Majalisar Dattawan Najeriya ta sanar da kiran zaman gaggawa a ranar Talata, 10 ga Fabrairu, 2026, sakamakon ƙara fushin jama’a kan gyaran Dokar Zaɓe, musamman kin amincewa da sashe da ke wajabta tura sakamakon zaɓe ta na’ura kai tsaye. Sanarwar kiran zaman ta fito ne daga Magatakardar Majalisar, Emmanuel Odo.
Matakin ya zo ne bayan Kungiyar Kwadago ta Najeriya (NLC) da wasu ƙungiyoyin farar hula sun yi barazanar zanga-zanga da kaurace wa zaɓe, suna zargin Majalisar Dattawa da tayar da rudani kan batun tura sakamakon zaɓe ta lantarki. Sabuwar ƙungiyar Movement for Credible Elections ta bayyana shirin gudanar da zanga-zangar “Occupy NASS” a Abuja.
Rigimar ta samo asali ne bayan Majalisar Dattawa ta ƙi sashe na 60(3) a ranar 4 ga Fabrairu, wanda ke wajabta wa INEC tura sakamakon zaɓe kai tsaye daga rumfunan zaɓe. Duk da haka, an ce kwamitin haɗin gwiwa na Majalisar Wakilai da Majalisar Dattawa zai gana a wannan mako domin warware sabanin da ke cikin dokar kafin amincewa ta ƙarshe.

