Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    • Shafin Farko
    • Labarai

      Ba Za Mu Bayar da Tabbacin Sahihin Zaɓe a 2027 Ba – Amupitan

      March 2, 2026

      Jirage Marasa Matuƙa Sun Kai Hari Matatar Man Saudiyya

      March 2, 2026

      Najeriya Ta Buƙaci a Kawo Karshen Rikicin Gabas ta Tsakiya

      March 2, 2026

      Iran Ta Naɗa Ayatollah Arafi A Matsayin Jagoran Addini Na Riƙo

      March 1, 2026

      Majalisar Dattawa Ta Sha Alwashin Amincewa da Dokar Kafa ‘Yan Sandan Jihohi Kafin Ƙarshen 2026

      March 1, 2026
    • Siyasa

      Gwamnan Adamawa Ya Sauya Sheƙa Zuwa APC

      February 27, 2026

      NDLEA Ta Kama Wata Mata Mai Cikin Bogi Ɗauke da Hodar Iblis a Iyakar Seme

      February 22, 2026

      Jam’iyyun Adawa Sun Kaurace wa Zaɓen Kano, APC Ta Lashe Kujerun Majalisa a Rivers

      February 22, 2026

      Kotu Ta Umarci INEC Ta Yi Wa Jam’iyyar NDP Rajista

      February 19, 2026

      Gwamnan Zamfara Ya Zargi Gwamnatin Tarayya da Nuna Masa Wariya Saboda Bambancin Jam’iyya

      February 18, 2026
    • Addini

      Bauchi Ta neman ƙarin Kujerun Hajji Daga Saudiyya

      February 16, 2026

      Sarkin Musulmi Ya Umarci Ƴan Najeriya Su Fara Duban Jinjirin Watan Ramadan Ranar Talata

      February 16, 2026

      Tinubu Ya Naɗa Ambasada Ismail Abba Yusuf a Matsayin Sabon Shugaban NAHCON

      February 11, 2026

      Sheikh Usman Kusfa Zaria (Rigi-rigi) Ya Rasu

      February 2, 2026

      Jigawa Ta Fara Gwajin Lafiya ga Maniyyatan Hajjin 2026

      January 28, 2026
    • Nishadi

      Oculus Founder Makes a VR Headset That Can Literally Kill You

      January 13, 2021
      85

      Braun Series 7 Electric Shaver Review: Quality at a Good Price

      January 13, 2021
      85

      Google Pixel 7, iPhone 14 Compared: Check Out 5 Major Differences

      January 13, 2021

      Why Apple Should Skip The MacBook Pro Launch

      January 12, 2021

      Apollo G2J Showcases Electric Sports Car

      January 12, 2021
    • Tsaro

      Ba a Fasa Bututun Mai Ko Ɗaya a Niger Delta a 2025 Ba – Sojoj

      January 20, 2026

      Sojojin Najeriya Sun Ƙwato lita 290,000 Na Man Fetur a Yankin Neja Delta

      October 21, 2025

      Ƴan Bindiga Sun Ƙwace Wayoyin Ƴan Sanda a Zamfara

      October 2, 2025

      Gwamnan Kano Ya Buƙaci Tinubu Ya Tsige Kwamishinan Ƴan Sandan Jihar

      October 1, 2025

      Will Using a VPN on Phone Helps Protect You from Ransomware?

      January 14, 2021
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    Home » Ƴan Sanda Sun Kama Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Shanu a Jigawa
    Featured

    Ƴan Sanda Sun Kama Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Shanu a Jigawa

    Abbass AbdurrahmanBy Abbass AbdurrahmanNovember 2, 2025No Comments2 Mins Read

    Rundunar ‘Yan sandan Jihar Jigawa ta kama mutane 10 da ake zargi da satar shanu, tumaki da kuma babur, wanda kimarsu ta kai sama da naira dubu 570,000 a yayin wani samame da aka gudanar don dakile ayyukan masu satar dabbobi a jihar. Mai magana da yawun rundunar, SP Shi’isu Adam, ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da aka fitar a ranar Lahadi, inda ya ce kama waɗannan mutane na daga cikin matakan da rundunar ke ɗauka wajen rage laifuka a yankin.

    A cewar SP Adam, an kama wasu daga cikin masu laifin ne a ranar 22 ga Oktoba bayan samun kiran gaggawa daga al’umma game da satar dabba a yankin Balangu. Masu laifin sun haɗa da Muhd Jafaru, Gidare Kansila, Dare Kabo, Buba Umaru da Manu Musa, waɗanda ake zargi da haɗa kai wajen satar saniya ɗaya mai kimanin naira 450,000 da tumaki masu darajar naira 120,000. Rundunar ta ce an sami nasarar kwato dabbobin da aka sace kuma za a gurfanar da su a kotu nan ba da jimawa ba.

    Haka zalika, a ranar 27 ga Oktoba, jami’an sashen Takur Site sun cafke wani matashi mai suna Mubarak Nasir, ɗan shekara 23, wanda ake zargi da satar babur a Dutse. Bincike ya nuna cewa Nasir ya amsa laifinsa, kuma shari’arsa tana kan tafiya. A wani samame daban a ranar 28 ga Oktoba, rundunar ta Hadejia ta kama wasu maza biyu, Ado Manu da Ibrahim Audu, daga ƙaramar hukumar Kiri Kasamma, bayan an same su da saniya da ake zargi da sacewa daga wani kauye da ake kira Zagari.

    SP Shi’isu Adam ya tabbatar da cewa duk waɗanda aka kama za a gurfanar da su a gaban kotu bayan kammala bincike, tare da jaddada cewa rundunar ta ƙuduri aniyar kawar da satar dabbobi a fadin Jigawa. Ya kuma yi kira ga jama’a da su ci gaba da bayar da bayanai don taimaka wa jami’an tsaro wajen yaki da masu aikata laifi.

    Jigawa
    Share. Facebook Twitter WhatsApp Telegram
    Previous ArticleYan Bindiga Sun Kashe Mutum 17 a Kaduna da Filato
    Next Article Babu Wani Martani Da Na Yi Kan Kalaman Donald Trump – Akpabio
    Abbass Abdurrahman
    • Website

    Related Posts

    Featured

    Ba Za Mu Bayar da Tabbacin Sahihin Zaɓe a 2027 Ba – Amupitan

    March 2, 2026
    Featured

    Jirage Marasa Matuƙa Sun Kai Hari Matatar Man Saudiyya

    March 2, 2026
    Featured

    Najeriya Ta Buƙaci a Kawo Karshen Rikicin Gabas ta Tsakiya

    March 2, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    SABBIN LABARAI

    Gwamnatin Kano Ta Dakatar da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi

    October 1, 202543 Views

    Kotu Ta Yankewa Tsohon Firayim Ministan Mali Hukuncin Zaman Gidan Yari Sakamakon Rubutu a Shafin Sada Zumunta

    October 27, 202541 Views

    Dantawaye Ya Zama Sabon Kwamishinan Ƴansanda a Abuja

    October 17, 202532 Views

    NAFDAC Ta Yi Gargaɗi Kan Wani Kororon Roba Me Matuƙar Haɗari Ga Lafiya

    December 30, 202527 Views

    An Gano Motar Ofishin Mataimakin Gwamna Da Aka Sace

    November 12, 202527 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    • Telegram
    © 2026 Bechi Hausa News. Developed by: ENGRMKS & CO.
    • Shafin Farko
    • Game da Mu
    • Ƙarin Bayani
    • Manufar Sirri
    • Ka’idoji da Sharudda
    • Tuntuɓe Mu

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.