Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    • Shafin Farko
    • Labarai

      Matatar Dangote Ta Ƙara Farashin Man Fetur

      March 3, 2026

      Doguwa Ya Yi Murabus Daga Muƙamin Kwamishinan Ruwa Na Kano

      March 3, 2026

      Amurka Na Da Isassun Makaman Yaƙi Da Za a Iya Amfani Da Su “Har Abada” – Trump 

      March 3, 2026

      ICPC Ta Bayyana Abubuwan Da Ta Samo Daga Gidan El-Rufai a Abuja

      March 3, 2026

      Ɗan Atiku Ya Ajiye Muƙamin Kwamishina a Gwamnatin Adamawa

      March 3, 2026
    • Siyasa

      Doguwa Ya Yi Murabus Daga Muƙamin Kwamishinan Ruwa Na Kano

      March 3, 2026

      Gwamnan Adamawa Ya Sauya Sheƙa Zuwa APC

      February 27, 2026

      NDLEA Ta Kama Wata Mata Mai Cikin Bogi Ɗauke da Hodar Iblis a Iyakar Seme

      February 22, 2026

      Jam’iyyun Adawa Sun Kaurace wa Zaɓen Kano, APC Ta Lashe Kujerun Majalisa a Rivers

      February 22, 2026

      Kotu Ta Umarci INEC Ta Yi Wa Jam’iyyar NDP Rajista

      February 19, 2026
    • Addini

      Bauchi Ta neman ƙarin Kujerun Hajji Daga Saudiyya

      February 16, 2026

      Sarkin Musulmi Ya Umarci Ƴan Najeriya Su Fara Duban Jinjirin Watan Ramadan Ranar Talata

      February 16, 2026

      Tinubu Ya Naɗa Ambasada Ismail Abba Yusuf a Matsayin Sabon Shugaban NAHCON

      February 11, 2026

      Sheikh Usman Kusfa Zaria (Rigi-rigi) Ya Rasu

      February 2, 2026

      Jigawa Ta Fara Gwajin Lafiya ga Maniyyatan Hajjin 2026

      January 28, 2026
    • Nishadi

      Oculus Founder Makes a VR Headset That Can Literally Kill You

      January 13, 2021
      85

      Braun Series 7 Electric Shaver Review: Quality at a Good Price

      January 13, 2021
      85

      Google Pixel 7, iPhone 14 Compared: Check Out 5 Major Differences

      January 13, 2021

      Why Apple Should Skip The MacBook Pro Launch

      January 12, 2021

      Apollo G2J Showcases Electric Sports Car

      January 12, 2021
    • Tsaro

      Ba a Fasa Bututun Mai Ko Ɗaya a Niger Delta a 2025 Ba – Sojoj

      January 20, 2026

      Sojojin Najeriya Sun Ƙwato lita 290,000 Na Man Fetur a Yankin Neja Delta

      October 21, 2025

      Ƴan Bindiga Sun Ƙwace Wayoyin Ƴan Sanda a Zamfara

      October 2, 2025

      Gwamnan Kano Ya Buƙaci Tinubu Ya Tsige Kwamishinan Ƴan Sandan Jihar

      October 1, 2025

      Will Using a VPN on Phone Helps Protect You from Ransomware?

      January 14, 2021
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    Home » Tinubu Ya Bada Umarnin Janye Ƴansanda Daga Gadin Manyan Mutane a Najeriya
    Featured

    Tinubu Ya Bada Umarnin Janye Ƴansanda Daga Gadin Manyan Mutane a Najeriya

    Abbass AbdurrahmanBy Abbass AbdurrahmanNovember 24, 2025No Comments3 Mins Read

     A wani mataki na gaggawa domin shawo kan matsalar garkuwa da mutane da ke ƙara kamari, Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya umarci a janye kusan ’yan sanda 100,000 daga jikin manyan mutane (VIPs) domin maida su aikin tsaro na jama’a da ya haɗa da yaƙi da ’yan ta’adda.

    A ganawar tsaro da aka gudanar a Abuja ranar Lahadi tare da Shugabannin Rundunonin Tsaro da Daraktan DSS, Tinubu ya bayar da umarnin cewa daga yanzu NSCDC za ta riƙe tsaron VIPs, yayin da ’yan sanda za su koma filin aiki kai tsaye don ƙara cike gibi a yankuna da dama da ke fama da ƙarancin jami’an tsaro. Rahotanni sun nuna cewa Najeriya na da ’yan sanda 371,800 kacal, kuma rabinsu suna bauta wa VIPs maimakon al’umma.

    A cewar mai ba Shugaban Kasa shawara kan labarai, Bayo Onanuga, gwamnati ta kuma amince da daukar sabbin ’yan sanda 30,000 tare da hadin gwiwar jihohi domin inganta cibiyoyin horaswa. Wannan na zuwa ne bayan fargabar da ta taso kan yadda sojoji suka janye daga makarantar St. Mary a Papiri kafin a yi garkuwa da ɗalibai fiye da 300. Rundunar Soji ta ce tana bincike kan dalilin janyewar.

    A halin da ake ciki, rundunar Operation Fansan Yamma ta umurci sojoji da su matsa lamba domin ceto ɗalibai, inda kwamandojin rundunar suka kai ziyara Papiri tare da tabbatar wa al’umma cewa “’yan bindiga ba za su samu mafaka ba.” Al’ummar yankin sun ce zuwan manyan hafsoshin ya saka musu kwarin gwiwa.

    A bangaren siyasa, jam’iyyar APC ta yi zargin cewa tashin hankulan Arewa “na da kamannin shiri na wasu ɓarayi” domin tada hankalin kasa kafin 2027. Wasu jiga-jigan jam’iyyar sun bukaci gwamnati ta bankado masu kutse a cikin tsarin tsaro. A gefe guda kuma, Vatican ta yi kira ga sakin daliban da aka sace, yayin da gwamnoni da dama suka rufe makarantu domin takaita barna — lamarin da masana tsaro suka ce na iya ƙara karfafa masu laifi.

    A ranar Lahadi, kusan dalibai 50 daga cikin wadanda aka sace a Papiri sun tsere sun koma gidajensu, amma har yanzu 253 suna hannun ’yan ta’adda tare da ma’aikata 12. Haka kuma, a Kwara, dukkan worshippers 38 da aka sace daga cocin CAC Eruku sun samu ‘yanci bayan wani gagarumin aikin hadin gwiwa da ya samu kulawar Tinubu kai tsaye. gwamnoni da hukumomin tsaro na ƙara haɗa kai domin kare makarantu da al’ummomi yayin da hare-haren ’yan bindiga ke ƙaruwa.

    Ƴansanda
    Share. Facebook Twitter WhatsApp Telegram
    Previous ArticleZargin Biyan kudin Fansa : Gwamnatin Kaduna Ta Buƙaci El-Rufai Ya Janye Kalamansa Ko Ta Makashi a Gaban Kotu
    Next Article Jam’iyyar PDP Ta Buƙaci Tinubu Ya Sauka Daga Mulki Matuƙar Bazai Iya Kare Rayukan Ƴan Najeriya Ba
    Abbass Abdurrahman
    • Website

    Related Posts

    Featured

    Matatar Dangote Ta Ƙara Farashin Man Fetur

    March 3, 2026
    Featured

    Doguwa Ya Yi Murabus Daga Muƙamin Kwamishinan Ruwa Na Kano

    March 3, 2026
    Featured

    Amurka Na Da Isassun Makaman Yaƙi Da Za a Iya Amfani Da Su “Har Abada” – Trump 

    March 3, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    SABBIN LABARAI

    Gwamnatin Kano Ta Dakatar da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi

    October 1, 202544 Views

    Kotu Ta Yankewa Tsohon Firayim Ministan Mali Hukuncin Zaman Gidan Yari Sakamakon Rubutu a Shafin Sada Zumunta

    October 27, 202541 Views

    Dantawaye Ya Zama Sabon Kwamishinan Ƴansanda a Abuja

    October 17, 202532 Views

    NAFDAC Ta Yi Gargaɗi Kan Wani Kororon Roba Me Matuƙar Haɗari Ga Lafiya

    December 30, 202527 Views

    An Gano Motar Ofishin Mataimakin Gwamna Da Aka Sace

    November 12, 202527 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    • Telegram
    © 2026 Bechi Hausa News. Developed by: ENGRMKS & CO.
    • Shafin Farko
    • Game da Mu
    • Ƙarin Bayani
    • Manufar Sirri
    • Ka’idoji da Sharudda
    • Tuntuɓe Mu

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.