Tsohon mataimakin gwamnan jihar Kano kuma ɗan takarar gwamna na jam’iyyar APC a zaɓen 2023, Nasiru Yusuf Gawuna, ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar. A cikin wasiƙar murabus mai ɗauke da kwanan wata 29 ga Maris, 2026, ya ce matakin nasa na son rai ne kuma na kansa.

Gawuna ya miƙa wasiƙar ne ga shugaban APC na mazabarsa ta Gawuna a ƙaramar hukumar Nassarawa, inda ya tabbatar da cewa murabus ɗin zai fara aiki nan take. Ya kuma gode wa jam’iyyar bisa damar da ya samu a lokacin da yake cikinta.

Sai dai bai bayyana matakin da zai ɗauka a gaba ba, yayin da ake ci gaba da sauye-sauyen siyasa a Kano. Majiyoyi sun ce ana sa ran zai gana da tsohon gwamnan jihar, Rabiu Musa Kwankwaso, a daren Litinin a gidansa da ke Miller Road.

Share.
Leave A Reply

Exit mobile version