Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    • Shafin Farko
    • Labarai

      Mutane 4 Sun Mutu a Turmutsutsun Karɓar Sadaka a Katsina

      March 2, 2026

      Ba Za Mu Bayar da Tabbacin Sahihin Zaɓe a 2027 Ba – Amupitan

      March 2, 2026

      Jirage Marasa Matuƙa Sun Kai Hari Matatar Man Saudiyya

      March 2, 2026

      Najeriya Ta Buƙaci a Kawo Karshen Rikicin Gabas ta Tsakiya

      March 2, 2026

      Iran Ta Naɗa Ayatollah Arafi A Matsayin Jagoran Addini Na Riƙo

      March 1, 2026
    • Siyasa

      Gwamnan Adamawa Ya Sauya Sheƙa Zuwa APC

      February 27, 2026

      NDLEA Ta Kama Wata Mata Mai Cikin Bogi Ɗauke da Hodar Iblis a Iyakar Seme

      February 22, 2026

      Jam’iyyun Adawa Sun Kaurace wa Zaɓen Kano, APC Ta Lashe Kujerun Majalisa a Rivers

      February 22, 2026

      Kotu Ta Umarci INEC Ta Yi Wa Jam’iyyar NDP Rajista

      February 19, 2026

      Gwamnan Zamfara Ya Zargi Gwamnatin Tarayya da Nuna Masa Wariya Saboda Bambancin Jam’iyya

      February 18, 2026
    • Addini

      Bauchi Ta neman ƙarin Kujerun Hajji Daga Saudiyya

      February 16, 2026

      Sarkin Musulmi Ya Umarci Ƴan Najeriya Su Fara Duban Jinjirin Watan Ramadan Ranar Talata

      February 16, 2026

      Tinubu Ya Naɗa Ambasada Ismail Abba Yusuf a Matsayin Sabon Shugaban NAHCON

      February 11, 2026

      Sheikh Usman Kusfa Zaria (Rigi-rigi) Ya Rasu

      February 2, 2026

      Jigawa Ta Fara Gwajin Lafiya ga Maniyyatan Hajjin 2026

      January 28, 2026
    • Nishadi

      Oculus Founder Makes a VR Headset That Can Literally Kill You

      January 13, 2021
      85

      Braun Series 7 Electric Shaver Review: Quality at a Good Price

      January 13, 2021
      85

      Google Pixel 7, iPhone 14 Compared: Check Out 5 Major Differences

      January 13, 2021

      Why Apple Should Skip The MacBook Pro Launch

      January 12, 2021

      Apollo G2J Showcases Electric Sports Car

      January 12, 2021
    • Tsaro

      Ba a Fasa Bututun Mai Ko Ɗaya a Niger Delta a 2025 Ba – Sojoj

      January 20, 2026

      Sojojin Najeriya Sun Ƙwato lita 290,000 Na Man Fetur a Yankin Neja Delta

      October 21, 2025

      Ƴan Bindiga Sun Ƙwace Wayoyin Ƴan Sanda a Zamfara

      October 2, 2025

      Gwamnan Kano Ya Buƙaci Tinubu Ya Tsige Kwamishinan Ƴan Sandan Jihar

      October 1, 2025

      Will Using a VPN on Phone Helps Protect You from Ransomware?

      January 14, 2021
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    Home » TInubu Ya Buƙaci Majalisar Dattawa Ta Amince Da Naɗin Sabbin Hafsoshin Tsaro
    Featured

    TInubu Ya Buƙaci Majalisar Dattawa Ta Amince Da Naɗin Sabbin Hafsoshin Tsaro

    Abbass AbdurrahmanBy Abbass AbdurrahmanOctober 28, 2025No Comments1 Min Read

    Shugaban ƙasa Bola Ahmad Tinubu ya aika wa Majalisar Dattijai da wasiƙa yana neman amincewar ta domin tantancewa da tabbatar da sabbin shugabannin hafsoshin tsaro da ya nada a baya-bayan nan. An karanta wasiƙar ne a zaman majalisar da aka gudanar ranar Talata 28 ga Oktoba ta bakin shugaban majalisar, Godswill Akpabio.

    A cikin wasiƙar, Tinubu ya bayyana sunayen waɗanda ake son a tabbatar, ciki har da Babban Hafsan Tsaro, Janar Olufemi Oluyede; Babban Hafsan Sojin Ƙasa, Manjo Janar Waheedi Shaibu; Babban Hafsan Rundunar Ruwa, Rear Admiral Idi Abbas; Babban Hafsan Rundunar Sama, Air Vice Marshal Kennedy Aneke; da kuma Daraktan Leken Asiri na Tsaro, Manjo Janar Emmanuel Undiendeye.

    Bayan karanta wasiƙar, Akpabio ya umurci a mika sunayen waɗanda ake son a tabbatar ga Kwamitin Majalisar Dattijai domin gudanar da bincike da tabbatarwa a mako mai zuwa. Wannan na zuwa ne bayan ganawar sirri da Tinubu ya yi da sabbin hafsoshin tsaro a fadar shugaban ƙasa ranar Litinin.

    Ana ganin wannan sabon mataki na shugaban ƙasa a matsayin ɓangare na ƙoƙarin sabunta tsarin tsaro da inganta haɗin kai tsakanin rundunonin sojoji domin tunkarar ƙalubalen tsaro da ƙasar ke fuskanta.

    Majalisar Dattawa
    Share. Facebook Twitter WhatsApp Telegram
    Previous ArticleƳansanda Sun Gano Wasu Motocin Sata a Gombe
    Next Article NEMA Ta Karɓi Ƴan Najeriya 153 Da Suka Makale a Chadi
    Abbass Abdurrahman
    • Website

    Related Posts

    Featured

    Mutane 4 Sun Mutu a Turmutsutsun Karɓar Sadaka a Katsina

    March 2, 2026
    Featured

    Ba Za Mu Bayar da Tabbacin Sahihin Zaɓe a 2027 Ba – Amupitan

    March 2, 2026
    Featured

    Jirage Marasa Matuƙa Sun Kai Hari Matatar Man Saudiyya

    March 2, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    SABBIN LABARAI

    Gwamnatin Kano Ta Dakatar da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi

    October 1, 202543 Views

    Kotu Ta Yankewa Tsohon Firayim Ministan Mali Hukuncin Zaman Gidan Yari Sakamakon Rubutu a Shafin Sada Zumunta

    October 27, 202541 Views

    Dantawaye Ya Zama Sabon Kwamishinan Ƴansanda a Abuja

    October 17, 202532 Views

    NAFDAC Ta Yi Gargaɗi Kan Wani Kororon Roba Me Matuƙar Haɗari Ga Lafiya

    December 30, 202527 Views

    An Gano Motar Ofishin Mataimakin Gwamna Da Aka Sace

    November 12, 202527 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    • Telegram
    © 2026 Bechi Hausa News. Developed by: ENGRMKS & CO.
    • Shafin Farko
    • Game da Mu
    • Ƙarin Bayani
    • Manufar Sirri
    • Ka’idoji da Sharudda
    • Tuntuɓe Mu

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.