Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    • Shafin Farko
    • Labarai

      Gwamnatin Kano Ta Shiryawa Ƴan Jaridar Yanar Gizo Horo Na Yini Biyu a Jigawa

      January 15, 2026

      Tanka Ta Murƙushe Mutane 5 a Gombe

      January 12, 2026

      Babu Siyasa a Binciken Da Ake Yi Wa Malami – EFCC

      January 12, 2026

      Ƴan Bindiga Sun Kashe Soja Da Jam’in NSCDC a Benue

      January 12, 2026

      Manyan Jiga-jigan APC 3 a Kogi Sun Mutu

      January 12, 2026
    • Siyasa

      Manyan Jiga-jigan APC 3 a Kogi Sun Mutu

      January 12, 2026

      Ganduje Zai Gana Da Masu Ruwa-da-tsaki Na APC

      January 11, 2026

      Datti Baba-Ahmed Ya Musanta Batun Tsayawa Takarar Shugaban Ƙasa

      January 9, 2026

      Fubara Barazana Ne Ga Demokaraɗiyya – Kakakin Majalisar Rivers

      January 9, 2026

      Kotu Ta Ƙi Bayar da Belin Kwamishinan Kuɗi Na Bauchi

      January 6, 2026
    • Addini

      Kano: Hisbah Ta Karɓi Ƙorafe-Ƙorafe Sama da 12,000 a 2025

      January 2, 2026

      Da Ɗumi-ɗumi : Sheikh Dahiru Bauchi Ya rasu

      November 27, 2025

      Zakaran Gwajin Dafi : Hajji 2025 Karkashin Farfesa Saleh Pakistan  

      November 24, 2025

      Hajji Da Shugabanci Nagari Ƙarƙashin Jagorancin Farfesa Pakistan

      November 17, 2025

      Hukumar NAHCON Ta Sanar Da Rage Kudin Aikin Hajjin 2026

      November 10, 2025
    • Nishadi

      Oculus Founder Makes a VR Headset That Can Literally Kill You

      January 13, 2021
      85

      Braun Series 7 Electric Shaver Review: Quality at a Good Price

      January 13, 2021
      85

      Google Pixel 7, iPhone 14 Compared: Check Out 5 Major Differences

      January 13, 2021

      Why Apple Should Skip The MacBook Pro Launch

      January 12, 2021

      Apollo G2J Showcases Electric Sports Car

      January 12, 2021
    • Tsaro

      Sojojin Najeriya Sun Ƙwato lita 290,000 Na Man Fetur a Yankin Neja Delta

      October 21, 2025

      Ƴan Bindiga Sun Ƙwace Wayoyin Ƴan Sanda a Zamfara

      October 2, 2025

      Gwamnan Kano Ya Buƙaci Tinubu Ya Tsige Kwamishinan Ƴan Sandan Jihar

      October 1, 2025

      Will Using a VPN on Phone Helps Protect You from Ransomware?

      January 14, 2021

      Popular New Xbox Game Pass Game Being Review Bombed With “0s”

      January 14, 2021
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    Home » Kashi 70% Na Matan Da Aka Yankewa Hukuncin Kisa a Najeriya Iyaye Ne- Bincike
    Featured

    Kashi 70% Na Matan Da Aka Yankewa Hukuncin Kisa a Najeriya Iyaye Ne- Bincike

    Abbass AbdurrahmanBy Abbass AbdurrahmanOctober 14, 2025No Comments2 Mins Read

    Wani sabon bincike ya gano cewa yawancin mata da ke fuskantar hukuncin kisa a Najeriya iyaye ne, kuma masu fama da talauci, rashin ilimi. Binciken wanda aka gabatar a taron tabbatar da sakamako a Abuja ranar Litinin, an gudanar da shi ne ta Hope Behind Bars Africa tare da hadin gwiwar Hukumar Kare Hakkokin Dan Adam ta Kasa (NHRC) da tallafin World Coalition Against the Death Penalty da French Development Agency.

    Rahoton ya nuna cewa kashi 47% na matan da aka yankewa hukuncin kisa su na tsakanin shekaru 18 zuwa 35, yayin da fiye da kashi ɗaya bisa uku ba su da ilimi kwata-kwata, sai kuma kashi 10% kacal suka kai matakin gaba. Haka kuma, kashi 70% daga cikinsu iyaye ne da suka bar ‘ya’yansu cikin mawuyacin hali da rashin kulawa, abin da ke kara tsananta matsalolin zamantakewa ga iyalansu. Yawancinsu sun taba fuskantar cin zarafi kamar auren dole da dukan aure.

    Binciken ya kuma nuna cewa kashi 75% daga cikin matan ba su san dokar da aka gurfanar da su a karkashinta ba, yayin da kashi 85% suka ce tsarin dokokin ya nuna wariya ga mata. Fiye da rabin matan sun bayyana cewa shari’unsu ba su kasance a bude ba, kuma tsarin shari’a mai rinjayen maza ya shafi sakamakon shari’unsu. Haka kuma, yawanci sun fuskanci tsangwama da kin amincewa daga mazajensu da al’ummarsu bayan gurfanar da su, musamman a shari’o’in da suka shafi zina ko laifukan jima’i.

    Shugaban NHRC, Dr. Tony Ojukwu (SAN), ya yi kira da a aiwatar da sauye-sauye cikin gaggawa tare da jaddada matsayinsu na adawa da hukuncin kisa. Ya bayyana hukuncin kisa a matsayin mataki da bai dace da tsarin kare hakkin dan Adam ba kuma bai rage laifuka yadda ake zato ba. Rahoton ya ba da shawarwari da suka hada da kafa moratorium kan aiwatar da hukuncin kisa, yin gyare-gyaren dokoki masu la’akari da jinsi, bunkasa tallafin shari’a da inganta yanayin zaman kurkuku. Wannan bincike ya zo ne a lokacin bikin Ranar Duniya ta Adawa da Hukuncin Kisa, wanda ake gudanarwa a duk shekara ranar 10 ga Oktoba.

    Najeriya
    Share. Facebook Twitter WhatsApp Telegram
    Previous ArticleJam’iyyar PDP Ta Ɗage Taron Majalisar Zartarwa Na Ƙasa
    Next Article Matsin Rayuwa Da Ƴan Najeriya Ke Fuskanta Ya Kusa Zuwa Ƙarshe – Shettima
    Abbass Abdurrahman
    • Website

    Related Posts

    Featured

    Gwamnatin Kano Ta Shiryawa Ƴan Jaridar Yanar Gizo Horo Na Yini Biyu a Jigawa

    January 15, 2026
    Featured

    Tanka Ta Murƙushe Mutane 5 a Gombe

    January 12, 2026
    Featured

    Babu Siyasa a Binciken Da Ake Yi Wa Malami – EFCC

    January 12, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    SABBIN LABARAI

    Gwamnatin Kano Ta Dakatar da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi

    October 1, 202542 Views

    Kotu Ta Yankewa Tsohon Firayim Ministan Mali Hukuncin Zaman Gidan Yari Sakamakon Rubutu a Shafin Sada Zumunta

    October 27, 202541 Views

    Dantawaye Ya Zama Sabon Kwamishinan Ƴansanda a Abuja

    October 17, 202532 Views

    An Gano Motar Ofishin Mataimakin Gwamna Da Aka Sace

    November 12, 202527 Views

    NAFDAC Ta Yi Gargaɗi Kan Wani Kororon Roba Me Matuƙar Haɗari Ga Lafiya

    December 30, 202525 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    • Telegram
    © 2026 Bechi Hausa News. Developed by: ENGRMKS & CO.
    • Shafin Farko
    • Game da Mu
    • Ƙarin Bayani
    • Manufar Sirri
    • Ka’idoji da Sharudda
    • Tuntuɓe Mu

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.