Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    • Shafin Farko
    • Labarai

      Gwamnatin Kano Ta Shiryawa Ƴan Jaridar Yanar Gizo Horo Na Yini Biyu a Jigawa

      January 15, 2026

      Tanka Ta Murƙushe Mutane 5 a Gombe

      January 12, 2026

      Babu Siyasa a Binciken Da Ake Yi Wa Malami – EFCC

      January 12, 2026

      Ƴan Bindiga Sun Kashe Soja Da Jam’in NSCDC a Benue

      January 12, 2026

      Manyan Jiga-jigan APC 3 a Kogi Sun Mutu

      January 12, 2026
    • Siyasa

      Manyan Jiga-jigan APC 3 a Kogi Sun Mutu

      January 12, 2026

      Ganduje Zai Gana Da Masu Ruwa-da-tsaki Na APC

      January 11, 2026

      Datti Baba-Ahmed Ya Musanta Batun Tsayawa Takarar Shugaban Ƙasa

      January 9, 2026

      Fubara Barazana Ne Ga Demokaraɗiyya – Kakakin Majalisar Rivers

      January 9, 2026

      Kotu Ta Ƙi Bayar da Belin Kwamishinan Kuɗi Na Bauchi

      January 6, 2026
    • Addini

      Kano: Hisbah Ta Karɓi Ƙorafe-Ƙorafe Sama da 12,000 a 2025

      January 2, 2026

      Da Ɗumi-ɗumi : Sheikh Dahiru Bauchi Ya rasu

      November 27, 2025

      Zakaran Gwajin Dafi : Hajji 2025 Karkashin Farfesa Saleh Pakistan  

      November 24, 2025

      Hajji Da Shugabanci Nagari Ƙarƙashin Jagorancin Farfesa Pakistan

      November 17, 2025

      Hukumar NAHCON Ta Sanar Da Rage Kudin Aikin Hajjin 2026

      November 10, 2025
    • Nishadi

      Oculus Founder Makes a VR Headset That Can Literally Kill You

      January 13, 2021
      85

      Braun Series 7 Electric Shaver Review: Quality at a Good Price

      January 13, 2021
      85

      Google Pixel 7, iPhone 14 Compared: Check Out 5 Major Differences

      January 13, 2021

      Why Apple Should Skip The MacBook Pro Launch

      January 12, 2021

      Apollo G2J Showcases Electric Sports Car

      January 12, 2021
    • Tsaro

      Sojojin Najeriya Sun Ƙwato lita 290,000 Na Man Fetur a Yankin Neja Delta

      October 21, 2025

      Ƴan Bindiga Sun Ƙwace Wayoyin Ƴan Sanda a Zamfara

      October 2, 2025

      Gwamnan Kano Ya Buƙaci Tinubu Ya Tsige Kwamishinan Ƴan Sandan Jihar

      October 1, 2025

      Will Using a VPN on Phone Helps Protect You from Ransomware?

      January 14, 2021

      Popular New Xbox Game Pass Game Being Review Bombed With “0s”

      January 14, 2021
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    Home » Cutar Zazzaɓin Lassa Ta Yi Ajalin Mutane 177 a Cikin Watanni 10 – NCDC
    Featured

    Cutar Zazzaɓin Lassa Ta Yi Ajalin Mutane 177 a Cikin Watanni 10 – NCDC

    Abbass AbdurrahmanBy Abbass AbdurrahmanNovember 21, 2025No Comments2 Mins Read

    21 ga Nuwamba 2025

    Najeriya ta sake fuskantar tashin hankali a fannin lafiya, inda Hukumar NCDC ta bayyana cewa mutane 177 sun riga mu gidan gaskiya sakamakon cutar Lassa daga watan Janairu zuwa farkon Nuwamba 2025. Rahoton mako na 44 ya nuna cewa an tabbatar da sabbin kamuwa 966 a jihohi 21 da kananan hukumomi 102, lamarin da ya daga yawan mace-mace zuwa kashi 18.3 cikin ɗari — wanda ya fi na bara.

    Rahoton ya nuna cewa sabbin kamuwa sun karu daga 11 a mako na 43 zuwa 12 a mako na 44, inda aka fi samun bullar cutar a Ondo, Edo da Benue. Jihohin da suka fi fuskantar kamuwa sun hada da Ondo da kashi 36%, Bauchi 21%, Edo 17% da Taraba 13%. Nau’in wadanda cutar ta fi shafa ya kasance masu shekaru 21–30, yayin da mafi ƙarancin shekaru da aka samu ya kasance shekara 1, mafi yawa kuma 96.

    NCDC ta ce babu wani sabon ma’aikacin lafiya da ya kamu a wannan mako, kuma kungiyar yaki da cutar Lassa mai kunshe da bangarori da dama na cigaba da jagorantar aikin dakile barkewar cutar a matakai daban-daban. Duk da cewa kamuwa ta ragu idan aka kwatanta da shekarar 2024, alkaluman mutuwa da ci gaba da yaduwar cutar na nuna kalubale a tsarin kare lafiya.

    Hukumar Lafiya ta Duniya WHO ta bayyana cewa cutar Lassa na yaduwa ne ta hanyar abinci ko kayan gida da berayen Mastomys suka gurɓata. Kasashe da dama a yammacin Afirka na fama da wannan cuta, lamarin da ke nuna bukatar karin matakan gaggawa da wayar da kai domin kare al’umma daga daya daga cikin cututtuka mafi hatsari a nahiyar.

    NCDC
    Share. Facebook Twitter WhatsApp Telegram
    Previous ArticleGwamna Bala Muhammad Ya Dakatar da Manyan Jami’an Gwamnati Guda Huɗu
    Next Article NDLEA Ta Cafke Mutane 230, Tare Da Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi a Kano
    Abbass Abdurrahman
    • Website

    Related Posts

    Featured

    Gwamnatin Kano Ta Shiryawa Ƴan Jaridar Yanar Gizo Horo Na Yini Biyu a Jigawa

    January 15, 2026
    Featured

    Tanka Ta Murƙushe Mutane 5 a Gombe

    January 12, 2026
    Featured

    Babu Siyasa a Binciken Da Ake Yi Wa Malami – EFCC

    January 12, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    SABBIN LABARAI

    Gwamnatin Kano Ta Dakatar da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi

    October 1, 202543 Views

    Kotu Ta Yankewa Tsohon Firayim Ministan Mali Hukuncin Zaman Gidan Yari Sakamakon Rubutu a Shafin Sada Zumunta

    October 27, 202541 Views

    Dantawaye Ya Zama Sabon Kwamishinan Ƴansanda a Abuja

    October 17, 202532 Views

    An Gano Motar Ofishin Mataimakin Gwamna Da Aka Sace

    November 12, 202527 Views

    NAFDAC Ta Yi Gargaɗi Kan Wani Kororon Roba Me Matuƙar Haɗari Ga Lafiya

    December 30, 202525 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    • Telegram
    © 2026 Bechi Hausa News. Developed by: ENGRMKS & CO.
    • Shafin Farko
    • Game da Mu
    • Ƙarin Bayani
    • Manufar Sirri
    • Ka’idoji da Sharudda
    • Tuntuɓe Mu

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.