soja Da Jam’in NSCDC a Benue

      January 12, 2026

      Manyan Jiga-jigan APC 3 a Kogi Sun Mutu

      January 12, 2026
    • Siyasa

      Manyan Jiga-jigan APC 3 a Kogi Sun Mutu

      January 12, 2026

      Ganduje Zai Gana Da Masu Ruwa-da-tsaki Na APC

      January 11, 2026

      Datti Baba-Ahmed Ya Musanta Batun Tsayawa Takarar Shugaban Ƙasa

      January 9, 2026

      Fubara Barazana Ne Ga Demokaraɗiyya – Kakakin Majalisar Rivers

      January 9, 2026

      Kotu Ta Ƙi Bayar da Belin Kwamishinan Kuɗi Na Bauchi

      January 6, 2026
    • Addini

      Kano: Hisbah Ta Karɓi Ƙorafe-Ƙorafe Sama da 12,000 a 2025

      January 2, 2026

      Da Ɗumi-ɗumi : Sheikh Dahiru Bauchi Ya rasu

      November 27, 2025

      Zakaran Gwajin Dafi : Hajji 2025 Karkashin Farfesa Saleh Pakistan  

      November 24, 2025

      Hajji Da Shugabanci Nagari Ƙarƙashin Jagorancin Farfesa Pakistan

      November 17, 2025

      Hukumar NAHCON Ta Sanar Da Rage Kudin Aikin Hajjin 2026

      November 10, 2025
    • Nishadi

      Oculus Founder Makes a VR Headset That Can Literally Kill You

      January 13, 2021
      85

      Braun Series 7 Electric Shaver Review: Quality at a Good Price

      January 13, 2021
      85

      Google Pixel 7, iPhone 14 Compared: Check Out 5 Major Differences

      January 13, 2021

      Why Apple Should Skip The MacBook Pro Launch

      January 12, 2021

      Apollo G2J Showcases Electric Sports Car

      January 12, 2021
    • Tsaro

      Sojojin Najeriya Sun Ƙwato lita 290,000 Na Man Fetur a Yankin Neja Delta

      October 21, 2025

      Ƴan Bindiga Sun Ƙwace Wayoyin Ƴan Sanda a Zamfara

      October 2, 2025

      Gwamnan Kano Ya Buƙaci Tinubu Ya Tsige Kwamishinan Ƴan Sandan Jihar

      October 1, 2025

      Will Using a VPN on Phone Helps Protect You from Ransomware?

      January 14, 2021

      Popular New Xbox Game Pass Game Being Review Bombed With “0s”

      January 14, 2021
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    Home » Najeriya Za Ta Iya Samun Naira Tiriliyan Ɗaya Duk Shekara a Sabon Tsarin Haraji – Bincike
    Featured

    Najeriya Za Ta Iya Samun Naira Tiriliyan Ɗaya Duk Shekara a Sabon Tsarin Haraji – Bincike

    Abbass AbdurrahmanBy Abbass AbdurrahmanOctober 6, 2025No Comments2 Mins Read

    Gwamnatin Najeriya na iya samun har Naira tiriliyan ɗaya duk shekara daga sabon harajin ribar jarin (CGT) na kashi 30% da ake shirin fara aiwatarwa a Janairu 2026. A shekarar 2024 an samu ribar da ta kai kusan N956.2 biliyan daga cinikin hannayen jari na N2.8 tiriliyan, wanda harajin zai bayar da N286.8 biliyan. A rabin farkon 2025 kuwa, an kai ciniki na N4.19 tiriliyan, wanda ke nuna yiwuwar samun harajin kusan N995 biliyan idan kasuwa ta ci gaba da wannan hanzari.

    Sai dai masana harkokin kasuwa sun gargadi cewa irin wannan babban kaso na haraji zai iya rage kwarin gwiwar masu zuba jari, musamman manyan kamfanoni da masu hannun jari na waje. Sun ce tsarin zai iya janyo fitar jarin kasashen waje (capital flight) zuwa kasuwannin da ke da rangwamen haraji, kamar Kenya da ke da 0%, Ghana 15%, da Morocco 10%, yayin da Masar ma ta soke nata harajin. Wannan bambanci na iya rage sha’awar zuba jari a kasuwar hannayen jarin Najeriya.

    Haka kuma, masana kamar Patrick Ajudua da Amaechi Egbo sun nuna damuwa kan rashin tsayayyen bayani a cikin dokar — musamman yadda za a tantance sake zuba jari da yiwuwar a dora haraji kan ribar da aka tara kafin dokar ta fara aiki. Sun bayyana hakan a matsayin rashin adalci da zai iya rage amincewar masu zuba jari da sa kasuwar ta zama mara tabbas.

    David Adonri na Highcap Securities ya bayyana harajin a matsayin mataki da zai iya rage cinikayya, raunana kasuwa da takura samun jarin dogon lokaci da ake bukata don farfado da tattalin arzikin Najeriya. Ya bukaci gwamnati ta sake nazarin tsarin, ta tsara shi cikin salo mai jawo jarin cikin gida da na waje, maimakon matakin da zai iya karya ci gaban kasuwar hannayen jari da ake kokarin ingantawa.

    CGT Najeriya
    Share. Facebook Twitter WhatsApp Telegram
    Previous ArticleFiraiministan Faransa Ya Yi Murabus Kwana Guda da Ƙaddamar da Majalisar Zartarwarsa
    Next Article Mutane 4,778 Ne Su Ka Mutu a Najeriya Sakamakon Cutar Kwalara – NCDC
    Abbass Abdurrahman
    • Website

    Related Posts

    Featured

    Gwamnatin Kano Ta Shiryawa Ƴan Jaridar Yanar Gizo Horo Na Yini Biyu a Jigawa

    January 15, 2026
    Featured

    Tanka Ta Murƙushe Mutane 5 a Gombe

    January 12, 2026
    Featured

    Babu Siyasa a Binciken Da Ake Yi Wa Malami – EFCC

    January 12, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    SABBIN LABARAI

    Gwamnatin Kano Ta Dakatar da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi

    October 1, 202543 Views

    Kotu Ta Yankewa Tsohon Firayim Ministan Mali Hukuncin Zaman Gidan Yari Sakamakon Rubutu a Shafin Sada Zumunta

    October 27, 202541 Views

    Dantawaye Ya Zama Sabon Kwamishinan Ƴansanda a Abuja

    October 17, 202532 Views

    An Gano Motar Ofishin Mataimakin Gwamna Da Aka Sace

    November 12, 202527 Views

    NAFDAC Ta Yi Gargaɗi Kan Wani Kororon Roba Me Matuƙar Haɗari Ga Lafiya

    December 30, 202525 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    • Telegram
    © 2026 Bechi Hausa News. Developed by: ENGRMKS & CO.
    • Shafin Farko
    • Game da Mu
    • Ƙarin Bayani
    • Manufar Sirri
    • Ka’idoji da Sharudda
    • Tuntuɓe Mu

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.