Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    • Shafin Farko
    • Labarai

      Ba Kama Gbajabiamila Muka Yi Ba Gayyatarsa Muka Yi – ICPC

      July 21, 2026

      Tinubu Ya Naɗa Sabbin Shugabanni Da Mambobi 26 a Hukumomi Da Kwamitocin Gwamnatin Tarayya

      July 21, 2026

      An Zargi Likitan El-Rufai Da Bayar da Rahoton Jinya Na Bogi

      July 21, 2026

      Guguwa Da Ruwan Sama Mai Ƙarfi Sun Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutane Huɗu a Sakkwato

      July 21, 2026

      Mamakon Ruwan Sama Ya Lalata Gidaje Da Gonaki a Filato

      July 20, 2026
    • Siyasa

      Kotu Ta Yi Watsi da Ƙarar da Tsagin Tanimu Turaki Suka Shigar Kan Rikicin Shugabancin PDP

      July 18, 2026

      Ya Kamata Majalisa Ta Yi Bincike Kan Ingancin Lafiyar Tinubu – ADC

      July 17, 2026

      Gwamna Yusuf Ya Zaɓi Garo a Matsayin Mataimakinsa a Zaɓen 2027

      July 13, 2026

      INEC Ta Ƙara Wa’adin Miƙa Sunayen ‘Yan Takarar Zaɓen 2027

      July 12, 2026

      Sauye-sauyen Gwamnatina Sun Inganta Ayyuka Da Tattalin Arziki a Kaduna – Gwamna Uba Sani 

      July 10, 2026
    • Addini

      An Rufe Birnin Tehran Domin Jana’izar Ayatollah Ali Khamenei

      July 1, 2026

      Kotu Ta Buƙaci a Gabatar Da Litattafan Da Sheikh Abduljabbar Ya Yi Amfani Da Su

      June 29, 2026

      NAHCON Ta Kammala Dawo Da Alhazan Najeriya Daga Saudiyya

      June 23, 2026

      Sarkin Musulmi Ya Buƙaci Hukumomi Su Gaggauta Ɗaukar Matakai Domin Magance Matsalar Tsaro

      June 17, 2026

      Gwamnatin Kano Za Ta Kashe Naira Biliyan 1.5 Domin Shirin ‘Auren Gata’

      June 15, 2026
    • Nishadi

      Oculus Founder Makes a VR Headset That Can Literally Kill You

      January 13, 2021
      85

      Braun Series 7 Electric Shaver Review: Quality at a Good Price

      January 13, 2021
      85

      Google Pixel 7, iPhone 14 Compared: Check Out 5 Major Differences

      January 13, 2021

      Why Apple Should Skip The MacBook Pro Launch

      January 12, 2021

      Apollo G2J Showcases Electric Sports Car

      January 12, 2021
    • Tsaro

      Sojoji Sun Kama Ƴan Ƙasashen Waje Da Ake Zargin Suna da Hannu a Matsalar Tsaron Najeriya – Bwala

      July 18, 2026

      ‘Yan Sanda Sun Fara Kwato Makaman Da Ke Hannun Jama’a Ba Bisa Ka’ida Ba – IGP Disu 

      July 17, 2026

      Sojoji Sun Gano Ƴan Ƙasashen Waje Uku Cikin Mayaƙan ISWAP a Borno

      July 13, 2026

      An Kashe Fitaccen Jagoran ‘Yan Bindiga Sani Yellow a Zamfara

      July 12, 2026

      Matasa a Borno Sun Gudanar Da Zanga-Zanga Kan Rashin Tsaro

      July 12, 2026
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    Home » Saura Ƙiris Mu Daƙile Matsalar Tsaro a Najeriya – Badaru Abubakar
    Featured

    Saura Ƙiris Mu Daƙile Matsalar Tsaro a Najeriya – Badaru Abubakar

    Abbass AbdurrahmanBy Abbass AbdurrahmanNovember 27, 2025No Comments2 Mins Read

    Ministan tsaron Najeriya, Mohammed Badaru Abubakar, ya bayyana cewa gwamnati na gudanar da bincike kan dalilin da ya janyo dawowar hare-haren satar ɗalibai a makarantu da ’yan bindiga suka sake farawa a wasu yankuna na ƙasar. Ya ce duk da cewa akwai raguwar matsalolin tsaro, irin wannan yaki da ’yan ta’adda ba ya ƙarewa cikin sauƙi, domin sukan ɓullo da sababbin dabaru lokaci zuwa lokaci. Badaru ya bayyana cewa akwai wuraren da gwamnati ta sani, amma ba za a iya kai farmaki ba saboda kasancewar su a cikin yankunan da ke cike da jama’a ko kuma daji da ba za a iya harba bam ba.

    A cewarsa, sojojin ƙasar na aiki ba dare ba rana domin murkushe waɗanda ke haddasa wannan sabon tashin hankali. Ministan ya ce gwamnati ba ta taɓa bayyana cewa an kammala kawar da matsalar tsaro gaba ɗaya ba, amma abin da ya fi tayar musu da hankali shi ne dawowar harin da ya ƙaddamar da satar ɗalibai daga makarantunsu. Ya ce ana gudanar da zurfin nazari domin gano ainihin musabbabin komawar wannan barazana da kuma matakan da za a ɗauka don dakile ta gaba ɗaya.

    Badaru ya yi karin bayani kan tsaron makarantu, yana mai cewa gwamnati na da tsari na musamman na kare cibiyoyin ilimi daga hare-haren ’yan bindiga. Ya ce wannan tsari ne ya sa aka samu sauƙi cikin shekaru biyun da suka gabata, inda ba a sami manyan hare-hare da suka shafi ɗalibai ba. Sai dai ministan ya ce ana sake duba tsarin ne domin tabbatar da cewa kura ta kama ne kawai, ba wai barazana ta dawo da ƙarfi ba.

    Ya ƙara da cewa gwamnati za ta karfafa matakai tare da inganta dabarun yaki da ‘yan ta’adda, musamman a yankunan da suka sha fama da matsalar satar ɗalibai. Masu nazari kan tsaro na bayyana cewa dawowar irin wadannan hare-hare na iya shafar burin gwamnati na dawo da kwarin gwiwar iyaye da ɗalibai kan komawa makarantu. Ana sa ran gwamnati za ta sanar da sabbin matakan tsaro cikin makonni masu zuwa domin tabbatar da cewa makarantu sun kasance wurare masu aminci ga yara a fadin Najeriya.

    Najeriya
    Share. Facebook Twitter WhatsApp Telegram
    Previous ArticleJanye Ƴansanda Daga Bawa Manyan Mutane Kariya Zai Jefa Rayuwarmu Cikin Haɗari – Sanatoci
    Next Article Gwamnonin Arewa Sun Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Sheikh Dahiru Bauchi
    Abbass Abdurrahman
    • Website

    Related Posts

    Featured

    Ba Kama Gbajabiamila Muka Yi Ba Gayyatarsa Muka Yi – ICPC

    July 21, 2026
    Featured

    Tinubu Ya Naɗa Sabbin Shugabanni Da Mambobi 26 a Hukumomi Da Kwamitocin Gwamnatin Tarayya

    July 21, 2026
    Featured

    An Zargi Likitan El-Rufai Da Bayar da Rahoton Jinya Na Bogi

    July 21, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    SABBIN LABARAI

    Ba Don Gudunmawar Masu Yiwa Ƙasa Hidima Ba Da Jihohi Dayawa Basu Kai Yadda Suke a Yanzu Ba – Minista

    December 8, 2025150 Views

    Sabon Rikici Ya Kunno Kai a NDC : Ƴan Takara Sun Kai Ƙara Kan Zaɓen Fidda-gwani a Kano

    June 30, 202679 Views

    Gwamnatin Kano Ta Dakatar da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi

    October 1, 202546 Views

    Kotu Ta Yankewa Tsohon Firayim Ministan Mali Hukuncin Zaman Gidan Yari Sakamakon Rubutu a Shafin Sada Zumunta

    October 27, 202541 Views

    Dantawaye Ya Zama Sabon Kwamishinan Ƴansanda a Abuja

    October 17, 202533 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    • Telegram
    © 2026 Bechi Hausa News. Developed by: ENGRMKS & CO.
    • Shafin Farko
    • Game da Mu
    • Ƙarin Bayani
    • Manufar Sirri
    • Ka’idoji da Sharudda
    • Tuntuɓe Mu

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.