Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    • Shafin Farko
    • Labarai

      Najeriya Ta Musanta Zargin Goyon Bayan Yunƙurin Juyin Mulki a Nijar

      September 4, 2026

      A shirye nake na mutu domin kare ƙuri’ata – Peter Obi

      September 4, 2026

      Sarkin Gumel Alhaji Ahmed Muhammad Sani Ya Rasu 

      September 3, 2026

      Gwamnatin Kano ta fitar da iyakoki tsakanin Jam’iar Bayero da alummar Rimin Zakara bayan kammala biyan diyya

      September 3, 2026

      Ƙungiyar Miyetti Allah Ta Buƙaci Tinubu Ya Sa a Saki Shugabanta

      September 3, 2026
    • Siyasa

      A shirye nake na mutu domin kare ƙuri’ata – Peter Obi

      September 4, 2026

      Ɗan Takarar Sanatan Kano ta Tsakiya a NDC Na Shirin Komawa APC

      September 2, 2026

      Ƴan Siyasa Ne Matsalar Najeriya – Peter Obi

      August 31, 2026

      Bai kamata Tinubu ya bar Najeriya a dai dai lokacin da matsaloli ke addabar ƙasarsa ba – Atiku

      August 31, 2026

      Atiku Ya Yi Alkawarin Sake Buɗe Iyakokin Najeriya Idan Ya Lashe Zaɓen 2027

      August 28, 2026
    • Addini

      Shugaban Asibitin Kwararru na Best Choice, Na Taya Gwamnan Kano Da Al’umma Bikin Murnar Maulidi Annabi SAW

      September 2, 2026

      Hajj 2027 : Kano ta kammala sayar da kujeru 3,050 da aka ware wa jihar

      August 31, 2026

      Gwamnatin Kano ta bayar da hutu domin bikin Takutaha

      August 26, 2026

      Wasu Malamai Daga Arewacin Najeriya Sun Goyi Bayan Tazarcen Tinubu

      August 23, 2026

      Gwamnatin Tarayya ta ayyana Talata a matsayin ranar hutun Maulidi

      August 21, 2026
    • Nishadi

      Oculus Founder Makes a VR Headset That Can Literally Kill You

      January 13, 2021
      85

      Braun Series 7 Electric Shaver Review: Quality at a Good Price

      January 13, 2021
      85

      Google Pixel 7, iPhone 14 Compared: Check Out 5 Major Differences

      January 13, 2021

      Why Apple Should Skip The MacBook Pro Launch

      January 12, 2021

      Apollo G2J Showcases Electric Sports Car

      January 12, 2021
    • Tsaro

      Ƴanbindiga Sun Sace Shugaban Jam’iyyar ’iyyar APC Na Ƙaramar Hukumar Rogo

      September 1, 2026

      Amurka Za Ta Janye Sojoji Kusan 200 Daga Najeriya

      August 28, 2026

      Sojoji Sun Kama Ƴan Ƙasashen Waje Da Ake Zargin Suna da Hannu a Matsalar Tsaron Najeriya – Bwala

      July 18, 2026

      ‘Yan Sanda Sun Fara Kwato Makaman Da Ke Hannun Jama’a Ba Bisa Ka’ida Ba – IGP Disu 

      July 17, 2026

      Sojoji Sun Gano Ƴan Ƙasashen Waje Uku Cikin Mayaƙan ISWAP a Borno

      July 13, 2026
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    Home » Mutane 2 Cikin 11 Na Fuskantar Yunwa a Najeriya — Binciken Masana
    Featured

    Mutane 2 Cikin 11 Na Fuskantar Yunwa a Najeriya — Binciken Masana

    Abbass AbdurrahmanBy Abbass AbdurrahmanOctober 4, 2025No Comments2 Mins Read

    Masana harkar noma sun bayyana cewa mutane biyu cikin kowace goma sha ɗaya a Najeriya na fama da yunwa a kullum, yayin da ɗaya cikin biyar na nahiyar Afirka ke fama da ƙarancin abinci.

    Wannan bayani ya fito ne daga Onijighogia Emmanuel, wakilin shirin Comprehensive Africa Agriculture Development Programme (CAADP) na kasa, yayin wani taron masu ruwa da tsaki da aka gudanar a Abuja kan aiwatar da Yarjejeniyar Kampala ta Tarayyar Afirka.

    Yarjejeniyar, wadda shugabannin ƙasashen Afirka suka amince da ita a Janairu 2025, na da nufin canza tsarin noma da abinci a nahiyar cikin shekaru goma masu zuwa (2026–2035).

    Emmanuel ya bayyana cewa kaso 58% na Afirka ke fama da matsananciyar rashin abinci, inda mutane miliyan 924.8 ba su iya samun abinci mai gina jiki. A Najeriya kuma, kusan gida 6 cikin 10 ba sa iya cin abinci mai kyau. Ya kuma nuna cewa sama da mutane 50,000 a Najeriya na kamuwa da cututtuka saboda abinci mara tsabta a duk shekara.

    Duk da cewa ƙasashen Afirka sun kuduri niyyar ware 10% na kasafin kuɗi ga noma, Najeriya na kashe kusan 3% kacal. Sai dai ya yaba da ƙoƙarin ma’aikatar noma wajen kafa kwamiti na musamman domin tsara sabon shirin shekaru goma.

    A nasa jawabin, Azubike Nwokoye na ActionAid ya jaddada muhimmancin tabbatar da gaskiya da bin doka wajen aiwatar da yarjejeniyar Kampala. Ya bukaci a samar da bashi ga manoma, kayan zamani, a inganta ajiya da sarrafa amfanin gona, tare da shigar da mata da matasa sosai cikin harkokin noma.

    Grace Oyediji, shugabar ƙungiyar ƙananan manoman mata, ta bukaci gwamnati ta ƙara saka hannun jari a fannin noma da sauƙaƙa samun bashi. Ta ce, “Manoma ba sa son yin yajin aiki, domin idan muka tsaya, babu wanda zai ci abinci.”

    Rahotanni sun nuna cewa Najeriya na cikin mummunan halin talauci, inda mutane miliyan 133 ke fama da rashin abinci, ruwa, ilimi, da kula da lafiya — lamarin da ya tsananta bayan cire tallafin mai da daidaita naira a 2024.

    Najeriya
    Share. Facebook Twitter WhatsApp Telegram
    Previous ArticleƳan Bindiga Sun Tilastawa Manoma Biyan Harajin Naira Miliyan 10 a Jihar Neja
    Next Article Na Yi Mamaki Da Buhari Bai Iya Magance Matsalar Boko Haram Ba – Jonathan
    Abbass Abdurrahman
    • Website

    Related Posts

    Featured

    Najeriya Ta Musanta Zargin Goyon Bayan Yunƙurin Juyin Mulki a Nijar

    September 4, 2026
    Featured

    A shirye nake na mutu domin kare ƙuri’ata – Peter Obi

    September 4, 2026
    Featured

    Sarkin Gumel Alhaji Ahmed Muhammad Sani Ya Rasu 

    September 3, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    SABBIN LABARAI

    Ba Don Gudunmawar Masu Yiwa Ƙasa Hidima Ba Da Jihohi Dayawa Basu Kai Yadda Suke a Yanzu Ba – Minista

    December 8, 2025229 Views

    Sabon Rikici Ya Kunno Kai a NDC : Ƴan Takara Sun Kai Ƙara Kan Zaɓen Fidda-gwani a Kano

    June 30, 202680 Views

    Gwamnatin Kano Ta Dakatar da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi

    October 1, 202551 Views

    Gwamnatin Kano Ta Raba Filaye Ga Masu Taimakawa Gwamna Sama da 2,500

    August 1, 202644 Views

    Kotu Ta Yankewa Tsohon Firayim Ministan Mali Hukuncin Zaman Gidan Yari Sakamakon Rubutu a Shafin Sada Zumunta

    October 27, 202541 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    • Telegram
    © 2026 Bechi Hausa News. Developed by: ENGRMKS & CO.
    • Shafin Farko
    • Game da Mu
    • Ƙarin Bayani
    • Manufar Sirri
    • Ka’idoji da Sharudda
    • Tuntuɓe Mu

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.