Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    • Shafin Farko
    • Labarai

      Tinubu Ya Sha Alwashin Murƙushe Ta’addanci a Najeriya

      November 6, 2025

      Hukumar Kiyaye Afkuwar Haɗura Ta Ƙasa Ta Kama Direbobi 27,000 a Abuja

      November 6, 2025

      Gidaje 20 Da Ake Zargina a Kansu Ba Nawa Bane Ne Waɗanda Mahaifinmu Ya Bar Mana Gado Ne – Abba Kyari

      November 6, 2025

      Matuƙar Ba’a Yi Yadda Aka Yi a Afghanistan Ba Baza’a Kawo Ƙarshen Ta’addanci a Najeriya Ba – Amurka

      November 6, 2025

      Shekarau @ 70: Damuwa Bata Taɓa Hanani Bacci Ba – Shekarau

      November 6, 2025
    • Siyasa

      Gombe Na Amfana Da Cire Tallafin Man Fetur – Inuwa Yahya

      November 4, 2025

      Sabon Rikici Na Shirin Kunno Kai Tsakanin Sanata Natasha Da Akpabio

      November 4, 2025

      Har Yanzu Bamu Janye Dakatarwar Shekaru 30 Da Mu Ka Yi Wa El-Rufai Ba – SDP

      November 2, 2025

      Gwamnan Taraba Zai Koma Jam’iyyar APC

      October 29, 2025

      Gwamnonin PDP Sun Zaɓi Tanimu Turaki a Matsayin Ɗan Takararsu a Zaɓen Shugabancin Jam’iyya

      October 25, 2025
    • Addini

      Ƙungiyoyin Fityanul Islam Da Samarin Tijjaniyya Sun Yi Ƙarar Gwamnatin Kano a Kotu

      November 5, 2025

      Saudiyya Ta Ragewa Najeriya Kujerun Hajjin 2026

      October 17, 2025

      Sarkin Musulmi Ya Buƙaci a Samar Da Dokokin Amfani Da Kafafen Sada Zumunta a Najeriya

      October 16, 2025

      Hisbah Ta Kama Wasu Matasa Da Laifin Yin Aure Ba Tare Da Amincewar Iyayensu Ba

      October 13, 2025

      Tinubu Ya Bawa NAHCON Umarnin Rage Kuɗin Hajjin 2026 Cikin Gaggawa

      October 7, 2025
    • Nishadi

      Oculus Founder Makes a VR Headset That Can Literally Kill You

      January 13, 2021
      85

      Braun Series 7 Electric Shaver Review: Quality at a Good Price

      January 13, 2021
      85

      Google Pixel 7, iPhone 14 Compared: Check Out 5 Major Differences

      January 13, 2021

      Why Apple Should Skip The MacBook Pro Launch

      January 12, 2021

      Apollo G2J Showcases Electric Sports Car

      January 12, 2021
    • Tsaro

      Sojojin Najeriya Sun Ƙwato lita 290,000 Na Man Fetur a Yankin Neja Delta

      October 21, 2025

      Ƴan Bindiga Sun Ƙwace Wayoyin Ƴan Sanda a Zamfara

      October 2, 2025

      Gwamnan Kano Ya Buƙaci Tinubu Ya Tsige Kwamishinan Ƴan Sandan Jihar

      October 1, 2025

      Will Using a VPN on Phone Helps Protect You from Ransomware?

      January 14, 2021

      Popular New Xbox Game Pass Game Being Review Bombed With “0s”

      January 14, 2021
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    Home » Ƴan Sanda Sun Gano Wayoyi 75 da Kwamfutoci 5 da Aka Sace a Lagos
    Featured

    Ƴan Sanda Sun Gano Wayoyi 75 da Kwamfutoci 5 da Aka Sace a Lagos

    Abbass AbdurrahmanBy Abbass AbdurrahmanOctober 18, 2025No Comments2 Mins Read

    Rundunar ‘Yan Sanda ta Jihar Lagos ta gano wayoyi 75 da kwamfutoci 5 da wasu barayi suka ajiye yayin da suke gudu a lokacin sintirin jami’an Rapid Response Squad (RRS) a Ikeja. Kakakin rundunar, SP Abimbola Adebisi, ya bayyana a ranar Asabar 18 ga Oktoba, cewa an gano kayan ne bayan jami’ai sun hango wasu mutum biyu dauke da manyan jakunkuna na “Ghana Must Go” a kusa da Allen Roundabout, inda suka tsere da ganin jami’an tsaro.

    Binciken da aka gudanar ya nuna cewa jakunkunan sun ƙunshi iPhones guda 32, wayoyi 38 na kamfanoni daban-daban kamar Samsung, Redmi, Tecno da Honour, kwamfutoci biyar, agogon zamani, AirPods, Samsung Tab da Sorapad. Kwamandan RRS, CSP Shola Jejeloye, ya ce kayan satar ne da barayin suka ajiye da gaggawa yayin da suka tsere. Rundunar ta bukaci duk wanda ya rasa irin wadannan na’urori ya je hedkwatar RRS da shaidar mallaka don karɓar kayansa.

    Kwamishinan ‘Yan Sanda na jihar, CP Moshood Jimoh, ya yabawa jami’an RRS bisa kwazon da suka nuna, tare da tabbatar da cewa rundunar za ta ci gaba da amfani da dabarun leken asiri da sintiri domin hana laifuka. Ya ce ana ƙara tsaurara tsaro a dukkan sassan jihar don kare rayuka da dukiyoyin jama’a.

    A wani samame dabam, rundunar ta kama ‘yan wata kungiyar fashi da sace motoci guda hudu, waɗanda ake zargi da kai hare-hare masu hatsari ga direbobi a jihar da maƙwabta. SP Adebisi ya ce an kama su ne tsakanin 15 zuwa 17 ga Oktoba sakamakon binciken sirri da jami’an sashen Tactical Squad suka gudanar. Rundunar ta tabbatar da cewa za a gurfanar da su a gaban kotu bayan kammala bincike.

    Ƴan Sanda
    Share. Facebook Twitter WhatsApp Telegram
    Previous ArticleDantawaye Ya Zama Sabon Kwamishinan Ƴansanda a Abuja
    Next Article Wike Ya Musanta Batun Tsayawa Takara a Zaben 2027
    Abbass Abdurrahman
    • Website

    Related Posts

    Featured

    Tinubu Ya Sha Alwashin Murƙushe Ta’addanci a Najeriya

    November 6, 2025
    Featured

    Hukumar Kiyaye Afkuwar Haɗura Ta Ƙasa Ta Kama Direbobi 27,000 a Abuja

    November 6, 2025
    Featured

    Gidaje 20 Da Ake Zargina a Kansu Ba Nawa Bane Ne Waɗanda Mahaifinmu Ya Bar Mana Gado Ne – Abba Kyari

    November 6, 2025
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    SABBIN LABARAI

    Gwamnatin Kano Ta Dakatar da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi

    October 1, 202535 Views

    Kotu Ta Yankewa Tsohon Firayim Ministan Mali Hukuncin Zaman Gidan Yari Sakamakon Rubutu a Shafin Sada Zumunta

    October 27, 202533 Views

    Dantawaye Ya Zama Sabon Kwamishinan Ƴansanda a Abuja

    October 17, 202526 Views

    Zama a Banɗaki Fiye Da Kima Kan Haifar Da Matsala Ga Lafiyar Ɗan Adam – Likita

    October 28, 202520 Views

    Kotu Ta Bayar Da Belin Sowore

    October 24, 202519 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    • Telegram
    © 2025 Bechi Hausa News. Developed by: ENGRMKS & CO.
    • Shafin Farko
    • Game da Mu
    • Ƙarin Bayani
    • Manufar Sirri
    • Ka’idoji da Sharudda
    • Tuntuɓe Mu

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.