Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    • Shafin Farko
    • Labarai

      Ba Za Mu Bayar da Tabbacin Sahihin Zaɓe a 2027 Ba – Amupitan

      March 2, 2026

      Jirage Marasa Matuƙa Sun Kai Hari Matatar Man Saudiyya

      March 2, 2026

      Najeriya Ta Buƙaci a Kawo Karshen Rikicin Gabas ta Tsakiya

      March 2, 2026

      Iran Ta Naɗa Ayatollah Arafi A Matsayin Jagoran Addini Na Riƙo

      March 1, 2026

      Majalisar Dattawa Ta Sha Alwashin Amincewa da Dokar Kafa ‘Yan Sandan Jihohi Kafin Ƙarshen 2026

      March 1, 2026
    • Siyasa

      Gwamnan Adamawa Ya Sauya Sheƙa Zuwa APC

      February 27, 2026

      NDLEA Ta Kama Wata Mata Mai Cikin Bogi Ɗauke da Hodar Iblis a Iyakar Seme

      February 22, 2026

      Jam’iyyun Adawa Sun Kaurace wa Zaɓen Kano, APC Ta Lashe Kujerun Majalisa a Rivers

      February 22, 2026

      Kotu Ta Umarci INEC Ta Yi Wa Jam’iyyar NDP Rajista

      February 19, 2026

      Gwamnan Zamfara Ya Zargi Gwamnatin Tarayya da Nuna Masa Wariya Saboda Bambancin Jam’iyya

      February 18, 2026
    • Addini

      Bauchi Ta neman ƙarin Kujerun Hajji Daga Saudiyya

      February 16, 2026

      Sarkin Musulmi Ya Umarci Ƴan Najeriya Su Fara Duban Jinjirin Watan Ramadan Ranar Talata

      February 16, 2026

      Tinubu Ya Naɗa Ambasada Ismail Abba Yusuf a Matsayin Sabon Shugaban NAHCON

      February 11, 2026

      Sheikh Usman Kusfa Zaria (Rigi-rigi) Ya Rasu

      February 2, 2026

      Jigawa Ta Fara Gwajin Lafiya ga Maniyyatan Hajjin 2026

      January 28, 2026
    • Nishadi

      Oculus Founder Makes a VR Headset That Can Literally Kill You

      January 13, 2021
      85

      Braun Series 7 Electric Shaver Review: Quality at a Good Price

      January 13, 2021
      85

      Google Pixel 7, iPhone 14 Compared: Check Out 5 Major Differences

      January 13, 2021

      Why Apple Should Skip The MacBook Pro Launch

      January 12, 2021

      Apollo G2J Showcases Electric Sports Car

      January 12, 2021
    • Tsaro

      Ba a Fasa Bututun Mai Ko Ɗaya a Niger Delta a 2025 Ba – Sojoj

      January 20, 2026

      Sojojin Najeriya Sun Ƙwato lita 290,000 Na Man Fetur a Yankin Neja Delta

      October 21, 2025

      Ƴan Bindiga Sun Ƙwace Wayoyin Ƴan Sanda a Zamfara

      October 2, 2025

      Gwamnan Kano Ya Buƙaci Tinubu Ya Tsige Kwamishinan Ƴan Sandan Jihar

      October 1, 2025

      Will Using a VPN on Phone Helps Protect You from Ransomware?

      January 14, 2021
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    Home » NDLEA Ta Cafke Mutane 230, Tare Da Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi a Kano
    Featured

    NDLEA Ta Cafke Mutane 230, Tare Da Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi a Kano

    Abbass AbdurrahmanBy Abbass AbdurrahmanNovember 21, 2025No Comments2 Mins Read

    Hukumar NDLEA reshen Kano ta sanar da cafke mutane 230 da ake zargi da aikata manyan laifukan miyagun kwayoyi, tare da kwato tarin haramtattun abubuwa a fadin birnin Kano. An bayyana haka ne yayin wani taron manema labarai da aka gudanar a ranar Juma’a, wanda ya nuna samun gagarumar nasara a yakin da hukumomin tsaro ke yi da sha, safara da yawan laifukan da suka shafi kwayoyi.

    Kwamandan NDLEA na Kano, Abubakar Ahmad, ya ce sun gudanar da aikin tsawon kwanaki 30 ba tare da dakatawa ba tare da hadin gwiwar rundunar ‘yan sanda, NSCDC, NIS, NCoS da DSS a karkashin rundunar hadin guiwa ta Kano Joint Task Force for Peace Restoration and Youth Rehabilitation da Yusuf Mata ke jagoranta. Rundunar ta kai samame a wuraren da suka hada da Kofar Ruwa, Tashar Rami, Rijiyar Lemo, Kurna, Zage, Dorayi, Dawanau, Filin Idi, Rimi Market, Zango, Kano Line da Kofar Mata.

    Hukumar ta ce an kwato hodar cannabis, Exol-5, diazepam, “suck and die”, roba solution, maganin tari na codeine da kuma makamai na gargajiya. Ahmad ya yaba da rawar da kwamishinan ‘yan sanda, Ibrahim Bakori, ya taka wajen hada kai tsakanin hukumomin tsaro, tare da jinjinawa DSS bisa taimakon bayanan sirri da take bayarwa. Ya kuma gode wa gwamnatin Kano a karkashin Gwamna Abba Yusuf bisa goyon bayan yaki da tabarbarewar matasa.

    NDLEA ta jaddada cewa binciken ya rage yawan laifuka da suka shafi fashi da wayar hannu, ta’addanci na titi da sauran munanan dabi’u. Kwamandan ya roki iyaye da al’umma da su ci gaba da bada hadin kai domin tabbatar da cewa yaki da sha da safarar miyagun kwayoyi ya yi nasara a fadin jihar.

    NDLEA
    Share. Facebook Twitter WhatsApp Telegram
    Previous ArticleCutar Zazzaɓin Lassa Ta Yi Ajalin Mutane 177 a Cikin Watanni 10 – NCDC
    Next Article NNPP Chairman Hails Formation of Kano Online Media Chapel as Timely and Impactful
    Abbass Abdurrahman
    • Website

    Related Posts

    Featured

    Ba Za Mu Bayar da Tabbacin Sahihin Zaɓe a 2027 Ba – Amupitan

    March 2, 2026
    Featured

    Jirage Marasa Matuƙa Sun Kai Hari Matatar Man Saudiyya

    March 2, 2026
    Featured

    Najeriya Ta Buƙaci a Kawo Karshen Rikicin Gabas ta Tsakiya

    March 2, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    SABBIN LABARAI

    Gwamnatin Kano Ta Dakatar da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi

    October 1, 202543 Views

    Kotu Ta Yankewa Tsohon Firayim Ministan Mali Hukuncin Zaman Gidan Yari Sakamakon Rubutu a Shafin Sada Zumunta

    October 27, 202541 Views

    Dantawaye Ya Zama Sabon Kwamishinan Ƴansanda a Abuja

    October 17, 202532 Views

    NAFDAC Ta Yi Gargaɗi Kan Wani Kororon Roba Me Matuƙar Haɗari Ga Lafiya

    December 30, 202527 Views

    An Gano Motar Ofishin Mataimakin Gwamna Da Aka Sace

    November 12, 202527 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    • Telegram
    © 2026 Bechi Hausa News. Developed by: ENGRMKS & CO.
    • Shafin Farko
    • Game da Mu
    • Ƙarin Bayani
    • Manufar Sirri
    • Ka’idoji da Sharudda
    • Tuntuɓe Mu

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.