Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    • Shafin Farko
    • Labarai

      Ba Kama Gbajabiamila Muka Yi Ba Gayyatarsa Muka Yi – ICPC

      July 21, 2026

      Tinubu Ya Naɗa Sabbin Shugabanni Da Mambobi 26 a Hukumomi Da Kwamitocin Gwamnatin Tarayya

      July 21, 2026

      An Zargi Likitan El-Rufai Da Bayar da Rahoton Jinya Na Bogi

      July 21, 2026

      Guguwa Da Ruwan Sama Mai Ƙarfi Sun Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutane Huɗu a Sakkwato

      July 21, 2026

      Mamakon Ruwan Sama Ya Lalata Gidaje Da Gonaki a Filato

      July 20, 2026
    • Siyasa

      Kotu Ta Yi Watsi da Ƙarar da Tsagin Tanimu Turaki Suka Shigar Kan Rikicin Shugabancin PDP

      July 18, 2026

      Ya Kamata Majalisa Ta Yi Bincike Kan Ingancin Lafiyar Tinubu – ADC

      July 17, 2026

      Gwamna Yusuf Ya Zaɓi Garo a Matsayin Mataimakinsa a Zaɓen 2027

      July 13, 2026

      INEC Ta Ƙara Wa’adin Miƙa Sunayen ‘Yan Takarar Zaɓen 2027

      July 12, 2026

      Sauye-sauyen Gwamnatina Sun Inganta Ayyuka Da Tattalin Arziki a Kaduna – Gwamna Uba Sani 

      July 10, 2026
    • Addini

      An Rufe Birnin Tehran Domin Jana’izar Ayatollah Ali Khamenei

      July 1, 2026

      Kotu Ta Buƙaci a Gabatar Da Litattafan Da Sheikh Abduljabbar Ya Yi Amfani Da Su

      June 29, 2026

      NAHCON Ta Kammala Dawo Da Alhazan Najeriya Daga Saudiyya

      June 23, 2026

      Sarkin Musulmi Ya Buƙaci Hukumomi Su Gaggauta Ɗaukar Matakai Domin Magance Matsalar Tsaro

      June 17, 2026

      Gwamnatin Kano Za Ta Kashe Naira Biliyan 1.5 Domin Shirin ‘Auren Gata’

      June 15, 2026
    • Nishadi

      Oculus Founder Makes a VR Headset That Can Literally Kill You

      January 13, 2021
      85

      Braun Series 7 Electric Shaver Review: Quality at a Good Price

      January 13, 2021
      85

      Google Pixel 7, iPhone 14 Compared: Check Out 5 Major Differences

      January 13, 2021

      Why Apple Should Skip The MacBook Pro Launch

      January 12, 2021

      Apollo G2J Showcases Electric Sports Car

      January 12, 2021
    • Tsaro

      Sojoji Sun Kama Ƴan Ƙasashen Waje Da Ake Zargin Suna da Hannu a Matsalar Tsaron Najeriya – Bwala

      July 18, 2026

      ‘Yan Sanda Sun Fara Kwato Makaman Da Ke Hannun Jama’a Ba Bisa Ka’ida Ba – IGP Disu 

      July 17, 2026

      Sojoji Sun Gano Ƴan Ƙasashen Waje Uku Cikin Mayaƙan ISWAP a Borno

      July 13, 2026

      An Kashe Fitaccen Jagoran ‘Yan Bindiga Sani Yellow a Zamfara

      July 12, 2026

      Matasa a Borno Sun Gudanar Da Zanga-Zanga Kan Rashin Tsaro

      July 12, 2026
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    Home » Sau 22 Ana Yunƙurin Haifar Da Matsala a Matatar Mai Ta Ɗangote – Edwin
    Featured

    Sau 22 Ana Yunƙurin Haifar Da Matsala a Matatar Mai Ta Ɗangote – Edwin

    Abbass AbdurrahmanBy Abbass AbdurrahmanOctober 18, 2025No Comments2 Mins Read

    Mataimakin Shugaban Sashen Mai da Iskar Gas na Kamfanin Dangote, Devakumar Edwin, ya bayyana cewa sau 22 aka yi ƙoƙarin lalata masana’antar man Dangote, wanda hakan ya sa kamfanin ya gudanar da sauye-sauyen cikin gida da suka haifar da sallamar ma’aikata da dama. Ya bayyana haka ne yayin taron manema labarai a Lagos, inda ya ƙaryata rade-radin cewa matakin ya samo asali ne daga matsin lambar ƙungiyar ma’aikata ta PENGASSAN. Edwin ya ce dukkan yunkurin haifqr da tarnaƙi an rubuta su tare da bayanan lokaci da sassan da aka yi ƙoƙarin haddasa gobara, amma tsarin tsaron masana’antar ya hana barnar kai ruwa rana.

    Edwin ya jaddada cewa manufar sauye-sauyen ita ce kare amincin da dorewar masana’antar, ba wai amsa wa matsin lambar ƙungiyoyin kwadago ba. Ya bayyana cewa kasancewar masana’antar ta zamani ce mai tsauraran matakan tsaro, duk wani yunkurin tayar da gobara ana dakatar da shi nan take. Wannan na zuwa ne bayan koke-koken ƙungiyoyin kwadago game da sallamar ma’aikata sama da 800 a kamfanin.

    A nasa bangaren, Sarkin Ibedaowei na Ekpetiama kuma shugaban majalisar sarakunan gargajiya ta jihar Bayelsa, Bubaraye Dakolo, ya bayyana goyon bayansa ga masana’antar Dangote, yana cewa ta kawo sauyi mai muhimmanci ga harkar mai a Najeriya. Ya ce ganin ana tace man Najeriya a cikin ƙasa ya nuna ana gyara kura-kuran shekaru da dama na dogaro da shigo da mai daga waje. Ya bukaci gwamnati da masu ruwa da tsaki su haɗa kai don tabbatar da cikakken ‘yancin Najeriya wajen samar da man fetur.

    Dakolo ya kuma zargi ƙungiyoyin ma’aikata da kasancewa cikin “kabal” da ke hana ci gaba a fannin mai. Ya tunatar da yadda PENGASSAN ta yi yajin aiki a 2007 bayan sayar da kaso 51% na matatun Port Harcourt da Kaduna ga kamfanin Bluestar Oil na Aliko Dangote, wanda hakan ya sa gwamnatin Yar’Adua ta soke yarjejeniyar — lamarin da ya haifar da shekaru 18 na durkushewar matatun Najeriya da asarar biliyoyin daloli. Ya yi kira da kada a sake maimaita irin wannan kuskure, yana mai cewa masana’antar Dangote ba ta da wata takura ga kasuwa, domin gwamnati ta riga ta bayar da lasisin gina matatun mai guda 30, amma wasu masu ruwa da tsaki sun fi son riba ta gaggawa daga shigo da mai fiye da saka hannun jari na dogon lokaci.

    Matatar Mai Ta Ɗangote
    Share. Facebook Twitter WhatsApp Telegram
    Previous ArticleWike Ya Musanta Batun Tsayawa Takara a Zaben 2027
    Next Article Kotu Ta Bayar Da Damar Gudanar Da Zanga-zangar Sako Nnamdi Kanu
    Abbass Abdurrahman
    • Website

    Related Posts

    Featured

    Ba Kama Gbajabiamila Muka Yi Ba Gayyatarsa Muka Yi – ICPC

    July 21, 2026
    Featured

    Tinubu Ya Naɗa Sabbin Shugabanni Da Mambobi 26 a Hukumomi Da Kwamitocin Gwamnatin Tarayya

    July 21, 2026
    Featured

    An Zargi Likitan El-Rufai Da Bayar da Rahoton Jinya Na Bogi

    July 21, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    SABBIN LABARAI

    Ba Don Gudunmawar Masu Yiwa Ƙasa Hidima Ba Da Jihohi Dayawa Basu Kai Yadda Suke a Yanzu Ba – Minista

    December 8, 2025150 Views

    Sabon Rikici Ya Kunno Kai a NDC : Ƴan Takara Sun Kai Ƙara Kan Zaɓen Fidda-gwani a Kano

    June 30, 202679 Views

    Gwamnatin Kano Ta Dakatar da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi

    October 1, 202546 Views

    Kotu Ta Yankewa Tsohon Firayim Ministan Mali Hukuncin Zaman Gidan Yari Sakamakon Rubutu a Shafin Sada Zumunta

    October 27, 202541 Views

    Dantawaye Ya Zama Sabon Kwamishinan Ƴansanda a Abuja

    October 17, 202533 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    • Telegram
    © 2026 Bechi Hausa News. Developed by: ENGRMKS & CO.
    • Shafin Farko
    • Game da Mu
    • Ƙarin Bayani
    • Manufar Sirri
    • Ka’idoji da Sharudda
    • Tuntuɓe Mu

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.