Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    • Shafin Farko
    • Labarai

      Najeriya Ta Musanta Zargin Goyon Bayan Yunƙurin Juyin Mulki a Nijar

      September 4, 2026

      A shirye nake na mutu domin kare ƙuri’ata – Peter Obi

      September 4, 2026

      Sarkin Gumel Alhaji Ahmed Muhammad Sani Ya Rasu 

      September 3, 2026

      Gwamnatin Kano ta fitar da iyakoki tsakanin Jam’iar Bayero da alummar Rimin Zakara bayan kammala biyan diyya

      September 3, 2026

      Ƙungiyar Miyetti Allah Ta Buƙaci Tinubu Ya Sa a Saki Shugabanta

      September 3, 2026
    • Siyasa

      A shirye nake na mutu domin kare ƙuri’ata – Peter Obi

      September 4, 2026

      Ɗan Takarar Sanatan Kano ta Tsakiya a NDC Na Shirin Komawa APC

      September 2, 2026

      Ƴan Siyasa Ne Matsalar Najeriya – Peter Obi

      August 31, 2026

      Bai kamata Tinubu ya bar Najeriya a dai dai lokacin da matsaloli ke addabar ƙasarsa ba – Atiku

      August 31, 2026

      Atiku Ya Yi Alkawarin Sake Buɗe Iyakokin Najeriya Idan Ya Lashe Zaɓen 2027

      August 28, 2026
    • Addini

      Shugaban Asibitin Kwararru na Best Choice, Na Taya Gwamnan Kano Da Al’umma Bikin Murnar Maulidi Annabi SAW

      September 2, 2026

      Hajj 2027 : Kano ta kammala sayar da kujeru 3,050 da aka ware wa jihar

      August 31, 2026

      Gwamnatin Kano ta bayar da hutu domin bikin Takutaha

      August 26, 2026

      Wasu Malamai Daga Arewacin Najeriya Sun Goyi Bayan Tazarcen Tinubu

      August 23, 2026

      Gwamnatin Tarayya ta ayyana Talata a matsayin ranar hutun Maulidi

      August 21, 2026
    • Nishadi

      Oculus Founder Makes a VR Headset That Can Literally Kill You

      January 13, 2021
      85

      Braun Series 7 Electric Shaver Review: Quality at a Good Price

      January 13, 2021
      85

      Google Pixel 7, iPhone 14 Compared: Check Out 5 Major Differences

      January 13, 2021

      Why Apple Should Skip The MacBook Pro Launch

      January 12, 2021

      Apollo G2J Showcases Electric Sports Car

      January 12, 2021
    • Tsaro

      Ƴanbindiga Sun Sace Shugaban Jam’iyyar ’iyyar APC Na Ƙaramar Hukumar Rogo

      September 1, 2026

      Amurka Za Ta Janye Sojoji Kusan 200 Daga Najeriya

      August 28, 2026

      Sojoji Sun Kama Ƴan Ƙasashen Waje Da Ake Zargin Suna da Hannu a Matsalar Tsaron Najeriya – Bwala

      July 18, 2026

      ‘Yan Sanda Sun Fara Kwato Makaman Da Ke Hannun Jama’a Ba Bisa Ka’ida Ba – IGP Disu 

      July 17, 2026

      Sojoji Sun Gano Ƴan Ƙasashen Waje Uku Cikin Mayaƙan ISWAP a Borno

      July 13, 2026
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    Home » Sau 22 Ana Yunƙurin Haifar Da Matsala a Matatar Mai Ta Ɗangote – Edwin
    Featured

    Sau 22 Ana Yunƙurin Haifar Da Matsala a Matatar Mai Ta Ɗangote – Edwin

    Abbass AbdurrahmanBy Abbass AbdurrahmanOctober 18, 2025No Comments2 Mins Read

    Mataimakin Shugaban Sashen Mai da Iskar Gas na Kamfanin Dangote, Devakumar Edwin, ya bayyana cewa sau 22 aka yi ƙoƙarin lalata masana’antar man Dangote, wanda hakan ya sa kamfanin ya gudanar da sauye-sauyen cikin gida da suka haifar da sallamar ma’aikata da dama. Ya bayyana haka ne yayin taron manema labarai a Lagos, inda ya ƙaryata rade-radin cewa matakin ya samo asali ne daga matsin lambar ƙungiyar ma’aikata ta PENGASSAN. Edwin ya ce dukkan yunkurin haifqr da tarnaƙi an rubuta su tare da bayanan lokaci da sassan da aka yi ƙoƙarin haddasa gobara, amma tsarin tsaron masana’antar ya hana barnar kai ruwa rana.

    Edwin ya jaddada cewa manufar sauye-sauyen ita ce kare amincin da dorewar masana’antar, ba wai amsa wa matsin lambar ƙungiyoyin kwadago ba. Ya bayyana cewa kasancewar masana’antar ta zamani ce mai tsauraran matakan tsaro, duk wani yunkurin tayar da gobara ana dakatar da shi nan take. Wannan na zuwa ne bayan koke-koken ƙungiyoyin kwadago game da sallamar ma’aikata sama da 800 a kamfanin.

    A nasa bangaren, Sarkin Ibedaowei na Ekpetiama kuma shugaban majalisar sarakunan gargajiya ta jihar Bayelsa, Bubaraye Dakolo, ya bayyana goyon bayansa ga masana’antar Dangote, yana cewa ta kawo sauyi mai muhimmanci ga harkar mai a Najeriya. Ya ce ganin ana tace man Najeriya a cikin ƙasa ya nuna ana gyara kura-kuran shekaru da dama na dogaro da shigo da mai daga waje. Ya bukaci gwamnati da masu ruwa da tsaki su haɗa kai don tabbatar da cikakken ‘yancin Najeriya wajen samar da man fetur.

    Dakolo ya kuma zargi ƙungiyoyin ma’aikata da kasancewa cikin “kabal” da ke hana ci gaba a fannin mai. Ya tunatar da yadda PENGASSAN ta yi yajin aiki a 2007 bayan sayar da kaso 51% na matatun Port Harcourt da Kaduna ga kamfanin Bluestar Oil na Aliko Dangote, wanda hakan ya sa gwamnatin Yar’Adua ta soke yarjejeniyar — lamarin da ya haifar da shekaru 18 na durkushewar matatun Najeriya da asarar biliyoyin daloli. Ya yi kira da kada a sake maimaita irin wannan kuskure, yana mai cewa masana’antar Dangote ba ta da wata takura ga kasuwa, domin gwamnati ta riga ta bayar da lasisin gina matatun mai guda 30, amma wasu masu ruwa da tsaki sun fi son riba ta gaggawa daga shigo da mai fiye da saka hannun jari na dogon lokaci.

    Matatar Mai Ta Ɗangote
    Share. Facebook Twitter WhatsApp Telegram
    Previous ArticleWike Ya Musanta Batun Tsayawa Takara a Zaben 2027
    Next Article Kotu Ta Bayar Da Damar Gudanar Da Zanga-zangar Sako Nnamdi Kanu
    Abbass Abdurrahman
    • Website

    Related Posts

    Featured

    Najeriya Ta Musanta Zargin Goyon Bayan Yunƙurin Juyin Mulki a Nijar

    September 4, 2026
    Featured

    A shirye nake na mutu domin kare ƙuri’ata – Peter Obi

    September 4, 2026
    Featured

    Sarkin Gumel Alhaji Ahmed Muhammad Sani Ya Rasu 

    September 3, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    SABBIN LABARAI

    Ba Don Gudunmawar Masu Yiwa Ƙasa Hidima Ba Da Jihohi Dayawa Basu Kai Yadda Suke a Yanzu Ba – Minista

    December 8, 2025229 Views

    Sabon Rikici Ya Kunno Kai a NDC : Ƴan Takara Sun Kai Ƙara Kan Zaɓen Fidda-gwani a Kano

    June 30, 202680 Views

    Gwamnatin Kano Ta Dakatar da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi

    October 1, 202551 Views

    Gwamnatin Kano Ta Raba Filaye Ga Masu Taimakawa Gwamna Sama da 2,500

    August 1, 202644 Views

    Kotu Ta Yankewa Tsohon Firayim Ministan Mali Hukuncin Zaman Gidan Yari Sakamakon Rubutu a Shafin Sada Zumunta

    October 27, 202541 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    • Telegram
    © 2026 Bechi Hausa News. Developed by: ENGRMKS & CO.
    • Shafin Farko
    • Game da Mu
    • Ƙarin Bayani
    • Manufar Sirri
    • Ka’idoji da Sharudda
    • Tuntuɓe Mu

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.