Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    • Shafin Farko
    • Labarai

      Gwamnatin Kano Ta Shiryawa Ƴan Jaridar Yanar Gizo Horo Na Yini Biyu a Jigawa

      January 15, 2026

      Tanka Ta Murƙushe Mutane 5 a Gombe

      January 12, 2026

      Babu Siyasa a Binciken Da Ake Yi Wa Malami – EFCC

      January 12, 2026

      Ƴan Bindiga Sun Kashe Soja Da Jam’in NSCDC a Benue

      January 12, 2026

      Manyan Jiga-jigan APC 3 a Kogi Sun Mutu

      January 12, 2026
    • Siyasa

      Manyan Jiga-jigan APC 3 a Kogi Sun Mutu

      January 12, 2026

      Ganduje Zai Gana Da Masu Ruwa-da-tsaki Na APC

      January 11, 2026

      Datti Baba-Ahmed Ya Musanta Batun Tsayawa Takarar Shugaban Ƙasa

      January 9, 2026

      Fubara Barazana Ne Ga Demokaraɗiyya – Kakakin Majalisar Rivers

      January 9, 2026

      Kotu Ta Ƙi Bayar da Belin Kwamishinan Kuɗi Na Bauchi

      January 6, 2026
    • Addini

      Kano: Hisbah Ta Karɓi Ƙorafe-Ƙorafe Sama da 12,000 a 2025

      January 2, 2026

      Da Ɗumi-ɗumi : Sheikh Dahiru Bauchi Ya rasu

      November 27, 2025

      Zakaran Gwajin Dafi : Hajji 2025 Karkashin Farfesa Saleh Pakistan  

      November 24, 2025

      Hajji Da Shugabanci Nagari Ƙarƙashin Jagorancin Farfesa Pakistan

      November 17, 2025

      Hukumar NAHCON Ta Sanar Da Rage Kudin Aikin Hajjin 2026

      November 10, 2025
    • Nishadi

      Oculus Founder Makes a VR Headset That Can Literally Kill You

      January 13, 2021
      85

      Braun Series 7 Electric Shaver Review: Quality at a Good Price

      January 13, 2021
      85

      Google Pixel 7, iPhone 14 Compared: Check Out 5 Major Differences

      January 13, 2021

      Why Apple Should Skip The MacBook Pro Launch

      January 12, 2021

      Apollo G2J Showcases Electric Sports Car

      January 12, 2021
    • Tsaro

      Sojojin Najeriya Sun Ƙwato lita 290,000 Na Man Fetur a Yankin Neja Delta

      October 21, 2025

      Ƴan Bindiga Sun Ƙwace Wayoyin Ƴan Sanda a Zamfara

      October 2, 2025

      Gwamnan Kano Ya Buƙaci Tinubu Ya Tsige Kwamishinan Ƴan Sandan Jihar

      October 1, 2025

      Will Using a VPN on Phone Helps Protect You from Ransomware?

      January 14, 2021

      Popular New Xbox Game Pass Game Being Review Bombed With “0s”

      January 14, 2021
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    Home » Mutane 2 Cikin 11 Na Fuskantar Yunwa a Najeriya — Binciken Masana
    Featured

    Mutane 2 Cikin 11 Na Fuskantar Yunwa a Najeriya — Binciken Masana

    Abbass AbdurrahmanBy Abbass AbdurrahmanOctober 4, 2025No Comments2 Mins Read

    Masana harkar noma sun bayyana cewa mutane biyu cikin kowace goma sha ɗaya a Najeriya na fama da yunwa a kullum, yayin da ɗaya cikin biyar na nahiyar Afirka ke fama da ƙarancin abinci.

    Wannan bayani ya fito ne daga Onijighogia Emmanuel, wakilin shirin Comprehensive Africa Agriculture Development Programme (CAADP) na kasa, yayin wani taron masu ruwa da tsaki da aka gudanar a Abuja kan aiwatar da Yarjejeniyar Kampala ta Tarayyar Afirka.

    Yarjejeniyar, wadda shugabannin ƙasashen Afirka suka amince da ita a Janairu 2025, na da nufin canza tsarin noma da abinci a nahiyar cikin shekaru goma masu zuwa (2026–2035).

    Emmanuel ya bayyana cewa kaso 58% na Afirka ke fama da matsananciyar rashin abinci, inda mutane miliyan 924.8 ba su iya samun abinci mai gina jiki. A Najeriya kuma, kusan gida 6 cikin 10 ba sa iya cin abinci mai kyau. Ya kuma nuna cewa sama da mutane 50,000 a Najeriya na kamuwa da cututtuka saboda abinci mara tsabta a duk shekara.

    Duk da cewa ƙasashen Afirka sun kuduri niyyar ware 10% na kasafin kuɗi ga noma, Najeriya na kashe kusan 3% kacal. Sai dai ya yaba da ƙoƙarin ma’aikatar noma wajen kafa kwamiti na musamman domin tsara sabon shirin shekaru goma.

    A nasa jawabin, Azubike Nwokoye na ActionAid ya jaddada muhimmancin tabbatar da gaskiya da bin doka wajen aiwatar da yarjejeniyar Kampala. Ya bukaci a samar da bashi ga manoma, kayan zamani, a inganta ajiya da sarrafa amfanin gona, tare da shigar da mata da matasa sosai cikin harkokin noma.

    Grace Oyediji, shugabar ƙungiyar ƙananan manoman mata, ta bukaci gwamnati ta ƙara saka hannun jari a fannin noma da sauƙaƙa samun bashi. Ta ce, “Manoma ba sa son yin yajin aiki, domin idan muka tsaya, babu wanda zai ci abinci.”

    Rahotanni sun nuna cewa Najeriya na cikin mummunan halin talauci, inda mutane miliyan 133 ke fama da rashin abinci, ruwa, ilimi, da kula da lafiya — lamarin da ya tsananta bayan cire tallafin mai da daidaita naira a 2024.

    Najeriya
    Share. Facebook Twitter WhatsApp Telegram
    Previous ArticleƳan Bindiga Sun Tilastawa Manoma Biyan Harajin Naira Miliyan 10 a Jihar Neja
    Next Article Na Yi Mamaki Da Buhari Bai Iya Magance Matsalar Boko Haram Ba – Jonathan
    Abbass Abdurrahman
    • Website

    Related Posts

    Featured

    Gwamnatin Kano Ta Shiryawa Ƴan Jaridar Yanar Gizo Horo Na Yini Biyu a Jigawa

    January 15, 2026
    Featured

    Tanka Ta Murƙushe Mutane 5 a Gombe

    January 12, 2026
    Featured

    Babu Siyasa a Binciken Da Ake Yi Wa Malami – EFCC

    January 12, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    SABBIN LABARAI

    Gwamnatin Kano Ta Dakatar da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi

    October 1, 202542 Views

    Kotu Ta Yankewa Tsohon Firayim Ministan Mali Hukuncin Zaman Gidan Yari Sakamakon Rubutu a Shafin Sada Zumunta

    October 27, 202541 Views

    Dantawaye Ya Zama Sabon Kwamishinan Ƴansanda a Abuja

    October 17, 202532 Views

    An Gano Motar Ofishin Mataimakin Gwamna Da Aka Sace

    November 12, 202527 Views

    NAFDAC Ta Yi Gargaɗi Kan Wani Kororon Roba Me Matuƙar Haɗari Ga Lafiya

    December 30, 202525 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    • Telegram
    © 2026 Bechi Hausa News. Developed by: ENGRMKS & CO.
    • Shafin Farko
    • Game da Mu
    • Ƙarin Bayani
    • Manufar Sirri
    • Ka’idoji da Sharudda
    • Tuntuɓe Mu

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.