Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    • Shafin Farko
    • Labarai

      Gwamnatin Kano Ta Shiryawa Ƴan Jaridar Yanar Gizo Horo Na Yini Biyu a Jigawa

      January 15, 2026

      Tanka Ta Murƙushe Mutane 5 a Gombe

      January 12, 2026

      Babu Siyasa a Binciken Da Ake Yi Wa Malami – EFCC

      January 12, 2026

      Ƴan Bindiga Sun Kashe Soja Da Jam’in NSCDC a Benue

      January 12, 2026

      Manyan Jiga-jigan APC 3 a Kogi Sun Mutu

      January 12, 2026
    • Siyasa

      Manyan Jiga-jigan APC 3 a Kogi Sun Mutu

      January 12, 2026

      Ganduje Zai Gana Da Masu Ruwa-da-tsaki Na APC

      January 11, 2026

      Datti Baba-Ahmed Ya Musanta Batun Tsayawa Takarar Shugaban Ƙasa

      January 9, 2026

      Fubara Barazana Ne Ga Demokaraɗiyya – Kakakin Majalisar Rivers

      January 9, 2026

      Kotu Ta Ƙi Bayar da Belin Kwamishinan Kuɗi Na Bauchi

      January 6, 2026
    • Addini

      Kano: Hisbah Ta Karɓi Ƙorafe-Ƙorafe Sama da 12,000 a 2025

      January 2, 2026

      Da Ɗumi-ɗumi : Sheikh Dahiru Bauchi Ya rasu

      November 27, 2025

      Zakaran Gwajin Dafi : Hajji 2025 Karkashin Farfesa Saleh Pakistan  

      November 24, 2025

      Hajji Da Shugabanci Nagari Ƙarƙashin Jagorancin Farfesa Pakistan

      November 17, 2025

      Hukumar NAHCON Ta Sanar Da Rage Kudin Aikin Hajjin 2026

      November 10, 2025
    • Nishadi

      Oculus Founder Makes a VR Headset That Can Literally Kill You

      January 13, 2021
      85

      Braun Series 7 Electric Shaver Review: Quality at a Good Price

      January 13, 2021
      85

      Google Pixel 7, iPhone 14 Compared: Check Out 5 Major Differences

      January 13, 2021

      Why Apple Should Skip The MacBook Pro Launch

      January 12, 2021

      Apollo G2J Showcases Electric Sports Car

      January 12, 2021
    • Tsaro

      Sojojin Najeriya Sun Ƙwato lita 290,000 Na Man Fetur a Yankin Neja Delta

      October 21, 2025

      Ƴan Bindiga Sun Ƙwace Wayoyin Ƴan Sanda a Zamfara

      October 2, 2025

      Gwamnan Kano Ya Buƙaci Tinubu Ya Tsige Kwamishinan Ƴan Sandan Jihar

      October 1, 2025

      Will Using a VPN on Phone Helps Protect You from Ransomware?

      January 14, 2021

      Popular New Xbox Game Pass Game Being Review Bombed With “0s”

      January 14, 2021
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    Home » NDLEA Ta Cafke Mutane 230, Tare Da Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi a Kano
    Featured

    NDLEA Ta Cafke Mutane 230, Tare Da Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi a Kano

    Abbass AbdurrahmanBy Abbass AbdurrahmanNovember 21, 2025No Comments2 Mins Read

    Hukumar NDLEA reshen Kano ta sanar da cafke mutane 230 da ake zargi da aikata manyan laifukan miyagun kwayoyi, tare da kwato tarin haramtattun abubuwa a fadin birnin Kano. An bayyana haka ne yayin wani taron manema labarai da aka gudanar a ranar Juma’a, wanda ya nuna samun gagarumar nasara a yakin da hukumomin tsaro ke yi da sha, safara da yawan laifukan da suka shafi kwayoyi.

    Kwamandan NDLEA na Kano, Abubakar Ahmad, ya ce sun gudanar da aikin tsawon kwanaki 30 ba tare da dakatawa ba tare da hadin gwiwar rundunar ‘yan sanda, NSCDC, NIS, NCoS da DSS a karkashin rundunar hadin guiwa ta Kano Joint Task Force for Peace Restoration and Youth Rehabilitation da Yusuf Mata ke jagoranta. Rundunar ta kai samame a wuraren da suka hada da Kofar Ruwa, Tashar Rami, Rijiyar Lemo, Kurna, Zage, Dorayi, Dawanau, Filin Idi, Rimi Market, Zango, Kano Line da Kofar Mata.

    Hukumar ta ce an kwato hodar cannabis, Exol-5, diazepam, “suck and die”, roba solution, maganin tari na codeine da kuma makamai na gargajiya. Ahmad ya yaba da rawar da kwamishinan ‘yan sanda, Ibrahim Bakori, ya taka wajen hada kai tsakanin hukumomin tsaro, tare da jinjinawa DSS bisa taimakon bayanan sirri da take bayarwa. Ya kuma gode wa gwamnatin Kano a karkashin Gwamna Abba Yusuf bisa goyon bayan yaki da tabarbarewar matasa.

    NDLEA ta jaddada cewa binciken ya rage yawan laifuka da suka shafi fashi da wayar hannu, ta’addanci na titi da sauran munanan dabi’u. Kwamandan ya roki iyaye da al’umma da su ci gaba da bada hadin kai domin tabbatar da cewa yaki da sha da safarar miyagun kwayoyi ya yi nasara a fadin jihar.

    NDLEA
    Share. Facebook Twitter WhatsApp Telegram
    Previous ArticleCutar Zazzaɓin Lassa Ta Yi Ajalin Mutane 177 a Cikin Watanni 10 – NCDC
    Next Article NNPP Chairman Hails Formation of Kano Online Media Chapel as Timely and Impactful
    Abbass Abdurrahman
    • Website

    Related Posts

    Featured

    Gwamnatin Kano Ta Shiryawa Ƴan Jaridar Yanar Gizo Horo Na Yini Biyu a Jigawa

    January 15, 2026
    Featured

    Tanka Ta Murƙushe Mutane 5 a Gombe

    January 12, 2026
    Featured

    Babu Siyasa a Binciken Da Ake Yi Wa Malami – EFCC

    January 12, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    SABBIN LABARAI

    Gwamnatin Kano Ta Dakatar da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi

    October 1, 202543 Views

    Kotu Ta Yankewa Tsohon Firayim Ministan Mali Hukuncin Zaman Gidan Yari Sakamakon Rubutu a Shafin Sada Zumunta

    October 27, 202541 Views

    Dantawaye Ya Zama Sabon Kwamishinan Ƴansanda a Abuja

    October 17, 202532 Views

    An Gano Motar Ofishin Mataimakin Gwamna Da Aka Sace

    November 12, 202527 Views

    NAFDAC Ta Yi Gargaɗi Kan Wani Kororon Roba Me Matuƙar Haɗari Ga Lafiya

    December 30, 202525 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    • Telegram
    © 2026 Bechi Hausa News. Developed by: ENGRMKS & CO.
    • Shafin Farko
    • Game da Mu
    • Ƙarin Bayani
    • Manufar Sirri
    • Ka’idoji da Sharudda
    • Tuntuɓe Mu

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.