Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    • Shafin Farko
    • Labarai

      Ba Kama Gbajabiamila Muka Yi Ba Gayyatarsa Muka Yi – ICPC

      July 21, 2026

      Tinubu Ya Naɗa Sabbin Shugabanni Da Mambobi 26 a Hukumomi Da Kwamitocin Gwamnatin Tarayya

      July 21, 2026

      An Zargi Likitan El-Rufai Da Bayar da Rahoton Jinya Na Bogi

      July 21, 2026

      Guguwa Da Ruwan Sama Mai Ƙarfi Sun Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutane Huɗu a Sakkwato

      July 21, 2026

      Mamakon Ruwan Sama Ya Lalata Gidaje Da Gonaki a Filato

      July 20, 2026
    • Siyasa

      Kotu Ta Yi Watsi da Ƙarar da Tsagin Tanimu Turaki Suka Shigar Kan Rikicin Shugabancin PDP

      July 18, 2026

      Ya Kamata Majalisa Ta Yi Bincike Kan Ingancin Lafiyar Tinubu – ADC

      July 17, 2026

      Gwamna Yusuf Ya Zaɓi Garo a Matsayin Mataimakinsa a Zaɓen 2027

      July 13, 2026

      INEC Ta Ƙara Wa’adin Miƙa Sunayen ‘Yan Takarar Zaɓen 2027

      July 12, 2026

      Sauye-sauyen Gwamnatina Sun Inganta Ayyuka Da Tattalin Arziki a Kaduna – Gwamna Uba Sani 

      July 10, 2026
    • Addini

      An Rufe Birnin Tehran Domin Jana’izar Ayatollah Ali Khamenei

      July 1, 2026

      Kotu Ta Buƙaci a Gabatar Da Litattafan Da Sheikh Abduljabbar Ya Yi Amfani Da Su

      June 29, 2026

      NAHCON Ta Kammala Dawo Da Alhazan Najeriya Daga Saudiyya

      June 23, 2026

      Sarkin Musulmi Ya Buƙaci Hukumomi Su Gaggauta Ɗaukar Matakai Domin Magance Matsalar Tsaro

      June 17, 2026

      Gwamnatin Kano Za Ta Kashe Naira Biliyan 1.5 Domin Shirin ‘Auren Gata’

      June 15, 2026
    • Nishadi

      Oculus Founder Makes a VR Headset That Can Literally Kill You

      January 13, 2021
      85

      Braun Series 7 Electric Shaver Review: Quality at a Good Price

      January 13, 2021
      85

      Google Pixel 7, iPhone 14 Compared: Check Out 5 Major Differences

      January 13, 2021

      Why Apple Should Skip The MacBook Pro Launch

      January 12, 2021

      Apollo G2J Showcases Electric Sports Car

      January 12, 2021
    • Tsaro

      Sojoji Sun Kama Ƴan Ƙasashen Waje Da Ake Zargin Suna da Hannu a Matsalar Tsaron Najeriya – Bwala

      July 18, 2026

      ‘Yan Sanda Sun Fara Kwato Makaman Da Ke Hannun Jama’a Ba Bisa Ka’ida Ba – IGP Disu 

      July 17, 2026

      Sojoji Sun Gano Ƴan Ƙasashen Waje Uku Cikin Mayaƙan ISWAP a Borno

      July 13, 2026

      An Kashe Fitaccen Jagoran ‘Yan Bindiga Sani Yellow a Zamfara

      July 12, 2026

      Matasa a Borno Sun Gudanar Da Zanga-Zanga Kan Rashin Tsaro

      July 12, 2026
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    Home » Kashi 70% Na Matan Da Aka Yankewa Hukuncin Kisa a Najeriya Iyaye Ne- Bincike
    Featured

    Kashi 70% Na Matan Da Aka Yankewa Hukuncin Kisa a Najeriya Iyaye Ne- Bincike

    Abbass AbdurrahmanBy Abbass AbdurrahmanOctober 14, 2025No Comments2 Mins Read

    Wani sabon bincike ya gano cewa yawancin mata da ke fuskantar hukuncin kisa a Najeriya iyaye ne, kuma masu fama da talauci, rashin ilimi. Binciken wanda aka gabatar a taron tabbatar da sakamako a Abuja ranar Litinin, an gudanar da shi ne ta Hope Behind Bars Africa tare da hadin gwiwar Hukumar Kare Hakkokin Dan Adam ta Kasa (NHRC) da tallafin World Coalition Against the Death Penalty da French Development Agency.

    Rahoton ya nuna cewa kashi 47% na matan da aka yankewa hukuncin kisa su na tsakanin shekaru 18 zuwa 35, yayin da fiye da kashi ɗaya bisa uku ba su da ilimi kwata-kwata, sai kuma kashi 10% kacal suka kai matakin gaba. Haka kuma, kashi 70% daga cikinsu iyaye ne da suka bar ‘ya’yansu cikin mawuyacin hali da rashin kulawa, abin da ke kara tsananta matsalolin zamantakewa ga iyalansu. Yawancinsu sun taba fuskantar cin zarafi kamar auren dole da dukan aure.

    Binciken ya kuma nuna cewa kashi 75% daga cikin matan ba su san dokar da aka gurfanar da su a karkashinta ba, yayin da kashi 85% suka ce tsarin dokokin ya nuna wariya ga mata. Fiye da rabin matan sun bayyana cewa shari’unsu ba su kasance a bude ba, kuma tsarin shari’a mai rinjayen maza ya shafi sakamakon shari’unsu. Haka kuma, yawanci sun fuskanci tsangwama da kin amincewa daga mazajensu da al’ummarsu bayan gurfanar da su, musamman a shari’o’in da suka shafi zina ko laifukan jima’i.

    Shugaban NHRC, Dr. Tony Ojukwu (SAN), ya yi kira da a aiwatar da sauye-sauye cikin gaggawa tare da jaddada matsayinsu na adawa da hukuncin kisa. Ya bayyana hukuncin kisa a matsayin mataki da bai dace da tsarin kare hakkin dan Adam ba kuma bai rage laifuka yadda ake zato ba. Rahoton ya ba da shawarwari da suka hada da kafa moratorium kan aiwatar da hukuncin kisa, yin gyare-gyaren dokoki masu la’akari da jinsi, bunkasa tallafin shari’a da inganta yanayin zaman kurkuku. Wannan bincike ya zo ne a lokacin bikin Ranar Duniya ta Adawa da Hukuncin Kisa, wanda ake gudanarwa a duk shekara ranar 10 ga Oktoba.

    Najeriya
    Share. Facebook Twitter WhatsApp Telegram
    Previous ArticleJam’iyyar PDP Ta Ɗage Taron Majalisar Zartarwa Na Ƙasa
    Next Article Matsin Rayuwa Da Ƴan Najeriya Ke Fuskanta Ya Kusa Zuwa Ƙarshe – Shettima
    Abbass Abdurrahman
    • Website

    Related Posts

    Featured

    Ba Kama Gbajabiamila Muka Yi Ba Gayyatarsa Muka Yi – ICPC

    July 21, 2026
    Featured

    Tinubu Ya Naɗa Sabbin Shugabanni Da Mambobi 26 a Hukumomi Da Kwamitocin Gwamnatin Tarayya

    July 21, 2026
    Featured

    An Zargi Likitan El-Rufai Da Bayar da Rahoton Jinya Na Bogi

    July 21, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    SABBIN LABARAI

    Ba Don Gudunmawar Masu Yiwa Ƙasa Hidima Ba Da Jihohi Dayawa Basu Kai Yadda Suke a Yanzu Ba – Minista

    December 8, 2025150 Views

    Sabon Rikici Ya Kunno Kai a NDC : Ƴan Takara Sun Kai Ƙara Kan Zaɓen Fidda-gwani a Kano

    June 30, 202679 Views

    Gwamnatin Kano Ta Dakatar da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi

    October 1, 202546 Views

    Kotu Ta Yankewa Tsohon Firayim Ministan Mali Hukuncin Zaman Gidan Yari Sakamakon Rubutu a Shafin Sada Zumunta

    October 27, 202541 Views

    Dantawaye Ya Zama Sabon Kwamishinan Ƴansanda a Abuja

    October 17, 202533 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    • Telegram
    © 2026 Bechi Hausa News. Developed by: ENGRMKS & CO.
    • Shafin Farko
    • Game da Mu
    • Ƙarin Bayani
    • Manufar Sirri
    • Ka’idoji da Sharudda
    • Tuntuɓe Mu

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.