Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    • Shafin Farko
    • Labarai

      Najeriya Ta Musanta Zargin Goyon Bayan Yunƙurin Juyin Mulki a Nijar

      September 4, 2026

      A shirye nake na mutu domin kare ƙuri’ata – Peter Obi

      September 4, 2026

      Sarkin Gumel Alhaji Ahmed Muhammad Sani Ya Rasu 

      September 3, 2026

      Gwamnatin Kano ta fitar da iyakoki tsakanin Jam’iar Bayero da alummar Rimin Zakara bayan kammala biyan diyya

      September 3, 2026

      Ƙungiyar Miyetti Allah Ta Buƙaci Tinubu Ya Sa a Saki Shugabanta

      September 3, 2026
    • Siyasa

      A shirye nake na mutu domin kare ƙuri’ata – Peter Obi

      September 4, 2026

      Ɗan Takarar Sanatan Kano ta Tsakiya a NDC Na Shirin Komawa APC

      September 2, 2026

      Ƴan Siyasa Ne Matsalar Najeriya – Peter Obi

      August 31, 2026

      Bai kamata Tinubu ya bar Najeriya a dai dai lokacin da matsaloli ke addabar ƙasarsa ba – Atiku

      August 31, 2026

      Atiku Ya Yi Alkawarin Sake Buɗe Iyakokin Najeriya Idan Ya Lashe Zaɓen 2027

      August 28, 2026
    • Addini

      Shugaban Asibitin Kwararru na Best Choice, Na Taya Gwamnan Kano Da Al’umma Bikin Murnar Maulidi Annabi SAW

      September 2, 2026

      Hajj 2027 : Kano ta kammala sayar da kujeru 3,050 da aka ware wa jihar

      August 31, 2026

      Gwamnatin Kano ta bayar da hutu domin bikin Takutaha

      August 26, 2026

      Wasu Malamai Daga Arewacin Najeriya Sun Goyi Bayan Tazarcen Tinubu

      August 23, 2026

      Gwamnatin Tarayya ta ayyana Talata a matsayin ranar hutun Maulidi

      August 21, 2026
    • Nishadi

      Oculus Founder Makes a VR Headset That Can Literally Kill You

      January 13, 2021
      85

      Braun Series 7 Electric Shaver Review: Quality at a Good Price

      January 13, 2021
      85

      Google Pixel 7, iPhone 14 Compared: Check Out 5 Major Differences

      January 13, 2021

      Why Apple Should Skip The MacBook Pro Launch

      January 12, 2021

      Apollo G2J Showcases Electric Sports Car

      January 12, 2021
    • Tsaro

      Ƴanbindiga Sun Sace Shugaban Jam’iyyar ’iyyar APC Na Ƙaramar Hukumar Rogo

      September 1, 2026

      Amurka Za Ta Janye Sojoji Kusan 200 Daga Najeriya

      August 28, 2026

      Sojoji Sun Kama Ƴan Ƙasashen Waje Da Ake Zargin Suna da Hannu a Matsalar Tsaron Najeriya – Bwala

      July 18, 2026

      ‘Yan Sanda Sun Fara Kwato Makaman Da Ke Hannun Jama’a Ba Bisa Ka’ida Ba – IGP Disu 

      July 17, 2026

      Sojoji Sun Gano Ƴan Ƙasashen Waje Uku Cikin Mayaƙan ISWAP a Borno

      July 13, 2026
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    Home » Zakaran Gwajin Dafi : Hajji 2025 Karkashin Farfesa Saleh Pakistan  
    Addini

    Zakaran Gwajin Dafi : Hajji 2025 Karkashin Farfesa Saleh Pakistan  

    Abbass AbdurrahmanBy Abbass AbdurrahmanNovember 24, 2025No Comments3 Mins Read

    Gabatarwa

    A kowace shekara, aikin Alhaji yana ɗaukar dubban ‘yan Nijeriya zuwa ƙasar Saudiyya don aiwatar da ɗaya daga cikin ginshiƙan Musulunci. Wannan babban aiki yana buƙatar tsari, gaskiya, da ƙwarewa abubuwan da suka zama alamar shugabancin Shugaban Hukumar Alhazai na ƙasa.

    A ƙarƙashin jagorancinsa, hukumar ta samu sauye-sauye masu muhimmanci da suka inganta tsarin tafiya, masauki, abinci, da kula da lafiya ga maniyyata. Wannan ya tabbatar da cewa aikin Alhaji ya zama abin alfahari ga Nijeriya da dukkan Musulmai.

    Gyare-gyare da Sauye-Sauye Masu Tasiri

    Tun bayan hawansa kujerar shugabanci, ya aiwatar da gyare-gyare na zahiri da na tsarin aiki da suka kawo sauƙi ga maniyyata.Daga cikin wannan tsare-tsaren akwai:

    An Kara Tsabtace Tsarin Rijista, Domin Gujewa Cin Hanci da Almundahana

    An samar da horar da maniyyata kafin tafiya, don su fahimci dokokin ibada da tsarin zamantakewa,

    An inganta huldar hukumar da hukumomin Saudiyya, domin tabbatar da aminci da jin daɗin maniyyata.

    Wadannan matakai sun nuna cewa wannan shugaba ba kawai mai kula da ofis ba ne, mai hangen nesa ne wanda ke son ganin aikin Alhaji yana gudana daidai da ƙa’idar Musulunci da mutuncin Najeriya.

    Walwalar Maniyyata na Gaba Da Komai

    Babban abin da ya fi mayar da hankali a kai shi ne walwalar maniyyata. A lokutan da wasu ke ganin wannan aiki a matsayin tafiyar ofis, shi yana ganinsa a matsayin ibada da amana. An samu sababbin tsare-tsare da suka tabbatar da cewa maniyyata suna samun:

    Masauki mai kyau da tsabta

    Kula da lafiya ta zamani

    Abinci mai inganci

    Sufuri mai aminci.

    A lokuta da dama shugaban hukumar alhazai da kansa yake zagayawa cikin sansanonin maniyyata yana dubawa kai tsaye don ganin duk wani umarni da ka bayar a rubuce ana aiwatar da shi a aikace wanda wannan alama ce ta an yi dacen shugaba mai kula da al’umma da zuciya ɗaya kuma jajirtacce.

    Jagoranci Da Addini

    A matsayinsa na malami kuma masani a fannin addini, yana jagoranci bisa tsoron Allah. Wannan halin nasa ne ya jawo masa girmamawa daga malamai da shugabannin addini daga sassa daban-daban na ƙasar.

    Ayyukansa sun tabbatar da cewa ibada da shugabanci suna iya tafiya tare, idan aka yi su da gaskiya, tsoron Allah, da hangen nesa.

    Tasirin Ayyukansa a Siyasa da Al’umma

    Baya ga aikin hajji, wannan shugaba ya zama murya ta gaskiya a cikin al’umma. Yana kira ga zaman lafiya, haɗin kai, da goyon bayan manufofin gwamnati masu amfani ga jama’a. A siyasance ya kare muradun gwamnati da ke nuni da kishin kasa son al’umma da tausaya musu , inganta tattalin arziki da kiwon lafiya da hada kawunan al’umma na kowacce nahiya da kabila a Nijeriya.

    Magoya bayansa sun ɗauke shi a matsayin malami mai kishin ƙasa, wanda ke amfani da matsayinsa wajen haɗa kai, ba rarrabuwar kai ba, don ya tafi da dukkan baggarori na dariku.

    Kammalawa

    Shugaban hukumar alhazai ya zama abin koyi ga shugabanni da dama mutum mai hangen nesa, mai gaskiya, mai amana, kuma mai kishin al’umma. “Duk wanda ya yi aiki da gaskiya, Allah zai tabbatar da darajarsa a duniya da lahira.

    Pakistan
    Share. Facebook Twitter WhatsApp Telegram
    Previous ArticleƳanbindiga Sun Yi Garkuwa Da Manoma 8 a Kebbi
    Next Article Zargin Biyan kudin Fansa : Gwamnatin Kaduna Ta Buƙaci El-Rufai Ya Janye Kalamansa Ko Ta Makashi a Gaban Kotu
    Abbass Abdurrahman
    • Website

    Related Posts

    Featured

    Najeriya Ta Musanta Zargin Goyon Bayan Yunƙurin Juyin Mulki a Nijar

    September 4, 2026
    Featured

    A shirye nake na mutu domin kare ƙuri’ata – Peter Obi

    September 4, 2026
    Featured

    Sarkin Gumel Alhaji Ahmed Muhammad Sani Ya Rasu 

    September 3, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    SABBIN LABARAI

    Ba Don Gudunmawar Masu Yiwa Ƙasa Hidima Ba Da Jihohi Dayawa Basu Kai Yadda Suke a Yanzu Ba – Minista

    December 8, 2025229 Views

    Sabon Rikici Ya Kunno Kai a NDC : Ƴan Takara Sun Kai Ƙara Kan Zaɓen Fidda-gwani a Kano

    June 30, 202680 Views

    Gwamnatin Kano Ta Dakatar da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi

    October 1, 202551 Views

    Gwamnatin Kano Ta Raba Filaye Ga Masu Taimakawa Gwamna Sama da 2,500

    August 1, 202644 Views

    Kotu Ta Yankewa Tsohon Firayim Ministan Mali Hukuncin Zaman Gidan Yari Sakamakon Rubutu a Shafin Sada Zumunta

    October 27, 202541 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    • Telegram
    © 2026 Bechi Hausa News. Developed by: ENGRMKS & CO.
    • Shafin Farko
    • Game da Mu
    • Ƙarin Bayani
    • Manufar Sirri
    • Ka’idoji da Sharudda
    • Tuntuɓe Mu

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.