Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    • Shafin Farko
    • Labarai

      Mutane 4 Sun Mutu a Turmutsutsun Karɓar Sadaka a Katsina

      March 2, 2026

      Ba Za Mu Bayar da Tabbacin Sahihin Zaɓe a 2027 Ba – Amupitan

      March 2, 2026

      Jirage Marasa Matuƙa Sun Kai Hari Matatar Man Saudiyya

      March 2, 2026

      Najeriya Ta Buƙaci a Kawo Karshen Rikicin Gabas ta Tsakiya

      March 2, 2026

      Iran Ta Naɗa Ayatollah Arafi A Matsayin Jagoran Addini Na Riƙo

      March 1, 2026
    • Siyasa

      Gwamnan Adamawa Ya Sauya Sheƙa Zuwa APC

      February 27, 2026

      NDLEA Ta Kama Wata Mata Mai Cikin Bogi Ɗauke da Hodar Iblis a Iyakar Seme

      February 22, 2026

      Jam’iyyun Adawa Sun Kaurace wa Zaɓen Kano, APC Ta Lashe Kujerun Majalisa a Rivers

      February 22, 2026

      Kotu Ta Umarci INEC Ta Yi Wa Jam’iyyar NDP Rajista

      February 19, 2026

      Gwamnan Zamfara Ya Zargi Gwamnatin Tarayya da Nuna Masa Wariya Saboda Bambancin Jam’iyya

      February 18, 2026
    • Addini

      Bauchi Ta neman ƙarin Kujerun Hajji Daga Saudiyya

      February 16, 2026

      Sarkin Musulmi Ya Umarci Ƴan Najeriya Su Fara Duban Jinjirin Watan Ramadan Ranar Talata

      February 16, 2026

      Tinubu Ya Naɗa Ambasada Ismail Abba Yusuf a Matsayin Sabon Shugaban NAHCON

      February 11, 2026

      Sheikh Usman Kusfa Zaria (Rigi-rigi) Ya Rasu

      February 2, 2026

      Jigawa Ta Fara Gwajin Lafiya ga Maniyyatan Hajjin 2026

      January 28, 2026
    • Nishadi

      Oculus Founder Makes a VR Headset That Can Literally Kill You

      January 13, 2021
      85

      Braun Series 7 Electric Shaver Review: Quality at a Good Price

      January 13, 2021
      85

      Google Pixel 7, iPhone 14 Compared: Check Out 5 Major Differences

      January 13, 2021

      Why Apple Should Skip The MacBook Pro Launch

      January 12, 2021

      Apollo G2J Showcases Electric Sports Car

      January 12, 2021
    • Tsaro

      Ba a Fasa Bututun Mai Ko Ɗaya a Niger Delta a 2025 Ba – Sojoj

      January 20, 2026

      Sojojin Najeriya Sun Ƙwato lita 290,000 Na Man Fetur a Yankin Neja Delta

      October 21, 2025

      Ƴan Bindiga Sun Ƙwace Wayoyin Ƴan Sanda a Zamfara

      October 2, 2025

      Gwamnan Kano Ya Buƙaci Tinubu Ya Tsige Kwamishinan Ƴan Sandan Jihar

      October 1, 2025

      Will Using a VPN on Phone Helps Protect You from Ransomware?

      January 14, 2021
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    Home » Ba Za Mu Yafewa Waɗanda Suka Kashe Mutanenmu a Zaria Ba – IMN
    Featured

    Ba Za Mu Yafewa Waɗanda Suka Kashe Mutanenmu a Zaria Ba – IMN

    Abbass AbdurrahmanBy Abbass AbdurrahmanDecember 11, 2025Updated:December 11, 2025No Comments2 Mins Read

    Mabiya mazhabar Shi’a a Najeriya sun sake tunawa da cikar shekaru goma da kisan gillar da aka yi musu a Zaria, yayin da suka ce har yanzu suna cikin raɗaɗin abin da ya faru. A 2015 ne rikici ya barke tsakanin jami’an sojin Najeriya da mabiya Sheikh Ibrahim Zakzaky, lamarin da ya yi sanadin mutuwar daruruwan mutane da kuma jikkata da dama, bayan zargin Rundunar Soji cewa an tare musu hanya.

    Farfesa Abdullahi Danladi, shugaban dandalin tattaunawa na IMN a Najeriya, ya bayyana wa BBC cewa a duk tsawon shekarun nan babu wani ɓangaren gwamnati da ya ɗauki mataki kan wadanda suka aikata kisan. Ya ce babu hukunci, babu kama, babu rahoton kwamitin binciken da aka kafa — abin da ya tabbatar musu cewa an yi ƙoƙarin rufe gaskiya. Ya ce hakan na ƙara tunzura zukatan mabiya Shi’a da kuma tabbatar musu da cewa an tauye musu adalci.

    A cewar Farfesan, al’ummar Shi’a za su ci gaba da neman adalci muddin suna raye, tare da jaddada cewa tarihi ba zai manta da abin da ya faru a Zaria ba. Ya yi nuni da cewa ko da shari’a ta ɗauki lokaci mai tsawo, gaskiya dole ta bayyana wata rana. A cewar sa, wannan rana ta tunawa ta musamman ta sake tayar masu da raɗaɗin abin da ya faru, tare da ƙarfafa matsayarsu na kin yafiya.

    Bechi Hausa ta tattaro cewa IMN na ci gaba da kira ga gwamnati da hukumomin tsaro da su fitar da cikakken rahoto kan lamarin, tare da hukunta wadanda suka aikata kisan. Farfesan Danladi ya ce za su ci gaba da taruwa duk shekara, su fadakar da junansu game da wannan hari, domin tabbatar da cewa ba a manta da waɗanda suka mutu ba kuma an tabbatar da ganin adalci.

    IMN
    Share. Facebook Twitter WhatsApp Telegram
    Previous ArticleEFCC Ta Kama Tsohon Minista Ƙwadago
    Next Article Najeriya Zata Ƙulla Ƙawance Da Saudiyya Kan Sha’anin Tsaro
    Abbass Abdurrahman
    • Website

    Related Posts

    Featured

    Mutane 4 Sun Mutu a Turmutsutsun Karɓar Sadaka a Katsina

    March 2, 2026
    Featured

    Ba Za Mu Bayar da Tabbacin Sahihin Zaɓe a 2027 Ba – Amupitan

    March 2, 2026
    Featured

    Jirage Marasa Matuƙa Sun Kai Hari Matatar Man Saudiyya

    March 2, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    SABBIN LABARAI

    Gwamnatin Kano Ta Dakatar da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi

    October 1, 202543 Views

    Kotu Ta Yankewa Tsohon Firayim Ministan Mali Hukuncin Zaman Gidan Yari Sakamakon Rubutu a Shafin Sada Zumunta

    October 27, 202541 Views

    Dantawaye Ya Zama Sabon Kwamishinan Ƴansanda a Abuja

    October 17, 202532 Views

    NAFDAC Ta Yi Gargaɗi Kan Wani Kororon Roba Me Matuƙar Haɗari Ga Lafiya

    December 30, 202527 Views

    An Gano Motar Ofishin Mataimakin Gwamna Da Aka Sace

    November 12, 202527 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    • Telegram
    © 2026 Bechi Hausa News. Developed by: ENGRMKS & CO.
    • Shafin Farko
    • Game da Mu
    • Ƙarin Bayani
    • Manufar Sirri
    • Ka’idoji da Sharudda
    • Tuntuɓe Mu

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.