Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    • Shafin Farko
    • Labarai

      Tinubu Ya Sha Alwashin Murƙushe Ta’addanci a Najeriya

      November 6, 2025

      Hukumar Kiyaye Afkuwar Haɗura Ta Ƙasa Ta Kama Direbobi 27,000 a Abuja

      November 6, 2025

      Gidaje 20 Da Ake Zargina a Kansu Ba Nawa Bane Ne Waɗanda Mahaifinmu Ya Bar Mana Gado Ne – Abba Kyari

      November 6, 2025

      Matuƙar Ba’a Yi Yadda Aka Yi a Afghanistan Ba Baza’a Kawo Ƙarshen Ta’addanci a Najeriya Ba – Amurka

      November 6, 2025

      Shekarau @ 70: Damuwa Bata Taɓa Hanani Bacci Ba – Shekarau

      November 6, 2025
    • Siyasa

      Gombe Na Amfana Da Cire Tallafin Man Fetur – Inuwa Yahya

      November 4, 2025

      Sabon Rikici Na Shirin Kunno Kai Tsakanin Sanata Natasha Da Akpabio

      November 4, 2025

      Har Yanzu Bamu Janye Dakatarwar Shekaru 30 Da Mu Ka Yi Wa El-Rufai Ba – SDP

      November 2, 2025

      Gwamnan Taraba Zai Koma Jam’iyyar APC

      October 29, 2025

      Gwamnonin PDP Sun Zaɓi Tanimu Turaki a Matsayin Ɗan Takararsu a Zaɓen Shugabancin Jam’iyya

      October 25, 2025
    • Addini

      Ƙungiyoyin Fityanul Islam Da Samarin Tijjaniyya Sun Yi Ƙarar Gwamnatin Kano a Kotu

      November 5, 2025

      Saudiyya Ta Ragewa Najeriya Kujerun Hajjin 2026

      October 17, 2025

      Sarkin Musulmi Ya Buƙaci a Samar Da Dokokin Amfani Da Kafafen Sada Zumunta a Najeriya

      October 16, 2025

      Hisbah Ta Kama Wasu Matasa Da Laifin Yin Aure Ba Tare Da Amincewar Iyayensu Ba

      October 13, 2025

      Tinubu Ya Bawa NAHCON Umarnin Rage Kuɗin Hajjin 2026 Cikin Gaggawa

      October 7, 2025
    • Nishadi

      Oculus Founder Makes a VR Headset That Can Literally Kill You

      January 13, 2021
      85

      Braun Series 7 Electric Shaver Review: Quality at a Good Price

      January 13, 2021
      85

      Google Pixel 7, iPhone 14 Compared: Check Out 5 Major Differences

      January 13, 2021

      Why Apple Should Skip The MacBook Pro Launch

      January 12, 2021

      Apollo G2J Showcases Electric Sports Car

      January 12, 2021
    • Tsaro

      Sojojin Najeriya Sun Ƙwato lita 290,000 Na Man Fetur a Yankin Neja Delta

      October 21, 2025

      Ƴan Bindiga Sun Ƙwace Wayoyin Ƴan Sanda a Zamfara

      October 2, 2025

      Gwamnan Kano Ya Buƙaci Tinubu Ya Tsige Kwamishinan Ƴan Sandan Jihar

      October 1, 2025

      Will Using a VPN on Phone Helps Protect You from Ransomware?

      January 14, 2021

      Popular New Xbox Game Pass Game Being Review Bombed With “0s”

      January 14, 2021
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    Home » Ana Fargabar Rashin Abinci Mai Gina Jiki Zai Yi Sanadiyyar Mutuwar Yara 96,000 a Najeriya
    Featured

    Ana Fargabar Rashin Abinci Mai Gina Jiki Zai Yi Sanadiyyar Mutuwar Yara 96,000 a Najeriya

    Abbass AbdurrahmanBy Abbass AbdurrahmanOctober 30, 2025No Comments2 Mins Read

    Kungiyar hadin gwiwar kungiyoyin agaji na ƙasa da ƙasa (INGO Forum) ta yi gargaɗi cewa sama da yara 96,000 a jihohi shida na arewacin Najeriya — Adamawa, Borno, Katsina, Sokoto, Yobe da Zamfara — na cikin haɗarin mutuwa sakamakon matsanancin rashin abinci ami gina jiki. Shugaban Action Against Hunger, Thierno Diallo, ya bayyana cewa lamarin akwai tayar da hankali, inda ya ce kimanin mutane miliyan 31 ke fuskantar ƙarancin abinci a 2025, wanda hakan zai sa Najeriya ta zama ƙasar da ke da mafi girman matsalar abinci a duniya.

    A cewar rahoton, hukumar UNICEF ta ruwaito cewa yara miliyan 11 ‘yan ƙasa da shekara biyar na fama da “ƙarancin abinci” inda suke cin abinci daga ƙananan rukunai, abin da ke ƙara musu yiwuwar fama da lalurar “wasting”. Haka kuma, Hukumar Abincin Duniya (WFP) ta yi hasashen cewa mutane miliyan 33 na iya fuskantar matsanancin yunwa idan ba a ɗauki matakan gaggawa ba, musamman saboda rikice-rikicen tsaro, hauhawar farashi, da sauyin yanayi da ke lalata noma da rayuwa.

    Diallo ya ce cikin watanni uku masu zuwa, yara 600,000 masu ƙasa da shekara biyar za su kasance cikin haɗarin matsanancin rashin abinci mai gina jiki, inda daga cikinsu yara 96,000 za su iya mutuwa idan ba su samu magani ba. Ya ƙara da cewa mata masu juna biyu da masu shayarwa sama da 800,000 ma suna cikin haɗari, yayin da kashi 32% na yara ƙasa da shekara biyar a Najeriya ke da matsalar “stunting” — rashin girma saboda rashin gina jiki.

    Shugaban Save the Children International (Nigeria), Duncan Harvey, da wakilar Plan International, Helen Idiong, sun bukaci gwamnati da abokan hulɗa su ɗauki matakin gaggawa tare da ƙara saka hannun jari wajen yaki da yunwa. Sun bayyana cewa yunwa da rashin abinci mai gina jiki ba wai matsalar jin kai ba ce kawai, har ma da take hakkin ‘ya’yan Najeriya na rayuwa da ci gaba. Sun kuma bukaci ƙarfafa tallafin abinci, magungunan gina jiki, da tsare-tsaren kare talakawa daga matsalolin tattalin arziki a gaba.

    Najeriya
    Share. Facebook Twitter WhatsApp Telegram
    Previous ArticleMajalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Dr. Bernard Doro a Matsayin Minista
    Next Article APC Ta Samu Rinjayen Kashi Biyu Cikin Uku a Zauren Majalisar Wakilai
    Abbass Abdurrahman
    • Website

    Related Posts

    Featured

    Tinubu Ya Sha Alwashin Murƙushe Ta’addanci a Najeriya

    November 6, 2025
    Featured

    Hukumar Kiyaye Afkuwar Haɗura Ta Ƙasa Ta Kama Direbobi 27,000 a Abuja

    November 6, 2025
    Featured

    Gidaje 20 Da Ake Zargina a Kansu Ba Nawa Bane Ne Waɗanda Mahaifinmu Ya Bar Mana Gado Ne – Abba Kyari

    November 6, 2025
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    SABBIN LABARAI

    Gwamnatin Kano Ta Dakatar da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi

    October 1, 202535 Views

    Kotu Ta Yankewa Tsohon Firayim Ministan Mali Hukuncin Zaman Gidan Yari Sakamakon Rubutu a Shafin Sada Zumunta

    October 27, 202533 Views

    Dantawaye Ya Zama Sabon Kwamishinan Ƴansanda a Abuja

    October 17, 202526 Views

    Zama a Banɗaki Fiye Da Kima Kan Haifar Da Matsala Ga Lafiyar Ɗan Adam – Likita

    October 28, 202520 Views

    Kotu Ta Bayar Da Belin Sowore

    October 24, 202519 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    • Telegram
    © 2025 Bechi Hausa News. Developed by: ENGRMKS & CO.
    • Shafin Farko
    • Game da Mu
    • Ƙarin Bayani
    • Manufar Sirri
    • Ka’idoji da Sharudda
    • Tuntuɓe Mu

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.