Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    • Shafin Farko
    • Labarai

      Gwamnatin Kano Ta Shiryawa Ƴan Jaridar Yanar Gizo Horo Na Yini Biyu a Jigawa

      January 15, 2026

      Tanka Ta Murƙushe Mutane 5 a Gombe

      January 12, 2026

      Babu Siyasa a Binciken Da Ake Yi Wa Malami – EFCC

      January 12, 2026

      Ƴan Bindiga Sun Kashe Soja Da Jam’in NSCDC a Benue

      January 12, 2026

      Manyan Jiga-jigan APC 3 a Kogi Sun Mutu

      January 12, 2026
    • Siyasa

      Manyan Jiga-jigan APC 3 a Kogi Sun Mutu

      January 12, 2026

      Ganduje Zai Gana Da Masu Ruwa-da-tsaki Na APC

      January 11, 2026

      Datti Baba-Ahmed Ya Musanta Batun Tsayawa Takarar Shugaban Ƙasa

      January 9, 2026

      Fubara Barazana Ne Ga Demokaraɗiyya – Kakakin Majalisar Rivers

      January 9, 2026

      Kotu Ta Ƙi Bayar da Belin Kwamishinan Kuɗi Na Bauchi

      January 6, 2026
    • Addini

      Kano: Hisbah Ta Karɓi Ƙorafe-Ƙorafe Sama da 12,000 a 2025

      January 2, 2026

      Da Ɗumi-ɗumi : Sheikh Dahiru Bauchi Ya rasu

      November 27, 2025

      Zakaran Gwajin Dafi : Hajji 2025 Karkashin Farfesa Saleh Pakistan  

      November 24, 2025

      Hajji Da Shugabanci Nagari Ƙarƙashin Jagorancin Farfesa Pakistan

      November 17, 2025

      Hukumar NAHCON Ta Sanar Da Rage Kudin Aikin Hajjin 2026

      November 10, 2025
    • Nishadi

      Oculus Founder Makes a VR Headset That Can Literally Kill You

      January 13, 2021
      85

      Braun Series 7 Electric Shaver Review: Quality at a Good Price

      January 13, 2021
      85

      Google Pixel 7, iPhone 14 Compared: Check Out 5 Major Differences

      January 13, 2021

      Why Apple Should Skip The MacBook Pro Launch

      January 12, 2021

      Apollo G2J Showcases Electric Sports Car

      January 12, 2021
    • Tsaro

      Sojojin Najeriya Sun Ƙwato lita 290,000 Na Man Fetur a Yankin Neja Delta

      October 21, 2025

      Ƴan Bindiga Sun Ƙwace Wayoyin Ƴan Sanda a Zamfara

      October 2, 2025

      Gwamnan Kano Ya Buƙaci Tinubu Ya Tsige Kwamishinan Ƴan Sandan Jihar

      October 1, 2025

      Will Using a VPN on Phone Helps Protect You from Ransomware?

      January 14, 2021

      Popular New Xbox Game Pass Game Being Review Bombed With “0s”

      January 14, 2021
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    Home » Ba Za Mu Yafewa Waɗanda Suka Kashe Mutanenmu a Zaria Ba – IMN
    Featured

    Ba Za Mu Yafewa Waɗanda Suka Kashe Mutanenmu a Zaria Ba – IMN

    Abbass AbdurrahmanBy Abbass AbdurrahmanDecember 11, 2025Updated:December 11, 2025No Comments2 Mins Read

    Mabiya mazhabar Shi’a a Najeriya sun sake tunawa da cikar shekaru goma da kisan gillar da aka yi musu a Zaria, yayin da suka ce har yanzu suna cikin raɗaɗin abin da ya faru. A 2015 ne rikici ya barke tsakanin jami’an sojin Najeriya da mabiya Sheikh Ibrahim Zakzaky, lamarin da ya yi sanadin mutuwar daruruwan mutane da kuma jikkata da dama, bayan zargin Rundunar Soji cewa an tare musu hanya.

    Farfesa Abdullahi Danladi, shugaban dandalin tattaunawa na IMN a Najeriya, ya bayyana wa BBC cewa a duk tsawon shekarun nan babu wani ɓangaren gwamnati da ya ɗauki mataki kan wadanda suka aikata kisan. Ya ce babu hukunci, babu kama, babu rahoton kwamitin binciken da aka kafa — abin da ya tabbatar musu cewa an yi ƙoƙarin rufe gaskiya. Ya ce hakan na ƙara tunzura zukatan mabiya Shi’a da kuma tabbatar musu da cewa an tauye musu adalci.

    A cewar Farfesan, al’ummar Shi’a za su ci gaba da neman adalci muddin suna raye, tare da jaddada cewa tarihi ba zai manta da abin da ya faru a Zaria ba. Ya yi nuni da cewa ko da shari’a ta ɗauki lokaci mai tsawo, gaskiya dole ta bayyana wata rana. A cewar sa, wannan rana ta tunawa ta musamman ta sake tayar masu da raɗaɗin abin da ya faru, tare da ƙarfafa matsayarsu na kin yafiya.

    Bechi Hausa ta tattaro cewa IMN na ci gaba da kira ga gwamnati da hukumomin tsaro da su fitar da cikakken rahoto kan lamarin, tare da hukunta wadanda suka aikata kisan. Farfesan Danladi ya ce za su ci gaba da taruwa duk shekara, su fadakar da junansu game da wannan hari, domin tabbatar da cewa ba a manta da waɗanda suka mutu ba kuma an tabbatar da ganin adalci.

    IMN
    Share. Facebook Twitter WhatsApp Telegram
    Previous ArticleEFCC Ta Kama Tsohon Minista Ƙwadago
    Next Article Najeriya Zata Ƙulla Ƙawance Da Saudiyya Kan Sha’anin Tsaro
    Abbass Abdurrahman
    • Website

    Related Posts

    Featured

    Gwamnatin Kano Ta Shiryawa Ƴan Jaridar Yanar Gizo Horo Na Yini Biyu a Jigawa

    January 15, 2026
    Featured

    Tanka Ta Murƙushe Mutane 5 a Gombe

    January 12, 2026
    Featured

    Babu Siyasa a Binciken Da Ake Yi Wa Malami – EFCC

    January 12, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    SABBIN LABARAI

    Gwamnatin Kano Ta Dakatar da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi

    October 1, 202543 Views

    Kotu Ta Yankewa Tsohon Firayim Ministan Mali Hukuncin Zaman Gidan Yari Sakamakon Rubutu a Shafin Sada Zumunta

    October 27, 202541 Views

    Dantawaye Ya Zama Sabon Kwamishinan Ƴansanda a Abuja

    October 17, 202532 Views

    An Gano Motar Ofishin Mataimakin Gwamna Da Aka Sace

    November 12, 202527 Views

    NAFDAC Ta Yi Gargaɗi Kan Wani Kororon Roba Me Matuƙar Haɗari Ga Lafiya

    December 30, 202525 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    • Telegram
    © 2026 Bechi Hausa News. Developed by: ENGRMKS & CO.
    • Shafin Farko
    • Game da Mu
    • Ƙarin Bayani
    • Manufar Sirri
    • Ka’idoji da Sharudda
    • Tuntuɓe Mu

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.