Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    • Shafin Farko
    • Labarai

      Ba Kama Gbajabiamila Muka Yi Ba Gayyatarsa Muka Yi – ICPC

      July 21, 2026

      Tinubu Ya Naɗa Sabbin Shugabanni Da Mambobi 26 a Hukumomi Da Kwamitocin Gwamnatin Tarayya

      July 21, 2026

      An Zargi Likitan El-Rufai Da Bayar da Rahoton Jinya Na Bogi

      July 21, 2026

      Guguwa Da Ruwan Sama Mai Ƙarfi Sun Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutane Huɗu a Sakkwato

      July 21, 2026

      Mamakon Ruwan Sama Ya Lalata Gidaje Da Gonaki a Filato

      July 20, 2026
    • Siyasa

      Kotu Ta Yi Watsi da Ƙarar da Tsagin Tanimu Turaki Suka Shigar Kan Rikicin Shugabancin PDP

      July 18, 2026

      Ya Kamata Majalisa Ta Yi Bincike Kan Ingancin Lafiyar Tinubu – ADC

      July 17, 2026

      Gwamna Yusuf Ya Zaɓi Garo a Matsayin Mataimakinsa a Zaɓen 2027

      July 13, 2026

      INEC Ta Ƙara Wa’adin Miƙa Sunayen ‘Yan Takarar Zaɓen 2027

      July 12, 2026

      Sauye-sauyen Gwamnatina Sun Inganta Ayyuka Da Tattalin Arziki a Kaduna – Gwamna Uba Sani 

      July 10, 2026
    • Addini

      An Rufe Birnin Tehran Domin Jana’izar Ayatollah Ali Khamenei

      July 1, 2026

      Kotu Ta Buƙaci a Gabatar Da Litattafan Da Sheikh Abduljabbar Ya Yi Amfani Da Su

      June 29, 2026

      NAHCON Ta Kammala Dawo Da Alhazan Najeriya Daga Saudiyya

      June 23, 2026

      Sarkin Musulmi Ya Buƙaci Hukumomi Su Gaggauta Ɗaukar Matakai Domin Magance Matsalar Tsaro

      June 17, 2026

      Gwamnatin Kano Za Ta Kashe Naira Biliyan 1.5 Domin Shirin ‘Auren Gata’

      June 15, 2026
    • Nishadi

      Oculus Founder Makes a VR Headset That Can Literally Kill You

      January 13, 2021
      85

      Braun Series 7 Electric Shaver Review: Quality at a Good Price

      January 13, 2021
      85

      Google Pixel 7, iPhone 14 Compared: Check Out 5 Major Differences

      January 13, 2021

      Why Apple Should Skip The MacBook Pro Launch

      January 12, 2021

      Apollo G2J Showcases Electric Sports Car

      January 12, 2021
    • Tsaro

      Sojoji Sun Kama Ƴan Ƙasashen Waje Da Ake Zargin Suna da Hannu a Matsalar Tsaron Najeriya – Bwala

      July 18, 2026

      ‘Yan Sanda Sun Fara Kwato Makaman Da Ke Hannun Jama’a Ba Bisa Ka’ida Ba – IGP Disu 

      July 17, 2026

      Sojoji Sun Gano Ƴan Ƙasashen Waje Uku Cikin Mayaƙan ISWAP a Borno

      July 13, 2026

      An Kashe Fitaccen Jagoran ‘Yan Bindiga Sani Yellow a Zamfara

      July 12, 2026

      Matasa a Borno Sun Gudanar Da Zanga-Zanga Kan Rashin Tsaro

      July 12, 2026
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    Home » Ba Za Mu Yafewa Waɗanda Suka Kashe Mutanenmu a Zaria Ba – IMN
    Featured

    Ba Za Mu Yafewa Waɗanda Suka Kashe Mutanenmu a Zaria Ba – IMN

    Abbass AbdurrahmanBy Abbass AbdurrahmanDecember 11, 2025Updated:December 11, 2025No Comments2 Mins Read

    Mabiya mazhabar Shi’a a Najeriya sun sake tunawa da cikar shekaru goma da kisan gillar da aka yi musu a Zaria, yayin da suka ce har yanzu suna cikin raɗaɗin abin da ya faru. A 2015 ne rikici ya barke tsakanin jami’an sojin Najeriya da mabiya Sheikh Ibrahim Zakzaky, lamarin da ya yi sanadin mutuwar daruruwan mutane da kuma jikkata da dama, bayan zargin Rundunar Soji cewa an tare musu hanya.

    Farfesa Abdullahi Danladi, shugaban dandalin tattaunawa na IMN a Najeriya, ya bayyana wa BBC cewa a duk tsawon shekarun nan babu wani ɓangaren gwamnati da ya ɗauki mataki kan wadanda suka aikata kisan. Ya ce babu hukunci, babu kama, babu rahoton kwamitin binciken da aka kafa — abin da ya tabbatar musu cewa an yi ƙoƙarin rufe gaskiya. Ya ce hakan na ƙara tunzura zukatan mabiya Shi’a da kuma tabbatar musu da cewa an tauye musu adalci.

    A cewar Farfesan, al’ummar Shi’a za su ci gaba da neman adalci muddin suna raye, tare da jaddada cewa tarihi ba zai manta da abin da ya faru a Zaria ba. Ya yi nuni da cewa ko da shari’a ta ɗauki lokaci mai tsawo, gaskiya dole ta bayyana wata rana. A cewar sa, wannan rana ta tunawa ta musamman ta sake tayar masu da raɗaɗin abin da ya faru, tare da ƙarfafa matsayarsu na kin yafiya.

    Bechi Hausa ta tattaro cewa IMN na ci gaba da kira ga gwamnati da hukumomin tsaro da su fitar da cikakken rahoto kan lamarin, tare da hukunta wadanda suka aikata kisan. Farfesan Danladi ya ce za su ci gaba da taruwa duk shekara, su fadakar da junansu game da wannan hari, domin tabbatar da cewa ba a manta da waɗanda suka mutu ba kuma an tabbatar da ganin adalci.

    IMN
    Share. Facebook Twitter WhatsApp Telegram
    Previous ArticleEFCC Ta Kama Tsohon Minista Ƙwadago
    Next Article Najeriya Zata Ƙulla Ƙawance Da Saudiyya Kan Sha’anin Tsaro
    Abbass Abdurrahman
    • Website

    Related Posts

    Featured

    Ba Kama Gbajabiamila Muka Yi Ba Gayyatarsa Muka Yi – ICPC

    July 21, 2026
    Featured

    Tinubu Ya Naɗa Sabbin Shugabanni Da Mambobi 26 a Hukumomi Da Kwamitocin Gwamnatin Tarayya

    July 21, 2026
    Featured

    An Zargi Likitan El-Rufai Da Bayar da Rahoton Jinya Na Bogi

    July 21, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    SABBIN LABARAI

    Ba Don Gudunmawar Masu Yiwa Ƙasa Hidima Ba Da Jihohi Dayawa Basu Kai Yadda Suke a Yanzu Ba – Minista

    December 8, 2025150 Views

    Sabon Rikici Ya Kunno Kai a NDC : Ƴan Takara Sun Kai Ƙara Kan Zaɓen Fidda-gwani a Kano

    June 30, 202679 Views

    Gwamnatin Kano Ta Dakatar da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi

    October 1, 202546 Views

    Kotu Ta Yankewa Tsohon Firayim Ministan Mali Hukuncin Zaman Gidan Yari Sakamakon Rubutu a Shafin Sada Zumunta

    October 27, 202541 Views

    Dantawaye Ya Zama Sabon Kwamishinan Ƴansanda a Abuja

    October 17, 202533 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    • Telegram
    © 2026 Bechi Hausa News. Developed by: ENGRMKS & CO.
    • Shafin Farko
    • Game da Mu
    • Ƙarin Bayani
    • Manufar Sirri
    • Ka’idoji da Sharudda
    • Tuntuɓe Mu

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.