Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    • Shafin Farko
    • Labarai

      Gwamnatin Kano Ta Shiryawa Ƴan Jaridar Yanar Gizo Horo Na Yini Biyu a Jigawa

      January 15, 2026

      Tanka Ta Murƙushe Mutane 5 a Gombe

      January 12, 2026

      Babu Siyasa a Binciken Da Ake Yi Wa Malami – EFCC

      January 12, 2026

      Ƴan Bindiga Sun Kashe Soja Da Jam’in NSCDC a Benue

      January 12, 2026

      Manyan Jiga-jigan APC 3 a Kogi Sun Mutu

      January 12, 2026
    • Siyasa

      Manyan Jiga-jigan APC 3 a Kogi Sun Mutu

      January 12, 2026

      Ganduje Zai Gana Da Masu Ruwa-da-tsaki Na APC

      January 11, 2026

      Datti Baba-Ahmed Ya Musanta Batun Tsayawa Takarar Shugaban Ƙasa

      January 9, 2026

      Fubara Barazana Ne Ga Demokaraɗiyya – Kakakin Majalisar Rivers

      January 9, 2026

      Kotu Ta Ƙi Bayar da Belin Kwamishinan Kuɗi Na Bauchi

      January 6, 2026
    • Addini

      Kano: Hisbah Ta Karɓi Ƙorafe-Ƙorafe Sama da 12,000 a 2025

      January 2, 2026

      Da Ɗumi-ɗumi : Sheikh Dahiru Bauchi Ya rasu

      November 27, 2025

      Zakaran Gwajin Dafi : Hajji 2025 Karkashin Farfesa Saleh Pakistan  

      November 24, 2025

      Hajji Da Shugabanci Nagari Ƙarƙashin Jagorancin Farfesa Pakistan

      November 17, 2025

      Hukumar NAHCON Ta Sanar Da Rage Kudin Aikin Hajjin 2026

      November 10, 2025
    • Nishadi

      Oculus Founder Makes a VR Headset That Can Literally Kill You

      January 13, 2021
      85

      Braun Series 7 Electric Shaver Review: Quality at a Good Price

      January 13, 2021
      85

      Google Pixel 7, iPhone 14 Compared: Check Out 5 Major Differences

      January 13, 2021

      Why Apple Should Skip The MacBook Pro Launch

      January 12, 2021

      Apollo G2J Showcases Electric Sports Car

      January 12, 2021
    • Tsaro

      Sojojin Najeriya Sun Ƙwato lita 290,000 Na Man Fetur a Yankin Neja Delta

      October 21, 2025

      Ƴan Bindiga Sun Ƙwace Wayoyin Ƴan Sanda a Zamfara

      October 2, 2025

      Gwamnan Kano Ya Buƙaci Tinubu Ya Tsige Kwamishinan Ƴan Sandan Jihar

      October 1, 2025

      Will Using a VPN on Phone Helps Protect You from Ransomware?

      January 14, 2021

      Popular New Xbox Game Pass Game Being Review Bombed With “0s”

      January 14, 2021
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    Home » Ƴan Bindiga Sun Ƙwace Wayoyin Ƴan Sanda a Zamfara
    Featured

    Ƴan Bindiga Sun Ƙwace Wayoyin Ƴan Sanda a Zamfara

    Abbass AbdurrahmanBy Abbass AbdurrahmanOctober 2, 2025No Comments2 Mins Read

    ‘Yan bindiga sun sace kansiloli biyu masu ci da kuma wani Liman a daren Laraba 01ga Oktoba, a garin Tsauni, birnin Gusau, babban birnin jihar Zamfara.

    Kansilolin da abin ya shafa su ne na mazabu biyu, Gidan Goga da Tsibiri a karamar hukumar Maradun, inda aka ce an kama su da misalin ƙarfe 8:05 na dare, jim kaɗan bayan sallar Magrib, a kusa da ofishin ‘yan sanda.

    Shugaban karamar hukumar Maradun, Hon. Sanusi Gama Giwa, ya tabbatar da lamarin, inda ya bayyana cewa waɗanda aka sace ɗin ‘yan majalisarsa ne.

    A cewarsa, mutanen suna zaune ne a wajen shan shayi lokacin da ‘yan bindigar suka kai farmaki.

    “Lamarin ya faru ne a gaban ofishin ‘yan sanda inda jami’ai kan kasance. ‘Yan bindigar ma sun kwace wayoyin ‘yan sandan ba tare da wata turjiya ba. Ba su cutar da kowa ba,” in ji Giwa.

    Ya ƙara da cewa maharan sun fito ne da niyyar kama wani mutum daga kauyen Kaura. Amma da suka kasa samun wanda suke nema, sai suka yi awon gaba da mutum shida, kafin daga baya su saki uku, sannan su ci gaba da tafiya da kansilolin biyu da Liman ɗin.

    Garin Tsauni, inda aka sace mutanen, na ɗaya daga cikin wuraren da aka taɓa karɓar bakin ‘yan gudun hijira da suka tsere daga hare-haren ‘yan bindiga a kauyukan da ke kewaye — lamarin da ya sake tayar da hankula kan raunin tsaron yankin.

    Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Zamfara, DSP Yazid Abubakar, ya tabbatar da aukuwar lamarin, yana mai cewa tuni jami’an tsaro su ka bi sahun su, kuma a halin yanzu su na yin dik mai yiwuwa wajen ceto su.

    “Muna yin duk abin da ya kamata don ceto waɗanda aka sace tare da tabbatar da an hukunta maharan,” in ji DSP Abubakar, yana kira ga al’umma da su rika ba da sahihan bayanai da za su taimaka wajen yaki da masu aikata laifuka.

    Zamfara
    Share. Facebook Twitter WhatsApp Telegram
    Previous ArticleAmbaliyar Ruwa: Gwamnatin Neja Ta Gargadi Al’umma Su Zauna Cikin Shiri Sakamakon Sakin Ruwa Daga Kogin Neja
    Next Article INEC Ta Buƙaci Majalisa Ta Gaggauta Amincewa Da Sabbin Dokokinta
    Abbass Abdurrahman
    • Website

    Related Posts

    Featured

    Gwamnatin Kano Ta Shiryawa Ƴan Jaridar Yanar Gizo Horo Na Yini Biyu a Jigawa

    January 15, 2026
    Featured

    Tanka Ta Murƙushe Mutane 5 a Gombe

    January 12, 2026
    Featured

    Babu Siyasa a Binciken Da Ake Yi Wa Malami – EFCC

    January 12, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    SABBIN LABARAI

    Gwamnatin Kano Ta Dakatar da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi

    October 1, 202542 Views

    Kotu Ta Yankewa Tsohon Firayim Ministan Mali Hukuncin Zaman Gidan Yari Sakamakon Rubutu a Shafin Sada Zumunta

    October 27, 202541 Views

    Dantawaye Ya Zama Sabon Kwamishinan Ƴansanda a Abuja

    October 17, 202532 Views

    An Gano Motar Ofishin Mataimakin Gwamna Da Aka Sace

    November 12, 202527 Views

    NAFDAC Ta Yi Gargaɗi Kan Wani Kororon Roba Me Matuƙar Haɗari Ga Lafiya

    December 30, 202525 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    • Telegram
    © 2026 Bechi Hausa News. Developed by: ENGRMKS & CO.
    • Shafin Farko
    • Game da Mu
    • Ƙarin Bayani
    • Manufar Sirri
    • Ka’idoji da Sharudda
    • Tuntuɓe Mu

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.